"" /> HADEJIA A YAU!: 03/01/2013 - 04/01/2013

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Monday, March 25, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) PART THREE (3)

HADEJIA A YAU.


DAGA M. MUHAMMAD IDRIS HADEJIA.


SHEIKH USMAN KADUNA *************** ­ Sheikh Usman Kaduna,daya daga cikin manyan malaman Jihar Jigawa,kololuwa­r malunta a masarautar Hadejia, daya daga cikin jigogin "council of ulama" na jihar jigawa, shehi kuma madugun tafiyar Darikar Tijjaniya a masarautar nan. Gaba daya rayuwar malam akan yada ilmin addini ta kare.

Malam ya yi aiki a L.E.A a matsayin babban inspector na Arabiya.Ya sha yin Board Member a Hukumar Alhazai ta jiha.

Gidan malam jami'a ce ta masarautar Hadejia. Malam malamin malamai ne domin duk wani malami mai shekaru saba'in zuwa kasa in malam bai karantar da shi ba to ya karantar da malaminsa. Malam ­ ya yi nisa a fagen bayarda ilmi domin har daga kasashen ketare ana zuwa wannan jami'a tasa.


Almajiran malam ne suka fara kafa Islamiya ta dare domin magance hira marar amfani da matasa kan yi a cikin wannan gari.

Malamyana gabatar da tafsiri a kowane watan azumi a dukshekara wanda ke samun halartar jama'a masu yawa. Bayan karantarwa ta yau da kullum malam yana karantar da hadisi a ranar kowace juma'a tsakanin magariba da isha'i. Allah ya karawa malamlafiya ya kuma ba shi ladan Ayyukanda yake na Alkairi.


ALHAJI HASHIMU AMAR(WAZIRIN HADEJI)*************** ­* Alhaji Hashimu Amar yana daya daga cikin tsofin 'yan bokon wannan masarauta, ajins­u daya da marigayi sarkin Hadejia Alh. Abubakar maje tun daga firamare har midil (Middle).


Alhaji Hashimu Amar a"internal revenue" ya yi aikinsa har ya kai kolokuwawato babban Darakta kuma anan ya yi ritaya. AlhajiHashimu ya dauki ma'aikata matuka a wannan masarauta har ma da wajenta.

Alhaji Hashimu dattijo ne mai gaskiya da rikon amana ya kare mutuncinsa da na masarautarsa matuka don haka wajen daukan aikinsa bai nuna kabilanci ba, babu ruwansa da kusa ko nesa, ko na gari ko kauye.

Wannan ya kara masa mutunci matuka a wannan masarauta. Alhaj­i Hashimu ya zama wazirin Hadejia a lokacin Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje kuma kullum yana hanya domin samo ci gaban wannan masarauta.

Hadejiawa suna masa addu'a Allah ya albarkanci zuriyarsa.

Saturday, March 23, 2013

HADEJIA EMIRATE

HADEIJA A YAU.

Authority : Mr. A. Campbell-Irons.

The Emirate of Hadejia contains an area of 2,768 square miles, and is divided into six Districts. It is situated to the north-east of Katagum, in the Northern Division. It is a disputed point whether in the tenth century.

Hadeija or Gobir formed one of the seven Haussa States. In the Kano Chronicle there is a mention that the son of the Sarkin Machina came to Kano in the reign of Yakubu (1452-63) and was made Chief over Hadeija, with the title of Sarkin Gabbas.

It became a Fulani Emirate at the time of the Jihad, Sambo receiving a flag from Othman Dan Fodio. His elder son Buhari made himself King in defiance of the Sarkin Musulmi's edict in favour of his younger brother ; and, obtaining the support of the Shehun Bornu, defeated all opponents. His reign was one long succession of wars and he was finally killed in battle at Gorgaram about 1863.

Hadeija sent in submission to the British in 1903. In 1904 the British occupied the country, but the fifth Chief opposed their advent and was overthrown and killed in 1906, and Haruna appointed in his place. He died in 1909, and was succeeded by the Chiroma Abdulkadir.

In that same year the Beiyut-el-Mal (Baitilmalu) was started.

The population number some 115,448, and consists of Kanuri, Fulani, Auyokawa, Maguzawa from Kano, Koyamawa, Beddawa, Ngizimawa, Mangawa.

