"" /> HADEJIA A YAU!: 08/01/2013 - 09/01/2013

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, August 28, 2013

DANGANTAKA TSAKANIN BIRNI DA KAUYUKAN KASAR HADEJIA. DAGA M. HUSAINI SHEHU..

Hadejia A yau!
Daga M. Hussaini Shehu


DANGANTAKAR BIRNI DA KAUYE

Dangantaka tsakanin birni da kauye a kasarmu ta Hadejia tanada tsohon tarishi. Yana da wuyar gaske kasami bahadeje ko bahadejiya dake birni ko kauye da bashi da gidan yan’uwa ko gonar gado a daya daga wadannan wurare dana ambata.DA

Bukukuwan sallah-: shekarun baya zakaga kowane gida cike da baki yan’uwanmu na kauye sunzo cikin Hadejia domin sada zumunci da juna da kuma kallon buku kuwan sallah.

Wannan al’ada tamu tataimaka wa kasarmu sosai wajen jaddada hadinkai a tsakaninmu , kuma tataimaka wajen kawarda kyama tsakanin junanmu. Yanzu a wannan zamani irin wannan kyakkawar al’ada tamu tazama tarishi, sai ayi bukukuwan sallah a
gama bazakaga kowa a gidajenmuba. Kai koda wakilan kananan hukumominmu dawuya kasami guda uku daga cikin takwas sunzo domin sada zumunci kamar yadda akeyi a shekarun baya.


Kuma abin mamaki saika iske sauran masarautu bahaka sukeba, zakaga kowane shugaban karamar hukuma yazo sun hallara domin tattauna matsalolin wannan masarauta.




Shin minene yajawo
hakan? Nomi jide-: Inna tsammanin wannan al’ada tamu itace tasa ake cemana “Hadejia tsintsiya madaurinki daya”. Watau dadama daga cikin mutanan dake cikin Birnin Hadejia a shekarun baya sunada gidajensu nagado dakuma gonaki a kauyuka, aduk lokacinda damina ta sauka sukan koma gidajensu dake kauyuka
domin yin noma. Bazasu dawo gariba sai bayan damina. Zan iya tunawa mahaifina wata shekara muna shira game da wannan dabia tamu, sai yace mini: aduk cikin lokonmu gidanmune kawai yake ragewa da mutane idan damina ta sauka. Sauran makwabta kowa yakan koma kauye dominyin noma.


Saboda haka yan’uwa tayaya idanba hudubar shedanba zamu banbanta mutumun birni da kauye? Amsata shine duk mutumin kauyen Hadejia Dan Garin Hadejia ne sannan kuma duk mutumin Birnin Hadejia dan kauyen Hadejiane.


Tambaya anan itace idan Maganar danayi a baya gaskiyace, shin akwai maana idan mukayi maganar rabuwar kawuna tsakanin mutumin kauye dana birni?


Ga-manda-: wannanma wata tsohuwar al’adace tamu ta Hadejiawa da take kara nuna mana karfin dangan taka tsakanin kauye da birni. Bayan al’adar Nomu jide wanda kamar yadda nafadi a baya take nufin zuwa kauyukanmu da damina donyin noma, idan mungirbe mu kwaso amfanin zuwa gidajenmu na birni. Ha’ilayau mutumin birni musamman ma Mata sukan je ziyarar yan’uwa kauyu kammu bayan an kawo amfanin gona gida.


Ayayinda zasu tafi sukanyi guzurin
kayan miya wanda baa fiya samunsu a karkaraba, sukuma ayayin da suka gama zayararsu, yan’uwanmu na kauye sukan basu
amfanin gona kamar su: gero, dawa, wake dadai sauransu domin yin guzuri. Inna tsammanin wannan alada tamu haryanzu tananan anayinta tsakaninmu, to kaga kuwa ashe idan akwai wadannan dagantaka to ashe gaba dayanmu Hadejiawa yan’uwan junane. Saboda haka miye dalilin rabe raben kawuna tsakanin kauye da birni?




Sarauta-: Kowa yasani Sarautarmu ta Hadejia dama ta sauran kasashen Hausa ana nada Mai sarauta watau hakimi ko dagaci daga cikin yayan sarakai dake cikin gari a turasu kauyukammu domin yin mulki. Sannan ayayin
da hakimi zai tare kasarsa yakan tafi da sauran yaransa wadanda zasu tayashi mulki yazuwa kauye. Kuma dadama daga cikinsu idan sukaje zasu auri mata acan daganan sunzama yan can kauyen.


