"" /> HADEJIA A YAU!: 02/01/2012 - 03/01/2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, February 29, 2012

Wakar Malam Amadu Dan matawalle Hadejia

1, Harama fasihi ka kara shiri, sarkin samari da 'yan mata.


2, Bismilla nayi nufin waka allah ta-ala kaban hikima, in shirya waka da hausa ta.


3, Nine nasan duk abinda nake nufi a wakar Hadejiawa.


4, sarki yana da mabudinsa nima ina da mabudi Malam idi kaine mabudina.


5, D.O yana da akawunsa nima ina da akawuna Abdu yaro kaine akawu na.


6, Ga mai fasaha kanin sidi, na abdu yaro na maitaushi.


7, Dan maraya na cikin daji, mugun dawa na cikin bene.


8, Su gajango an samu gun Ala, hannun ruwa zaya sha kashi.


9, A gidan biki damisa tilas aka sata sai da ta dau tandu.


10, Giwa tana yin bikin 'yarta, zaki ka bai alwalin ango namun dawa za'a sha hidima.


Sauran baiti goma a baya!

Wednesday, February 22, 2012

TARIHIN SARKIN HADEJIA HARU BUBBA

Sarkin Hadeji Haru bubba shine Mahaifin Sarkin Hadejia Muhammadu mai Shahada, wanda a zamaninsa Turawa sukaci Hadejia da yaki. Sarki Haru bubba Malami ne kuma mutum ne mai son zaman lafiya, kuma shine ya gina Masallacin juma'a Na Hadejia. Kuma a zamaninsa Gumel sukayi yaki da Hadejia, wato lokacin sarkin Gumel Abdu jatau. Sarkin Gumel ya aikowa Sarkin Hadejia zai wuce ta kasarsa wato ta kudu a gayawa Talakawa kada su tsorata bazai taba kowa ba. To amma koda yazo wucewa sai ya saba Alkawari don yana sawa ana debe kayan talakawan ana kaiwa Gumel. Koda Sarkin Hadejia ya samu labari sai yasa akayi sirdi aka fita, a wannan yakin aka kashe sarkin Gumel Abdu jatau. Galadiman Hadejia yakuba shine ya sareshi. Dama sarkin Gumel yayi mafarki bazai koma gida ba. Sai ya fadawa kaninsa Abubakar in ya mutu to a kaishi Gumel ayi masa jana'iza, kuma hakan akayi. Kuma a zamanin Sarkin Hadejia Haru ne Dansa Muhammadu Yayi yaki da Maguzawan Mada Rumfa ta Sokoto, inda sarkin musulmi ya masa sarautar Sarkin yakin Sarkin Musulmi. Kafin ya Zama Sarkin Hadejia. Allah yaji kansu.

WAKOKIN MALAM AMADU DAN MATAWALLE HADEJIA!

AMSHI- Hakane malam Amadi na idi ka sake shiri duniya ta Allah ce malam Amadi.


1, Ku saurara jama'a zana baku labarin wani shi hakimi wanda bazai iya saukarmu ba.


2, Akwai wani dan sarki anyi mar sarauta shi buri ya cika, gaba daya ya baza yaran gidansu bubba da yaro duk sun tafi.


3, Naje kasarsu na samu hakimi wani mai siffar mujiya, da fadawa da mutanen gari suna ja mar Allah ya isa.


4, Jemage ba tsuntsu ba yai kamar tsuntsu sai halin tsiya, ga tsuntsu da hakora kamar mutum ni ban gane kanka ba.


5, Agarnana masu kahonnin karo, mai zafin rayi sai kace na karya in taso haihuwa.


6, Wanda tuwo yafi karfinsa in ya samu tuwo shima sai yaci, wannan in aka tuka ka bashi tare da fadawan zasuci.


7, Yautai dan yawon duniya, shi aka baiwa sarauta ya kama mulki bai san girmansa ba.


8, Ungulu komai namanki ne, ya hana 'yan mata dan irin wasan nan da ake dandali.


9, Bera mai ta'adin gayya shi haram da halak ma bai sansu ba.


10, Yautai dan yawon duniya, ya shiga tsuntsaye 'yan uwansa an rasa mai ganewa dashi.


11, Kyawun dan sarki ai a sanshi mai kyauta ga mutanen gari.


12, Shi gogana ai nasuma yake karba yayi chacha dashi.


13, Ai ni in baka ban naka ba, nawa fa shima ba naka ba.


14, Dumau nake ba fashi ko cikin sa'a daya bani da dadin gamo.


15, Bangon dutse in kaki masu sarawa da diga sa gaji.


