content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, May 1, 2012

DAGA JIMEH SALEH B. B. C. HAUSA..

Image Hosted by ImageTitan.comJama'a da dama sun kauracewa birnin Maiduguri sakamakon rikicin Wakilin BBC Jimeh Saleh ya kai ziyara zuwa mahaifarsa ta Maiduguri a Arewacin Najeriya a karon farko cikin shekara guda - inda ya tarar da garin a cikin wani mawuyacin hali sakamakon munanan hare-haren da kungiyar Boko haram ke kaiwa.


A daidai lokacin da rana ke shirin faduwa; duhu kuma na kara yi, wani ladani na rangada kiran salla. Karar muryarsa na tashi daga saman daya daga cikin tsaffin masallatai na birnin.


Jama'ar musulmai sun gudanar da sallah Magrib - inda suke hada wa da Isha'i saboda akwai dokar hana zirga-zirga daga karfe bakwai zuwa shida na safe. Halin da ake ciki a yanzu na rashin tabbas da tsaro - ya sha banban da birnin Maiduguri da na taso a ciki. A 'yan watannin da suka wuce, kungiyar Boko Haram ta kaddamar da hare-hare a sassan Najeriya da dama - ciki harda na bama-bamai a Maiduguri.


Na isa Maiduguri bayan na dawo daga London a karon farko cikin shekara daya, birnin na nan cikin kamar yadda na barshi - sai dai talauci ya karu - haka kuma jama'ar garin masu hazaka da hadada. Babu masu motocin haya, masu bara, da shaguna wadanda ke kaiwa dare suna harkokinsu.


A yanzu jama'a ba sa iya cin abinci sau ukku a rana. Masu hada-hadar gidaje na cewa a yanzu harkar babu riba, wasunsu ma asara suke tafkawa. "Rufe shago karfe 7 na yamma daidai yake ace mutum ya yi aikin rabin rana," a cewar wani masanin tattalin arziki a jami'ar Maiduguri, wanda kamar yawancin mutane, ya nemi a saya sunansa.


"Muna cikin matukar tsoro," kamar yadda wani mazaunin birnin ya shaida min, "kuma kai kadai ne dan jaridar da zan iya magana da shi, saboda kaima na sanka, amma don Allah kar ka bayyana sunana."


Mutane da yawa sun kauracewa Maiduguri watanni da dama da suka gabata saboda kashe-kashen da ake yi, inda suka bar gidajensu a kargame. Wasu daga cikin attajiran birnin sun yi kaura da harkokin kasuwancinsu zuwa wasu biranen. An kafa dokar tabaci a Maiduguri bayan da aka kai harin ranar kirsimetin 2011 a Abuja da Jos wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 40.


Tun daga wancan lokaci, sojoji dauke da muggan makamai suka kafa shingayen bincike a sassa daban-daban na birnin, tare da tsaurara matakan tsaro a majami'u da ofisoshin 'yan sanda da sauran wuraren da Boko Haram ke kaiwa hari. An tura sojojin ne domin su kare mazauna birnin - sai dai baki ya zo daya wurin yin Alla-wadai da dokar hana zirga-zirgar da aka sanya da kuma yadda suka mamaye titunan birnin.


Sun zargi sojojin da cin zarafin jama'a da sauran laifuka masu alaka da cin zarafin bil'adama. Da zarar an kai hari, sai sojoji su shiga unguwanni suna farautar mutane a cikin gidaje tare da nakadawa maza duka. Sojojin dai sun musanta wannan na faruwa - amma abu ne mai wuyar musantawa saboda yadda jama'a ke nanata shi a kodayaushe.


Babban layi ne wurin da aka fi yin hada-hadar kasuwanci a birnin ta hanyar sayar da kayayyakin sawa, da na latironi da sauran kayan al'amura na yau da kullum. Kwarori da 'yan Chadi da sauran jama'a na fadi tashin futuka a wannan wuri domin amfana daga arzikin da ke akwai - sai dai a yanzu komai ya tsaya a wurin. Daga cikin 'yan wadanda da suka yi sa'a su ne masu sayar da kekuna da kuma kani-kawa: Kasuwar kekuna ta bude tun bayan da aka hana hawa babur a bara sakamakon hare-haren da ake kaiwa a kan baburan.


Sai dai duk da haka wasu da dama na fatan abubuwa za su daidaita a birnin Maiduguri, mafi yawa kuma sun koma ga Allah domin yin addu'a ko an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali - wanda a baya shi ne taken mahaifata ta Maiduguri.

RA'AYI BA GABA BANE

Dandalin Muazu Hadejia MENENE RA'AYINKA/KI??? A tunanina da dogon naxarina inaga raba nigeria biyu shine xaibawa nan arewa samun qaddamar dama komenene... Idan shari'ar musuluncin cema... ABIN LURA: Meyasa duk inda ake tashin hankali a arewane? Kuma musamman ma wadanda suka nunawa GUDLUCK QIYAYYA a fili a shekarar xabe ta 2011... Meyasa akai birin da tattaunar da akace wai anayi da 'yan boko haram? Meyasa GEJ yaqi daukar shawarar gwamnan KADUNA? Shin gwamnatin JAR HULA ta kano tana ganin cin kashin da akewa talakawanta wadanda sukasha rana awajen xabenta? Shin yanxu anacigaba da gudanar da komai lfy a BUK? Idan a'a to yaushene komai xaidawo nrml a BUK? Gwara araba kowa yasan gidan ubansa gaskia... Karkucemin idan anraba xamusha wuya.. Yanxunma ita mukesha kuma da sunan gwamnatin KAFIRCI.. Ga NIGER nan... Nan gaba kadan xata bawa duniya mamaki wajen cigaban xamani... Ina manyan Arewan da ake cewa akwaisu? Ko suma tsoron 'yan boko haram dinne yasa sukai shiru??? Mudai gwara araba! Suje suci MAI muxo muci wuyarmu daga karshe mayi hankali! By Inuwa A liman.