Shiyasa duk wani mai sarauta ko yaran mai sarauta a kauye idan aka binciki tarishinsu zaka iske zuwa yayi tare da hakiminsa ko dagacinsa Watau mutumin birnin Hadejiane, musamman ma da ya kasance al’adarmu ta Hadejiawa ta banbanta data Kanawa maana duk wanda fada ta tura kauye domin wakilci to zai zauna ne dindindin watau babu canji. Shiyasa idan shekaru sukayi yawa bama iya gane cewar zuwa mukayi donyin sarauta ba a nan muke ba shekarun baya. To amma abin mamaki saika iske yaron hakimi ko dagaci yana korafin nuna banbanci tsakanin birni da kauye. Shin akwai ma'ana a wannan dabia?


Allah yasa mugane.

Sunday, August 11, 2013

JAWABIN ALH. BAIDI GAJO YELLEMAN A BUBBAN TARO DA AKAYI DON HADIN KAN Al'UMMAR MASARAUTAR HADEJIA. (KASHI NA DAYA 1)

Free Web Proxy
Jamaa Salamu Alaikum. Na tsaya gabanku ne a game da izinin da aka mani akan in yi bayani gameda “Cusawa matasa kishin masarautar Hadejia”. Shi dai kishi wani kauna ne da mutun yake dashi na wani abu, ko Kasa, Addini, Mutum da sauransu. Misali Kishin da mutum yakewa kasarsa, Mace da take game da mijinta, mutum yake game da addinsa. Wannan tsanannin kishin zai iya sa mutum yayi dukkan abinda zai iya domin yaga cewa ya amfani abinda yake kishin kuma yakare
martabarsa. Kakan yi amfani da kishi don ka cimma kyakkyawar manufa mai amfani.


Wani babban alamarine da zai sa kayi duk abinda zaka iyayi iyakar karfinka domin shi wanda kake kishin ko abinda kake kishin.


Kasar Hadejia al’ummace da Allah Yayiwa dimbin albarka ta fannoni daban daban na rayuwa Kamar dimbin masu Ilimin addini dana zamani, Manyan Sarakuna, Attajirai, Manyan yan siyasa, Manyan Maaikata tun shekaru aru aru. Idan nace kasar Hadejia ina nufin Hadejia, Auyo, Birniwa, Guri, Kafin Hausa, Kaugama, Kiri kasamma da Malam Madori.


Bari muga yanda maganar kishi ta shigo a harkar jamaar Hadejia. Sanin kowane cewa yakamata ace Hadejia ta wuce inda take dinnan kasancewarta Mai sarautar daraja ta daya tun shekaru aru aru, kuma mutanenta ne suke mamaye aikin Gwamnati tun Kano State har yanzu a Jigawa State sannan kuma a gwamnatin tarayya. To amma har yanzu mun san akwai sauran abubuwa da yawa da muke bukata don mu cimma burinmu na samarda abubuwan more rayuwa ga jamaarmu. Su
wadannan abubuwan more rayuwa kuma suna samuwane ta hanyoyi daban daban. Jamaa zasu taru su hada karfe da karfi don su
samarda wadannan abubuwa.


Amma almuhimmi shine abinda zaa samowa jammaa daga hukuma, wato Gwamnati.
Hanyoyin samu wadannan abubuwa shine zai nuna tsananin kishin da zakayi na samosu daga hukumar da abin ya shafa. Babban
maaikacin Gwamnati zai iya samawa matasa aiki a gwamnati, zai iya kawo Maaikata (Project), ko Makaranta, Titi, Asibiti. Ko ruwansha a bangarensa. Dan Siyasa zai iya amfani da mukaminsa yakawo duk abubuwan da na lissafa a sama. Attajirai zasu iya kawo kamfanoni. To idan wadannan suka hada karfe da karfi, nan da nan zaka ga
abubuwa sun bunkasa ta kowane fanni kuma jammaa sun sami biyan bukata. Ina tunanin ko muna da irin wannan tsananin kishi da nake nufi anan. Idan kuma muna dashi, to ina tunani ko muna amfani dashi yanda yakamata don ciyarda alummarmu gaba.