16, Shaho birkita kaji na sidi malam baka da dadin gamo, bauna wanda ya dosheta babu maduhu sai wani ba tasa ba.


18, Tamat wa bi hamdu ilallahi zan yi ban kwana waka ta cika.



DAGA ISMA'ILA A. SABO HADEJIA.

Monday, February 20, 2012

WAKAR SAUDATU ADO BAYERO!

1, Daren jiya ba na yau bane gun kwanan yaro daban da bubba.

2, Bismillah zana shirya waka sarki Allah kaban basira inyi wakar saude 'yar nikatau.

3, Ina dada godiya ga rabbi Allah da yasa na sanki saude.

4, Ga saude sarauniyar kano mai saukin kayi da son mutane.

5, A wajen kyauta fa ba kamar saude 'yar sarkin kano na korau.

Taurari ko suna da haske basu kai hasken farin wata ba.

6, Inda mata suna sarauta a kano mukan muna da saude.

7, A zaria sunyi Quen Amina to mu a kano muna da saude.

8, A gabas na dangana da Borno ba kyakkyawa kamarki saude.

9, A yamma kwa har naje Ilorin ni banga ba wadda tayi saude.

10, ta nan kudu har zuwa Adamawa banga ba wadda tayi saude.

11, A arewa saida na wuce Nijar banga ba wadda tayi saude.

12, Kai duk matan dake cikin facebook babu wadda tayi saude.

14, Hotonki ana comment akanshi na kirga comment dubu a yanzu.

15, Ga allurar cikin duhu sai mai zurfin hankali ka tsinta.

16, Ga saude bakin zare a matoya sai mai hankali ka tsinta.

17, Ni burina a duniya inga kina mulkin kano sa'ade.

18, Allah ba yanda bai iya ba a zazzau shi ya bai Amina.

19, Ansa giwa cikin zubo taci guda bakin rabonta kelau.

20, Allah in yai nufi ga iko nai babu abinda zai hana shi.

Sunday, February 19, 2012

WAKAR DOKIN SARKIN GUMEL MUHD. SANI. DAGA MALAM AMADU DAN MATAWALLE.

1, Bismillahi rabbana Allah sarkin taimako ka kaini gumel gun sarkin gumel muhammadu sani.



2, Sake shiri muhammadu linzamin duniya uban na makwallah.



3, Na bar Hadejia ran asabat mutane suna ina mallam zaije sai nace Gumel zan jeni.



4, Kuma naje Gumel cikin sa'a sarki na ishe cikin barga tai.



5, Akwa wani doki yana Gumel mai kyau a cikin fada yai daban da dawaki.



6, Doki guda a bakin ran doki goma bidi dan yalawa.



7, Nagarta da kyan gani akwaita a gun bidi takamarsa abar kallo ce wajen rawa mazari ma yasan da bidi dan yalawa.



8, Dokin sarakunan iko ne jirgin saman dawakan lautai.



9, Dokin da ko yana barga tasa indai ka ganshi ka gama kallo.



10, sarkin Gumel uban malam sule kune kuke da mulkin lautai.


Zan kawo muku sauran baiti 5oma a gaba.

Saturday, February 18, 2012

WAKAR TARIHIN YAKIN HADEJIA DAGA MARIGAYI ALH. IBRAHIM KATALA!

1, Allahu sarki shi kadai yake wahidun sammai da kassai jalla bashi da kishiya.

2, Shi ba fari shi ba baki ba ubangiji ba ja ba ba alkashi bashi ga rawaya.

3, Ba sake sake ba ba kamar yarani ba shudi da kore jalla bashi da mai kama.

4, Zatinsa baya tattara bai rarraba da kawai da motsi bayayi ko sau daya.

5, Sarkinda ba na biyunsa ba na uku nasa ka dadan basira zanyi waken shahidu.

6, Ranar talata munga tashin duniya Rannan Muhammadu yai shahada zahira.

7, Shi yai jawabi ya fada shi bai gudu kuma bashi mai kamu a darul duniya.

8, Raggo ake kora a bishi a cim masa amma sadauki bai gudu sai faduwa.

9, Sarki Muhammadu yai jawabi ya cika shi bashi mai kamu a jashi ya tunkiya.

10, Dan melle sarkin yaki shima ya fada in dai da rai sarkinmu baya kamuwa.

11, Ma'ajin Hadejia saleh shima ya fada mun dau shahada zahira bahakikiya.

12, Manya da yara duk shirin yaki suke kowa yana wanka yana yin alwalah.

13, Kowa yana yin sallama a gida nasa sunsa gabansu a lahira ba dawaya.