There is a town of historic interest in Hadeija named Garungabas, but which in old times bore the name of Biram, which was originally of great influence. It was founded by Arabs from Bagdaza or Baghdad. One Muktari, or Bayajibda, with his younger brother Biram, Migrated west until they reached Birnin Bornu (Kukawa), where the Shehu gave Muktari a town and his daughter in marriage. Muktari was presently compelled to flee, but left his wife on the road, where she gave birth to Biram, who founded Garin Gabbas, Muktari continuing his journey as far as Daura, where he slew the celebrated serpent and married the Queen.

Another version of the legend is that it was Buram, the younger brother, who founded Garingabas.

A descendant of this Arab family still reigns as Chief. Hadejia A yau.

Tuesday, March 19, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) Part two (2)

Image Hosted by ImageTitan.com Hadejia A yau! Daga M.MUHAMMAD IDRIS.. A cigaba da kawo muku Takaicaccen tarihin wadanda suka bada Gudunmawa a kasar Hadejia, yau mun tabo Mutum Uku wadanda tarihin Hadejia bazai manta dasu ba!


AIR VICE MARSHAL HAMZA ABDULLAHI(RTD) *************** AVM Hamza Abdullahi. Daya daga manyan hafsoshin soja na kasa, daya daga cikin manyan arewa, tsohon Gwamnan Jihar kano, tsohon ministan Abuja, tsohon ministan aiyuka na musamman. Avm Hamza yayi mulki na wata 18 amma ya yi aiki na mamaki a fadin jihar kano.


Aiyukan da suka shafi masarautar Hadejia sun hada da: ginin hanyar Bulangu da Guri, ginin Asibitin Birniwa, K/Hausa da Bulangu, ginin makarantun mata na kaugama da Birniwa, ginin kwaltocin cikin garin Hadejia da gina fadar Hadejia ta zo daidai da zamani. karin streets light. .


Lokacin yana ministan Abuja ko 'yan kwangila da dama sun samu aiki, manyan mutane da yawa sun samu fulotai, ya samarwa matasa karatu a institute of management ta Abujan.


Avm Hamza bayan ya bar Gwamnati ya ci gaba da bayar da gudunmawa domin ci gaban al'ummarsa ya gina katafaren gida domin saukar bakin kunya, ya gina masallaci na juma'a mahadi ka ture ya kuma tanaji makeken fili a yamma da masallacin domin gina makaranta, yana kawo masu Likitocin ido domin masu larurin ido.


Avm yana daukan yara masu karamin karfi ya kaisu Turkish School in sun gama ya nema musu admission a kasa ko a waje,yanzu haka akwai yara biyu a kasar Turkey wanda shi yake daukan nauyinsu. Tsakanin Avm. da masarautarsa akwai kauna domin ba sallar da za ta zo bai yi ta a Hadejia ba sai in ba ya kasa. Muna masa fatan alheri da karuwar arziki mai amfani.



ALHAJI BELLO IBRAHIM AUYO **************** Marigayi Alhaji Bello Ibrahim Auyo. "Agogo sarkin aiki" tsohon malamin makaranta, gogaggen dan siyasa. Ya fara aiki tun daga malamin makaranta har ya kai mukamin sakataren ilmi.


Ya rike mukamin kwamishinan zabe tun muna jihar kano. Ya yi shugabancin karamar hukumar Hadejia har sau biyu. Shi ne shugaban ALGON na kasa.


Alhaji Bello Ibrahim ya fi kowane shugaban karamar hukuma da aka yi a Hadejia aiyuka na raya gari. Alhaji Bello Ibrahim ne ya gina sakatariyar karamar hukumar Hadejia da ake cikinta, shi ne ya gina Asibitin Kofar Arewa da shagunan bayanta, shi ne ya gina kasuwar jan bulo. Bello ya dauki ma'aikata da malaman makaranta masu yawa a zamaninsa. A zamaninsa matasa masu yawa sun samu muhalli domin ya raba filaye da dama a wurare masu yawa.

Misali shi ya raba filin idi kuma ya sanyawa wurin suna Unguwar Mu'azu Hadejia,


ya bayar a fanisau kuma shi ya sayarwa mutane gidajen fanisau, ya raba a gabari, ya raba a Gandun Sarki.

Bello ya yi ginan magudanan ruwa ba adadi a Hadejia. Yayi aiyuka a Auyo lokacin muna hade da ita.

"Turmin tsakar gida sha gwagwarmaya"
Bello mutum ne mai riko da addini, jam'i ba ya wuce shi, ya rike dangi musamman marayu, da azumi a bakinsa Allah ya karbi ransa. Allah ya sa ya sha ruwa a Aljanna, ya yafe masa kura-kuransa.......