In Ciyaman Local Government bashi da kishi, ina zaiyi aiki?


Idan Dan Majalisa bashi da kishi, ina zai yiwa jamaa kyakkyawan wakilci?


Idan babban maaikacin gwamnati bashi da kishi, ina zai kawo ayyuka (Projects) garinsu?
Da sauransu.


Anan ina so inyi wasu yan tambayoyi: MU HADU A KASHI NA BIYU (2) DON JIN TAMBAYOYIN.

JAWABIN ALH. BAIDI GAJO YELLEMAN A BUBBAN TARON HADIN KAN AL'UMMAR MASARAUTAR HADEJIA. (KASHI NA BIYU 2)

Free Web Proxy Hadejia A yau.


Anan ina so inyi wasu yan tambayoyi:


1. Kana da kishi ne sai ka jira Mai Martaba Sarki ya tura ma tawaga a gaya maka jamaar Hadejia suna bukatar abu?


2. Kana da kishi ne sai ka jira har jamaa sunyi zanga zanga kafin ka biya musu bukata?


3. Kana da kishi ne baka son zuwa garinku ko cikin jamarka?


4. Kana da kishi ne kake yiwa garinka shigar dare kuma a mota mai tinted glass don kada a ganka?


5. Kana da kishi ne zaka rike mukamin gwamnati har kayi ritaya baka kari jamaarka da komai ba? Da sauransu.


Shi kishi ne zai sa kayi abu ba sai an sa ka ba, kuma in kayi ba sai an gode makaba. Rashin wakilci mai kyau duk rashin kishi ne yake kawo shi. Saboda haka idan dai muka dore akan wadannan abubuwa biyar da na lissafa a sama, to gaskiya babu inda zamu.


A duniyarmu ta yau, da wuya wani ya dafa maka abinci ya sa ma a bakinka. Kai ne zaka yunkura ka nemowa kanka yancinka ko kuma abinda zai amfaneka. Sabida haka dole musa kishi a zukatanmu don mu samowa lardinmu abinda yakamata daga gwamnatin Jiha har gwamnatin tarayya.
Babban burinmu shine mu sami Jiha (Hadejia State). Domin idan ka sami jiha, to duk wasu abubuwa na ci gaba zasu zo da sauki.


To amma kafin mu sami jihar, yakamata muci gaba da amfani da dimbin arzikin da Allah Ya bamu na masu ilimi, Sarakuna, maaikata,
manyan yan siyasa da yan kasuwa domin cimma duk wani cigaba da muke bukata.


Alhamdulillahi muna da Manyan maikata kamar Directors Permanent Secretaries, Ministoci, Soja, Yan Sanda da sauransu. Idan muka hada karfe da karfi muka sa kishi a alaamuranmu babu inda bazamu kaiba. Tarihi ya nuna akwai inda mutum daya mai kishi ya kawowa jamaarsa cigaba.
Saboda haka kara jaddadawa iyayenmu da yayyenmu da kuma musamman matasa manyan gobe gameda duk abinda zasuyi su sa kishi da hadin kai a gaba. Mu zama tsintsiya madaurinki daya muna haduwa da juna muna tattaunawa muna tsaida shawarwari kuma muna daukan dukkan matakin da yakamata don muga cewa mun cimma burinmu.
Matasa kune kunnenmu, kuma kune idanunmu. Saboda haka duk abinda yakamata Jamaa su sani, ku yakamata ku jaddadashi domin a dauki mataki. Har abada yin shiru baya warware matsala sai dai ya kawo rashin jituwa marar amfani Allah Yasa wannan taro ya zama dalilin samarda hadin kai da cigaba ga alummar Hadejia da Jigawa baki daya.

Thursday, August 8, 2013

HAWAN SALLAR AZUMI NA 8/8/2013 ALHAMIS.

Hadejia A yau. Daga Muhd Yawale Hadejia >


kamar yadda Aka sani Hawan sallar Azumi yana da tarihi mai tsawo a cikin Garin Hadejia, wannan sallar ma A bisa al'adar masarautar hadejia ranar sallah maimartaba sarki zai fito daga gida da safe, akafa tareda sauran mutanan fada domin zuwa filin idi. Dukda cewa za'ayi sallar ne a Bubban Masallacin Juma'a na cikin gari. Sakamakon ruwan sama da akayi kuma yayi ta'adi, Mai martaba sarki ya dage Hawan sallah domin Jajantawa ga wadanda ruwa yayi musu ta'adi.