14, Jama'ar Hadejiawa fa duk sun hallara kowa yana cewa fa mun zama shahidai.

15, Sarki Muhammadu mai shahadar zahiri ba badili ko dai cikin tawaga tasa.

16, Shi bai kamar tsoro ba baya razana kan ya ije ma babu sauran hanzari.

17, Ajali idan yayi babu kwana duniya kai dai zamo kullum shiri duka safiya.

18, Shi bai kamar tsoro a baya razana baya gudu dan Garba sarkin jarumai.

19, Mutuwa tafarki wanda kowa zayabi ai kulli nafsin dukka rai zai dandana.

20, Aka daura sirdi nai ya hau bisa ya tsaya yace mu dau himmar shahada zahira.

21, Sarki Muhammadu baya tsoro ko kadan Allah ma'aiki su take tsoro kadai.

22, Hauninsa linzamin mayani ya rike damansa tasbihi salatin annabi.

23, Dan mai karatu tudun kasa ba dawaya dan garba jikan sambo sarkin adalai.

24, Duk mai shahada auwalinsa madacima suka barace da fari ya mutu shahidi.

25, Farkon hawa yaki galadima sai haru ranar talata sun ka sauka a barzahu.

26, Alkali sarkin yaki kaura amada sarkin arewa da sunkaje can sun tsaya.

27, Suka jeru sunka tsaya a nan kofar gabas kafin suje har mai ruwa ya taddasu.

28, Kasan igwa dokinmu shi bai santa ba duka dokuna na faduwa ba lissafa.

29, Igwa tana tashi madafa na zuba yau sai ta Allah babu sauran shawara.

30, Jaruman Muhammadu basu tsoro ko kadan sun gwammace mutuwa da dai subi kafiri.

31, kuma sabo jikan tete harbi nai ake anan a kofar fada duk suka tuntsure.

32, Firyan Hadejia shi da bori na salihu kofar gabas suka fadi nan aka cim musu.

33, Dodo na zela da shi da gwanki barin nufe sun karbi hartashi a kwaryar kai nasu.

34, Ai babu mai mutuwa gaban ajali nasa kan surfa gero kan daka wasu sun fice.

35, iko idan Allahu yayi nufi nasa ai ba tsimi balle dabara ko daya.

36, Tamkar kamar inuwarka baka guje mata in kai gudun ta bika harma ka tsaya.

37, Hartashi na yawo kamar burduduwa tamkar zubar wake a can a masussuka.

38, Ya ratsa soraye ya ratsa katanguna tamkar kabewa ko kamar tumfafiya.

39, Yasha zarar soro ya keta katanguna da kago da zaure sun zube ba tambata.

40, Tsarnu da kurna har kasa durumi dada ya kar dabinai cediya da itatuwa.

41, Rannan Hadejia munga tashin hankali Allah da manzo su kadai ne magani.

42, Abdulwahabu baka tana hannu nasa artashi ya samar ya tsinke tsirkiya.

DA SAURAN BAITI SAI A SAURAREMU A GABA.

Friday, February 17, 2012

Wakar Yakin Hadejia da Turawa 1906. Daga marigayi Alh. Ibrahim katala.

Zan kawo mukuwakar da Marigayi Ibrahim katala yayiwa Shashidai wadanda suka mutu a yakin Hadejia da Turawa. Wato 1906. Wannan waka ta tabo sunayen jaruman Hadejia wadanda suka rasa ransu. Kamarsu Madacima, furya, sarkin yaki cilin Dan malle, sarkin baka Abdulwahabu, Ma'ji salihu, Kaura Amadu, da sauransu.

Tuesday, February 14, 2012

Sannu sannu!

Da sannu zan baku Tarihin Malam Amadu Dan-Matawalle da na Malam Mu-azu Hadejia. Shekarun da aka haifesu da kuma zamanin da sukayi da kadan daga cikin wakokin da sukayi.

Sunday, February 12, 2012

WAKAR MAIJIDDA DAGA M. AMADU DANMATAWALLE

AMSHI - Haka nan ne malam Ahmadu masu fasaha kanda gwamna kai aka yiwa firimiya.


1, Bismillah waka nai nufi tarihin malam amadu na hadejia wanda ake fadi.


2, A watan august ran litinin kwana daya nai wakar nana tarihin mai girkin dina.


3, Zamanin nan a Hadejia shi ba sarkin samari bane Allah ne yai masa martaba.


4, 'ya'yan sarki da na hakimai talakawa 'ya'yan tajirai a gidansa ake girkin dina.


5, zamanin nan a Hadejia abinda ya shirya babu mai rushewa malam amadu.