ALHAJI ADAMU KWANO *************** Alhaji Adamu kwano tsohon ma'aikacin lafiya ne wanda ya bayar da gudun mawa matuka a wannan fage. Allah ya yi masa fikira kwarai domin shi ba likita ba ne amma yakan yi aikin da ya gagari likitoci.


Adamu kwano ya shahara akan kaciya domin galibin matasan Hadejia da kewaye daga 'yan shekara 30 zuwa 50 duk yawanci shi ya musu shayi.

Alhaji Adamu kwano attajiri ne mai son ci gaban addini, shi ne ya gina makarantun islamiya ta Hudu da Garko da makarantar sakandire ta Aminu Yusuf.

Adamu kwano shi ne mutum na farko da ya yi kokarin gina Asibiti mai zaman kanta sai dai ba ta fara aiki ba Allah (SWT) ya yi masa rasuwa.

Muna rokon Allah(SWT) ya ji kansa yaarzurta mu da masu hali irin nasa. AMEEN.

Monday, March 18, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) Part One (1)

Image Hosted by ImageTitan.comHadejia A yau! DAGA MUHAMMAD IDRIS HADEJIA


Shirin Taurarinmu zai Rinka tabo takaicaccen Tarihin Mutanen Kasar Hadejia da Irin ci gaban da suka bata, Domin kaima ka bada taka Gudunmawa. Kuma zamu fara da takaicaccan Tarihin.......


ALHAJI HAMZA TURABU *************** Alhaji Hamza Turabu. Bahadeje mazaunin kano. Alhaji Hamza tsohon ma'aikaci ne a Hukumar Aikin Gona ta Jiha. Yana rike da mukamin Director Forestry tun muna kano har muka zo jigawa kuma akansa ya bar aiki.

Dattijo ya yi wa mutane da yawa hanyar samun aiki musamman a Ma'aikatar Aikin Gona kuma shi ne ya assasa filantaishin masu yawa da muke gani a yau fadin kano da jigawa.

Alhaji Hamza mutum ne mai son ya ga matasa sun yi karatu shi ya sa gidansa ya zama mazaunin Dalibai 'yan wannan masarauta har a yau. Hadejawa suna ma addu'a Allah ya albarkanci zuriyarka. Amin.


SHEIKH MUHAMMAD LAMIN KHAN (MALAM MODIBO YALLEMAN) **************** Marigayi Sheikh Muhammad Lamin Khan yana daya daga cikin dattijon 'Yalleman, daya daga cikin malaman addini na wannan masarauta, shine bubban Limamin 'Yalleman.


Malam Modibo ya zaga kasashen Afirka da dama akan neman ilmin addini kuma ya same shi domin ya karantu a bangarori na addini dabam-dabam. Ana zuwa har daga garuruwan makwabta a dauki karatu a wurinsa.


Bayan kasancewar gidansa makaranta ce shi ne ya assasa Makarantar firamare ta Madani da kuma Sakandiren Madani. Matasa da yawa cikin garuruwan 'Yalleman, Dakayyawa, Hadiyin, Ubba, da kewaye a wannan makaranta suke karatu. Malam Modibo ya hada duk wani hali na dattako da ake so,don haka yake da girma a idon jama'a a ciki da wajen wannan masarauta.


Muna addu'a Allah ya sa kur'ani ya cece shi. Amin.


HAJIYA LAMI AMINU KANI *************** Hajiya Lami Aminu Kani 'ya ce a wurin Sarkin Fulanin Hadejia Alhaji Daudu Saleh. kuma matar na hannun daman AVM Hamza Abdullahi, wato Alhaji Aminu Kani. Hajiya Lami tana daya daga cikin tsofin 'yan boko mata na wannan masarauta.


Hajiya Lami babbar ma'aikaciya ce a hukumar bayar da wuta "PHCN" Kuma zamanta a wannan wuri ya amfanar da wannan masarauta matuka domin idan ka kasa masu aiki a PHCN na wannan masarauta kashi dari Hajiya Lami ce ta kai kashi saba'in daga cikinsu PHCN. Mace mai kamar maza.


Hadejawa sun baki Sarkin Fulanin Mata. Muna addu'a Allah ya kara daukaka. Amin.

Saturday, March 16, 2013

SAKO ZUWA GA MASU AMFANI DA FACEBOOK.



