"" /> HADEJIA A YAU!: Sep 8, 2013

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, September 8, 2013

****TAURARINMU HADEJIAWA PART SIX(6)****

Free Web Proxy
Hadejia A yau.. Daga Muhammad Idris.
A ci gaba da kawo muku Tarihin wadanda Suka baiwa Kasar Hadejia Gudunmawa, yau Mun Tabo kadan daga Tarihin Marigayi Shatiman Hadejia Alh. Hassan Abbas.
****SHATIMAN HADEJIA ALHAJI HASAN ABBAS*****

Marigayi Shatiman Hadejia yana daya daga cikin dattijan arewa,manya a jihar kano da jigawa.Ya fara aiki tun daga Native Authority(NA) daga nan ya koma tarayya.Ya rike mukamin karamin ministan fetur a zamanin IBB. Shatiman Hadejia mutum ne mai kishin kasa da rikon addini. Shi ne sanadin aikin mutane da yawa a kaduna kuma har ya rasu akwai mutane da dama a zaune a gidansa.


Shatima ne ya fara gina katafaren gida domin saukar bakin kunya a Hadejia. Shi ya dauki dawainiyar
gyaran masallacin juma'a na lokaci mai tsawo.


Ya dauki nauyin sayen likkafani ga mamata har tsawon rayuwarsa. Arzik insa ya amfani 'yan uwa da sauran jama'a matuka domin akwai wadanda ya dauki nauyin ba su albashi har ya koma ga Allah subhanahu wa ta'ala.Muna addu'a Allah subhanahu wa ta'ala ya ji kansa ya albarkanci zuriyarsa.
Daga Muhammad Idris.