6, sai malam yai musu shawara aduba budurwa mai mukami Hadejia ayi mata gwamnati.


7, samari sai sukace masa a dallah asa mai jidda domin tafi budurwar zamani.


8, gurinda take ban al'ajab bata fushi mai jidda bata da girman kai kuma ga ladab.


9, in tana zance fa murmushi ga karamar murya a gunta kamar 'yan matan india.


10, sunan mai jidda hawa'u gwamnan 'yan mata a hadejia.

Allah sarki duniya!

Saturday, February 11, 2012

WAKAR MALAM AMADU DAN MATAWALLE! DAGA ISMAILA A SABO HADEJIA.


Amshi- Hakane malam amadi na idi ka kara shiri duniya ta Allah ce malam amadi.


1, Ku saurara jama'a zana baku labarin malam amadu, sa'ar Bayero sarkin kano yana mulki malam amadi.

2, Yajeshi kano ranar litinin ya dawo malam ran laraba, ana masha'a kwana takwas ciroma sunusi yana hakimi.

3, Yajeshi kano gun maina bashir da sarkin shanu da malam haruna su duka 'ya'yan sarkinmu ne.

4, Yajeshi kano suka gaisa dashi, domin shi mai kaunarsu ne, sa'ar da yajeshi ya samesu duk suna middle ba'a tasosu ba.

5, Malam sai ya wuce har bichi, yaje gurbin wambai Abubakar shima mai kaunarsa ne.

6, Wambai dan sarkin duniya, duk a kano ba tamkar Abubakar wane jikan sarki Alu.


7, Kyawu dan sarki ai a sanshi mai kyauta da halin arziki wambai yayi halin arziki.


8, Sai kuma taken malam na sidi ban kwana da mutanen kano malam zaya tsaya zakirai.


9, Malam yayi shirin duniya da safe da yamma mutane kuji, domin rainin wayon mahassada da magauta baya sake.

10, Yafi zuma zaki na haruna amma in ba'a fareshi ba, malam in aka fareshi ko madaci baiyi ya dacinsa ba.

11, Malam amadu ne kokuwar tabo ba dadi wan shekara, in kaine kayi kayen ka baci in ma kai aka kayar ka baci wanda ka duba kowa tabo.

12, Malam amadu ne kainuwa dashen Allah yaya zakuyi, wanda ya zauna kayin mahassada sai ya kauce zasu kau, ruwa sai ya kare kainuwa ta kare ba'a ga bayanta ba.

13, Malam amadu in yai adonsa randa yasa riga koriya, in ya fito ya kore mahassada sai yanda yace zasuyi.

14, Dumau yake ba fashi ko cikin sa'a daya bashi da dadin gamo, bangon dutse in kaki masu sarawa da diga sa gaji.

15, Talau yake kaifin adda na sidi malam mai zurfin hankali, tilan dan badi ko an daka a turmi sai ko yakai badi.

16, Zabgai yabin Bauchi da kare dangi maza sai kuy hankali, malam amadu baya sake kanin darasuma na malam barau.

17, Alqur'ani yaro da saurayi da budurwa in babu gaskiya aka dafa asha wuya.

18, Sarkin 'yan mata gaskiya wuka ce inda ka dokata sai ta kama mai nasara dole gaskiya tafi karya dadin fada.

19, Kaka sara kaka Hadejia kwado yaci kunama ashe, ko ya kama kafin ya karta su duka kowa yasha wuya.

20, Malam yai baiti sha tara, sai na cikon ashirin wanda zaya sanya dan ya zamo gargadi.

21, Mai gina ramin keta gina gajere dan juyin zamani, karka haka da tsawo domacin na baya su zosu suna shan wuya.

22, Tamat wa bi hamdi ilallahi zana saurara waka ta cika.

Friday, February 10, 2012

HADEJIA A SHEKARUN BAYA!

Hadejia a yau! A shekara arba'in da ta Gabata Hadejia tana da masallacin juma'a guda daya ne, wato masallacin cikin gari. wanda kuma ana zuwa sallar juma'a daga kauyukan kusa da Hadejian a wancan shekarun. kamar Kadume,Arawa,Yamidi,Ganuwar kuka,Hadin mai dan karofi, da sauransu. Da yake zamani juyawa yake kuma jama'a karuwa suke yau a Hadejia akwai masallatan juma'a kusan goma wanda kuma duk wanda kaje kai kace duk jama'ar garin suna can ne. To muna kara godiya ga Allah wanda da ikonsa ne komai yake gudana. Allah ya karo mana alkairi da zaman lafiya. a gaba zan baku labari akan kasuwar Hadejia duk a filin Hadejia a yau.