Hadejia A yau!Shafukan INTERNET da Wayar Hannu ta GSM....Bincike ya nuna cewa shafin internet na FACEBOOK da wayar hannu ta GSM suna daga cikin ababen dake kara rura wutar fadan addini a Nigeria.

Hakan yana faruwa sakamakon irin yadda mutane ke amfani da su wajen isar da sako atsakaninsu. Mutanen mu suna da son bayar da labari,Inma ingantacce ko mara inganci don neman addu'ar 'yan uwansu ko don nuna bajintar su ko kuma don wata manufa ta su ta daban.

Wannan yasa dayawa sukan fadi abinda basu da tabbas akansa, ko kuma suyi kari cikin labarin na su.

Ya kai dan'uwana mai son bayarda labari! Kaji tsoron Allah, kada kafadi, ko kada karubuta sai abin da kaji ko kagani kokuma kake da tabbas akansa. kasani za ka amsa tamyar Allah akan abinda kake fadi kokuma kake rubutawa a duniya (facebook), wacce amsa ka tanada?

Ba wani abin birgewa bane afara jin labarin dake tayar da hankali agurinka. Addinin muslunci ya hore mu da yin magana ba tare da ILIMI ba. Mu kiyaye ko Allah (S.W.A) ya kiyaye mu.

Ya Allah! Kakiyaye mu, kabamu zaman lafiya, Amin.

Haka kuma a Facebook zakaga GROUP ko PAGE wadanda basu da Aiki sai watsa Labarin karya. Misali sai a saka Hoton Yarinyar da bata jiba bata Gani ba wai Ace tace tana neman Miji. Wanda kuma Addinin Musulunci bai yarda da hakan ba.

Kuma 'yan mata kuji tsoron Allah duk abinda ya sameku kuke Janyowa kanku. Domin kune kuke yawan sauya Hoto dan ku Birge mutane!

A garin hakan kuma sai a samu wasu bata gari suyi downloading din hoton su dinga Talla daku.

Ko kuma Namiji ya Bude 2go da sunan mace yasa hoton wadda bata jiba bata gani ba. Wai dan ya yaudari 'yan Iska 'yan'uwansa. Allah ya kiyaye mu.

To Jama'a sai mu kula da fadar jita jita, domin karya haramun ce. Allah ya kare mu amin....

Friday, March 15, 2013

KUDUBAR JUMA'A DAGA BUBBAN MASALLACIN HADEJIA.

HADEJIA A YAU. A yau malam Na'ibi yi mana kudubace mai taken :- JIN TSORO DAGA AZABAR ALLAH S.W.T. Fassara:- Ibrahim Umar. Yan uwana musulmai Malam ya ja hankalinmune game da jin tsoro daga azabar Allah Mai Girma da Daukaka domin kamun ubangiji ya kasance mai tsananine. Yan uwana kullun mu cigaba da kasancewa daga cikin bayin Allah Madaukaki masu da'a tare da jin tsoron azabarsa. Kada mu kasance daga bayi azzalumai masu zalintar kansu wajen keta Abubuwan da musulunci ya hana. Manzon Allah S.A.W yana cewa "kuji tsoran wuta ko da da tsagin dabino ne" Ma'ana koda abin da zakayi sadaka dashi kamar tsagin dabinone don ka bayar dashi ka kare kanka daga wuta to kayi kokari ka bayar. ALLAHUMMA INNA NARJU RAHMATIKA WA NAKHAFU AZABAK. ya Allah SWT ka karemu daga azabar wuta amin.

Monday, March 11, 2013

FACEBOOK A KARKARA!

HADEJIA A YAU!Hadejia A yau! Assalamualaikum! 'Yan uwa barkanmu da yau, da fatan Alkairi. muna gaf da fara wani shiri a wannan shafi na facebook. shirin kuwa zai leka ne loko na kauyukan Arewacin Nigeria, domin jin halin da talakawa suke ciki a kauyuka da karkara. domin wasu kauyukanma ba'a kulasu sai an buga gan-gar siyasa. Sanin kowane Talakawa akar-kara suna cikin mawuyacin hali fiye da na biranen Arewacin Nigeriya. Ada sashin hausa na gidan redion b.b.c. yana gudanar da wannan shiri wanda kuma yin hakan na sanya gwamnati ta gyara kura-kuranta. To amma yanzu shiru muke ji ba labari. Hakan yasanya mu yin azama wajen gabatar da wannan shiri ta hanyar fcbk. kasancewar shugabanni na amfani da shafin na fcbk. Duk da ma dai sunsan halinda ake ciki to amma fadawa duniya zai kara sanyasu su gyara. Kaima kema zaku iya shiga wannan shiri ayi da ku domin yin hakan jihadi ne bubba wanda Allah ne kadai yasan ladan da zaka samu. Domin ka yi sanadiyyar fitar miliyoyin alumma daga cikin Kangin talauci. Duk mai bukatar ayi wannan aiki da shi ya Tuntubi Garba Tela Hadejia ta inbox. Ko ya kira lambarsa ko ya masa sakon Wasika (text). 07065540705. Allah ya bada Iko.

Thursday, March 7, 2013

HUKUNCIN GADO DA MASU CIN GADO. KASHI NA DAYA (1)

HADEJIA A YAU! Assalamu Alaikum! Wannan babi zai yi bayani a kan masu gado a cikin maza, da masu gado a cikin mata. Sannan babin zai yi bayani akan irin bambancin darajojin magada. (1) MASU GADO A CIKIN MAZA Masu gado daga cikin maza, su goma (10) ne! Ga jimlarsu, amma idan aka rarraba su, su goma sha biyar ne, (15) kamar haka:- 1. Da (Na tsatso) 2. Dan da, (Jika har zuwa tattaba kunnansa) 3. Uba (Na ciki) 4. Kaka namiji (Na wajan uba, har zuwa Sama) 5. Dan'uwa shakiki (Na uwa daya, uba daya) 6. Dan'uwa li'abi (Na uba daya, uwa daban) 7. Dan'uwa li'ummi (Na uwa daya, uba daban) 8. Dan dan'uwa shakiki (Na uwa daya, uba daya) 9. Dan dan'uwa li'abi (Na uba daya, uwa Daban) 10. Kanin uba, shakiki (Na uwa daya, uba daya) 11. Kanin uba li'abi (Na uba daya, uwa daban) 12. Dan dan kanin uba, shakiki (Na uwa daya uba daya) 13. Dan dan kanen uba, li'abi (Na uba daya uwa daban) 14. Miji. 15. Ubangijin bawa. Hadejia A yau! MASU GADO A CIKIN MATA Masu gado a cikin mata su bakwai ne (7) Ga jimlarsu, amma idan aka rarraba su, su goma ne, (10) kamar haka:- 1. 'Ya ko Diya (Ta tsatso) 2. 'Yar da, (Na tsatso duk yadda ya yi nisa) 3. Uwa 4. Kaka mace (Ta wajan uba) 5. Kaka mace (Ta wajan uwa) 6. 'Yar'uwa shakikiya (Ta uwa daya, uba daya) 7. 'Yar'uwa, li'abiya (Ta uba daya, uwa daban) 8. 'Yar'uwa, li'ummiya (Ta uwa daya, uba daban) 9. Matar Aure 10. Uwargijiyar bawa ko baiwa. Hadejia A yau! MASU GADO DARAJARSU TANA DA BAMBANCI DA JUNA Masu gado suna da bambanci da junansu. Ma'ana gado ba abu ba ne wanda za a ce a raba shi daidai, a tsakanin magada. Dole ne a raba shi yadda Allah Madaukakin Sarki Ya raba shi cikin hikimarSa. A rabon gado wani ya fi wani rabo. Wani kuma ba ya da rabo in ga wani. Wani kuwa zai tashi daga wani rabo ya koma ga wani rabo, saboda samun wani tare da shi. Wani kuma zai kada wani; wani sauran dukiya yake kwashewa. Saboda haka za mu bi su dalla-dalla, domin mu yi bayaninsu, in sha Allahu. MASU FARALI Za mu fa ra da bayanin abin da ake nufi da masu farali. Masu farali su ne wadanda Allah Madaukakin Sarki Ya ambaci rabonsu a cikin Alkur'ani Mai girma. wadannan su ne kamar haka: 1. 'Ya (Ta tsatso) 2. 'Yar da (Na tsatso) 3. Uwa 4. Uwar uwa 5. Uwar uba 6. Dan'uwa li'ummi (Na uwa daya) 7. 'Yar'uwa li'ummiya, (Ta uwa daya) 8. Miji. 9. Mata. MASU ASIBCI Za mu fara bayani a kan abin da ake nufi da asibi. Asibi shi ne wanda idan a ka zo wajan rabon gado, zai tsaya har a fitar wa masu farali, farilinsu, sannan abin da ya yi saura ya kwashe, za mu jera su kamar haka: 1. Da (Na tsatso) 2. Dan da (Na tsatso) 3. Dan'uwa shakiki, (Uwa daya uba daya) 4. Dan'uwa li'abi, (Na uba daya) 5. Dan dan dan'uwa shakiki (Uwa daya uba daya) 6. Dan dan dan'uwa li'abi, (Na wajan uba) 7. Kanin uba shakiki (Uwa daya uba daya) 8. Kanin uba li'abi, (Uba daya uwa daban) 9. Dan kanin uba shakiki, (Uwa daya uba daya) 10. Dan kanin uba li'abi, (Uba daya uwa daban) 11. Wanda ya 'yanta bawansa. 12. Wadda ta 'yanta bawanta. MASU ASIBCI WANI LOKACI WANI LOKACI SU KARBI FARALI Wadanda ke yin asibci wani lokaci, wani lokaci kuma su amshi farali, su ne kamar haka: 1. 'Yar'uwa shakikiya (Uwa daya uba daya) 2. 'Yar'uwa li'abiya (Uba daya uwa daban-daban) MASU ASIBCI WANI LOKACI WANI LOKACI SU KARBI FARALI WANI LOKACI SU HADA DUK Wadanda ke yin asibci wani lokaci, wani lokaci kuma su amshi farali, wani lokacin kuma duka gaba daya, da asibci da farali. Sune:- 1. Uba. 2. Kaka namiji. MASU GADON NISFI Kafin mu yi bayanin masu gadon nisfi, ya kamata mu san mene ne nisfi? Nisfi kalmace ta Larabci. Ma'anarta rabi (1/2). Idan an raba wani abu biyu, kowane daya daga cikinsu ya zama nisifi ke nan. Masu gadon nisfi (Rabi), su biyar ne kamar haka: 1. Miji. 2. 'Ya (Ta tsatso) 3. 'Yar da (Na tsatso) 4. 'Yar'uwa (Ta uwa daya, uba daya) 5. 'Yar'uwa (Ta uba daya, uwa daban) Wadannan su ne masu nisifi. Za mu bisu daya bayan daya; mu yi bayanin su dalla- dalla, ta hanyar da za a fahimta, in sha Allahu, domin ko wanensu yana da sharuda. Alhamdulillahi.

Tuesday, March 5, 2013

WA YA KAMATA YA TSAYA A BAYAN LIMAN?

Hadejia A yau! Assalamu Alaikum! Godiya ta tabbata Ga Allah wanda ya Halicci Mutum da Aljannu dan mu bauta masa.

Tsira da Aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu, wanda Allah ya Aikoshi da Alqur'ani da Salloli guda Biyar (5).

Bayan haka Al-ummar Musulmi Musulunci yana da tsare tsare wanda Idan ka bisu zaka rabauta! Hakika Tsayuwa a bayan Liman a yayinda ake sallah ba na kowa bane na Masana ne! Domin Idan Liman yayi kuskure a sallah sune suka san Irin abinda zasu fada masa dan ya gyara.

Idan wanda baida Ilmi ya tsaya bayan Liman kuma aka samu akasi Liman yayi Kuskure kana tunanin zai iya gyara masa? Bazai iya ba, saidai ya sake batawa.

Manzo (s.a.w.) yana cewa :- An sanya muku Liman dan kuyi koyi dashi, Idan yayi Ruku'i kuyi Ruku'i, Idan yayi Sujudi kuyi sujudi.

Danme zakayi abinda Liman baiyi ba?

ZAN BAKU LABARIN MUJRIMI... Mujrimi wani Balaraben Kauye ne! Yazo Birni kuma Sallah ta Magriba ta kamashi sai yazo yayi Alwala ya tsaya a bayan Liman. Sai akayi Sa'a Liman ya karanto Ayar nan da take cewa:-

Alam Nukhliqil Awwalyn? (Fassara) shin bakuga yadda muka Halakarda Mutanen farko ba? Sai Balaraben kauye ya fice daga sahun farko ya koma sahu na biyu.

Sai Liman ya sake karanta Summa Nutbi'uhumul-Akhiriyn. (fassara) sannan haka muka aikata ga mutanen baya. Sai Balaraben kauye ya koma sahun Karshe.

Sai Liman ya kara karanta Kazalika Naf'alu bil- Mujrimiyn. (fassara) sannan haka Muka aikata ga Mujrimai.

Sai Balaraben kauye ya fita a guje yace Ni ake Nema. Domin yaji an ambaci kamar sunansa. To dan Allah me ya janyo haka? Allah yasa mu Gane.