"" /> HADEJIA A YAU!: Apr 13, 2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, April 13, 2012

TARIHIN MU'AZU HADEJIA! DAGA TURAKAR SHA'IRAI

Tarihin Malam Mu'azu Hadejia, dan
takaitacce ne. Ya rasu yana da Shekara
38, domin acikin 1958 ya rasu. an haifi
Malam Mu'azu Hadeja a garin Hadeja,
cikin 1920. shine Bahaushe na farko da
ya fara rubuta Wakokinsa da rubutun
Boko. Wannan kuwa ya faru ne, saboda
acikin marubuta mawakan Hausa, shine
wanda ya fara samun cikakken illimin
boko. Dangidan Sarautar Hadejia ne,
shine dalilin da wakokinsa suka fi maida
himma wajen yada aqidun NPC a
madadin NEPU. Kila wannanne ya janyo
takaddama tsakaninsa da Malam Mudi
Spikin. Bayan kammala karatunsa ne, ya
fara aikin koyarwa a birnin Kano, har
kuma ya rasu aikin da yake yi kenan.
Nayi ta kokarin in san ko yabar baya,
amma har yanzu ban samu abin
kamawa ba. Na kuma yi kokarin in san
ko yana da iyali a birnin Kano, shima dai
ban samu abin kamawa ba. Sai dai naji
Shata na yiwa Inuwa Mai mai Kirari da
"Baban Mu'azu, wanne Mu'azu? Mu azun
Hadeja. Haji Inuwa Baban Yahaya" Na
kuwa so hakanne don ko zan sami wasu
wakokinsa da ba'a buga ba. Naji ya kan
yiwa kansa kirari da "V T maineman
albarka". Ga dai wata wakarsa, kafinmu
kawo muku wasu.
Bin Allah shine babban bi
Kuma sai kabi wanda ya haife ka
Ka kiyaye hududulLahi suna
nan amru da nahyu suna kanka
Wallahi Uwa da Uba sune
Hanyarka ta neman albarka
In sun gajiya bisa zamani
Sai ka dau wahalarsu da karfinka
Yi fata kadda ka sabe su
Wata rana Allah zai saka
Abinda ka shuka don ka sani
Shine ka tsirowa gonarka
In hairi, hairi zaka gani
In sharri, sharri zai bi ka
Wa adi'ulLahu fadar Allah
Kuma girmama wanda ya girme ka
Duk wanda ya raina fadar Allah
Shi ya bata ya auka halaka
Duk wanda ya raina fadar Allah
Shine muka cewa Dan Iska
Har shina wa kansa kirari, sau
rara kaji taken dan iska
Dan iska sandan Kuka da sun
gumi nai ba;a yin taki
Dusar buntu ba'a ba dabba
To kaji kirarin dan iska
Dan iska naman Balbela
Ba a cin shi da na Hankaka
Kilishin Jaba sai dan iska
Ba mai ci sai ko mai shirka
Kashin Bera baya taki
Balle kayi dokin ga-na-ka
Kiwon Yimka, kiwon banza
Wata ran zai gallabi yayanka
Ajiyar Bera ajiyar wofi
Bari murna sabon dan iska
Ni zan hore ka abokina
Bari jawo dan iska ajika
In har ka yarda ya rabe ka
Ba'alin jama'a sa tsarge ka
Zai koya ma mugun hali
Watakil a kira ka da dan iska
Da 'wa kullu karinin' duba man
Ta'alimi ka samu zancenka
Kuma ka zama Shaidanil insi
Sai hirzi kai da masoyanka
Kuma ka zama Fattani domin
Allah ma bai son ka
Ka girmama Allah da Ma'aiki
Da iyaye duk da sarakinka
Wa ulul amri minkum duba
Ka kiyaye fadar mahaliccinka
In ka rainawa sarakinka
Ka rainawa mahaliccinka
Bari jin kyashin baiwar Allah
Mai kaskantawa da daukaka
Shi yadda ya so haka nan zai yi
Da yayi su sarakai, kai talaka
Da yaso zai baka duniya
Ba komai ce ba ga Rabbaka
In yaso sai kaga ka gajiya
Har ka gaza amfanin kan ka
Kai dai riki aikin alheri
Kowa kaya nasa zai dauka
Shine sarki mai fifiko
Da kasanka, wadansu ko sun fi ka
Wani na da Jaka zambar Goma
Wani bashi Kwabo balle fataka
Wani kullum mota za shi shiga
Wani kullum kaya zai dauka
Da tuwon Baure da gudun kurna
Wainar shinkafa Annafaka
Ga Alkaki duk da Alkubus
Allah ya baiwa wadansu haka
Wani sai shi tsugunna kan titi
In anci a miko mai sadaka
Wani mata nai hudu ne, kuma ga
Soraye, Benaye, Taska
shimfidu, da kujeru, Darduma
ko ina sai kamshi ke binka
Sai fenti zane iri-iri
Ga lantarki, kuma ga fanka
Wani bin Zaure shi kayi domin
Wani kasuwa zai je shi faka
Suturar wani ganye ko walki
Ba rigarma balle shi saka
Shi kance daurin Allah,
Ya daure bawa nai a daka
Wani ga sutura nan iri da iri
Ya jibge wasu cikin adaka
Kullum sai ya sake tsari
Duk wadda yaso ita za shi saka
A gidan wani guda zaka ji don
A gidan wani kuka za'a saka
Kai ba'awa Allah tilas
Shi yadda yaso haka zai baka
Da abin dariya dana mamaki
Ba sa karewa ba shakka
Wai kura ce aka ce ta tu
ba da sata don tsoron halaka
Makiyayi sai amince har
Ya kafa mata turke cikin maruka
Shi mai hakuri shike dafa du
tse ya sha romo mai albarka
Ya Allah taimaki bayinka
Duk wanda yake son manzonka
Mu'azu Hadejia nan ya tsaya
V T mai neman albarka