"" /> HADEJIA A YAU!: MARIGAYI ALHAJI ADAMU KWANO HADEJIA.....

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, February 21, 2016

MARIGAYI ALHAJI ADAMU KWANO HADEJIA.....


Daga Mallam Muhammad Rabakaya...

A madadin al'ummar Hadejia da gaba dayan masarautar Hadejia muna addu'a da alhinin Marigayi Alhaji Adamu Kwano (kwano baka karaya) Allah ka gafartawa wannan bawa naka, ka yafe masa kura kurensa da iyayenmu Allah ta'ala kasa aljannah madaukakiya ce makomarsu. Alhaji Adamu Kwano miliyoyin mutane sunyi tarayya da 'ya'yansa wajen gadon dukiyar da Allah ya mallaka masa Allah ka hada mu a Aljannah. zaka\ki so ka\kiji dalili -biyoni..................

Duk wadda ya baka Ilmi ko yayi ma hanyar samun Ilmi ya gama maka alfarma kuma kaci gado daga cikin gadonsa tare da 'ya'yansa. Marigayi Alhaji Adamu Kwano Hadejia Tun kafin a haifeni wannan bawan Allah yana da gida babba mai kallon gidanmu (Gida na a yanzu) Rahama chemist a yanzu ya gina yayi fasalin ajujuwa na Kasa da rufin kwano ya maidashi makarantar  Islamiyya (islamiyyar farko a garin Hadejia), ya tafi kano ya samo Marigayi Malam Aminu Yusuf da Malam Alhaji da Malam Sabo na Madabo da Malam Nasiru Ahli da Malam Rufa'i Kafin Hausa  kuma a matsayin Headmaster da malamai, kuma yabasu mahalli a wancan lokacin mun samu tabbaci daga matar daya daga cikinsu cewa daga gidansa ake dauko musu abinci. Aka saka yara maza da mata aka fara koyarda su darussan addini a tsarin zamani (formal education) mai Allo da Alli.


Daga nan abu ya kara fadada, yasa kudinsa ya cike wani rami mai tarihi wato RAMIN MALAM HUDU inda ya gina ajujuwa na siminti akan ramin da staffroom islamiyya ta koma can ya kara malamai, lokacin duk babu islamiyya sai ita Hudu islamiyya prim. sch. mai tsohon tarihi daga nan gwabnati ta shigo ta taimaka masa da karin Malamai da tsare tsare, Amma gini da gudanarwa nasane.
Bai tsaya nan ba tashinsa zuwa Asibiti inda yake aiki, ya sayi fili anan farin gida ta yanzu ya kara Gina wasu ajujuwan islamiyya ya bude makarantar Islamiyya Garko, duk a lokacin babu Islamiyya sai dai makarantun mu na zaure da na allo, daga nan ya kara fadada niyyarsa da burinsa na habaka ilmin addini a Hadejia ya raba Islamiyya Garko ya Kirkiri Karamar sakandare Islamiyya yasa mata sunan Headmaster na makarantarsa ta farko wato Malam Aminu Yusuf. Ya sake samo wani mutumin Sudan Sheik Ali Fu'ad a matsayin principal inda ya dauka mata malamai itace Aminu Yusuf Junior Islamiyya sec. sch. Hadejia. Wadda daga baya gwabnati ta bashi wani bangare a cikin Buhari primary school Hadejia ta tashi daga Garko ta koma can inda takoma hannun gwamnati kachokam bayan Allah ya masa rasuwa, wannan makaranta yanzu itace babbar sakandaren Islamiyya ta jeka ka dawo ta mata da maza a garin Hadejia.

Daga wancan lokacin zuwa yanzu mutum nawa aka raya? mutum nawa su kuma nawa suka raya da Ilmi? Kuma Bayansa tayi kyau, yana da 'ya'ya da jikoki da sukayi karatun Addini da Boko a fannoni da dama, da wadda yayi digirin farko tun 1977 har zuwa yau agida da kasar waje, sannan kafin yabar aiki yana daya daga cikin wadanda Gen. Olusegun Obasanjo ya baiwa lambar yabo yana shugaban Kasa a shekarar 1977.

Da fatan zamuyi koyi da irinsu a duk bangarorin rayuwa.
posted from Bloggeroid

3 comments:

  1. Allah ya gafarta masa.

    ReplyDelete
  2. Slm Mallam Ismail ko xan samu wasu rubututtuka akan sa , da Tarishin rayuwarsa ? Marigayi Alhaji Adamu kwano.

    ReplyDelete
  3. Muhammad Matta Hadejia ne Mmh.blogger.com

    ReplyDelete

RUBUTA RA'AYINKA!