Ga bayanin yanda Hawan sallah yake kasancewa da kuma ta Gurarenda ake bi. Bayan an idar sallar idi liman ya kammala huduba,sai hakimai da sauran mahaya dawaki su hau, sannan maimartaba shima zai hau dokinsa tare da Dandalmu, zai bi ta kasuwar kuda zuwa Titin yahai zuwa makera, sannan zai bi ta makwallah zuwa kofar Liman.


Idan maimartaba sarki yazo daidai kofar liman yakan tsaya domin karfar Jafi daga Hakimai. Wanda hakan ta samo Asali ne Tun Lokacinda Sarkin Hadejia Muhammadu Mai shahada ya dawo daga Yakin Madarumfa, ya tsaya a wannan Gurbin Inda su Jarumansa suke zuwa suke masa Jinjina. Amma a lokacin yana Hakimi ne kafin ya zama sarki. Bayan ya zama sarkin Hadejia sai ya maidata Al'ada wato duk sallar Azumi da Layya zai tsaya Hakimai suzo suyi masa jafi.


Daga nan kuma sai maimartaba sarki ya karasa rumfar manyan baki domin gabatarda jawabin sallah, bayan nan kuma sai maimarta ya karasa gida ya sauka tareda sauran hakimai.


Wannan shine Bayanin Hawan sallar Azumin wannan shekara a takaice da fatan Allah yasa ayi hawa lafiya a sauko lafiya. Allah yaja zamanin maimartaba sarki.

Saturday, August 3, 2013

TAKAICACCEN TARIHIN SHEIKH ISAH WAZIRI (WAZIRIN KANO)

HADEJIA A YAU!
Shekh Isah Muhammad Gidado wanda akafi sani da Mallam Isah Waziri.. An haifeshi a cikin garin Kano a shekarar 1925, kuma Da ne ga Wazirin kano Muhammadu Gidado. Yayi karatunsa na Allo a ciki da wajen kasar kano, sannan ya halarci makarantar koyon Aikin Shari'ah a cikin garin kano, daga bisani ya tafi Jami'ar Al-Azhar dake Egypt Inda ya karasa karatunsa. Kuma ya samu ilmin shari'ah da Koyarda Ilmin Addinin Musulunci.




Bayan ya gama karatunsa Sheikh Isah Waziri ya dawo kano inda ya fara aiki a Ma'aikatar Shari'ah ta kano, a matsayin Clerk daga bisani ya zama Registrar. kuma ya fara Tafsirin Alqu'ani mai tsarki a Garin Zakirai ta karamar hukumar Gezawa a wancan lokacin.




Bayan ya bar Aikin Gwamnati Mai martaba Sarkin kano Alh. Ado Bayero ya nadashi Limamin Masallacin Murtala dake kano, kuma anan yaci gaba da Tafsirin Alqur'ani mai girma. Shekh isah Waziri ya bada gudunmawa da dama a cik da wajen kano wajen Daukaka Addinin Musulunci, kuma yayi kokari wajen ganin anyi aiki da Shari'ar Musulunci a kasar kano ganin cewa Mafiya yawansu musulmi ne!




Sheikh Isah Waziri ya samu wannan sunan ne a lokacin yana Makarantar koyon aikin Shari'a Inda wani Malaminsu mai suna Sheikhul-Bashir yake fada masa ganin cewa Da ne ga Wazirin Kano Gidado. A maimakon yace masa Isah Muhammad Gidado, sai ya takaita sunan yake kiransa Isah Waziri.




Bayan da Limamin kano Kuliya ya tafi Aikin Ambasada a shekarar 1998, Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero ya nada Shekh Isah Waziri a Matsayin Bubban Limamin Kano. Sannan daga bisani An nadashi Wazirin Kano bayan da Dan-uwansa Wazirin Kano ya rasu.




A yau Juma'a 2/8/2013 azumi yana 24 Allah yayiwa Sheikh Isah Waziri rasuwa. Muna rokon Allah ya Gafarta masa ya kyauta Makwancinsa. Muma in tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani.