"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Monday, June 11, 2012

TARIHIN RAYUWAR MARIGAYI UMARU MUSA 'YAR-ADUA


Umaru Musa Yar'Adua
Shi dai marigayi Malam Umaru Babangida
Musa 'Yar'Adua, an haifeshi ne a ranar 16
ga watan Augustan 1951 a birnin Katsina
dake arewacin Najeriya. Mahaifinsa shine
tsohon ministan birnin Lagos na farko a
jamhuriya ta farko, kuma kafin ya rasu
shine Matawallen Katsina, sarautar da
kuma shi ma marigayi Umaru Musa
'Yar'Adua ya gada.

Marigayin ya fara makarantar Firamare ta
Rafukka a 1958 kafin a mayar da shi
makarantar Firamare ta kwana dake
Dutsen Ma a 1962. Ya kuma halarci
kwalejin gwamnati dake Keffi daga 1965
zuwa 1969. Sai kwalejin Barewa 1971,
inda ya samu takardar shedar karatu ta
HSC.
Tsohon shugaba 'Yar'Adua ya halarci
Jami'ar Ahmadu Bello dake Zariya daga
1972 zuwa 1978 inda ya samu takardar
shedar digiri akan kimiyyar haɗa sinadirai
ko Chemistry da Malanta, kafin ya koma
domin samun babban digiri duk dai akan
kimiyyar ta Chemistry.

Marigayin yayi bautar
ƙasa a jihar Lagos inda ya koyar a wata
makaranta da ake kira Holy Trinity daga
1975-1976.
Bayan da ya kammala aikin yiwa ƙasa
hidima ya fara aikin Malanta gadan-gadan
a kwalejin share fagen shiga jami'a da ake
kira CAST dake Zariya a tsakanin 1976
zuwa 1979.

A shekarar 1983 marigayi
Malam Umaru Musa 'Yar'adua ya bar aikin
Malanta ya fara aiki da Gonar Sambo Farms
a Funtua dake jihar Katsina inda ya zama
GM daga 1983-1989.
Daga shekarar 1984 bayan da Sojojin
sukayi juyin mulki malam Umaru Musa
'Yar'adua an kira shi domin zama wakili a
hukumar gudanarwar kanfanoni da
hukumomin gwamnati da dama da suka
haɗa da hukumar samar da kayan Noma
da kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar
katsina, Bankin Habib da Hamada Carpets
da Madara Limited da kuma kanfanin buga
Jaridu da Mujalla ta The Nation wanda ke
kaduna kuma wansa Marigayi Janar Shehu
Musa 'Yar'Adua ya mallaka.


A lokacin da marigayi Malam Umaru Musa
'Yar'Adua ya shiga siyasa ya yi hannun riga
da mahaifinsa wanda a wancan lokaci yake
mataimakin shugaban Jam'iyar NPN, inda
shi kuma ya zama wakili a jam'iyar PRP ta
Malam Aminu Kano mai adawa da NPN. A
lokacin da Janar Babangida ya kaɗa gangar
siyasa ya zama sakataren jam'iyar SDP a
jihar ta Katsina kuma ɗan takararta na
gwamna, amma kuma ɗan takarar
jami'iyar NRC na wancan lokaci Malam
Saidu Barda ya kada shi.

To sai dai a 1999
Malam Umaru Musa 'Yar'Adua ya tsaya
takakarar muƙamin gwamnan jihar ta
Katsina kuma ya samu nasara a ƙarƙashin
jam'iyar PDP, haka kuma ya sake nasara a
zaɓen 2003.
A shekarar 2007 Umaru Musa 'Yar'Adua ya
zama ɗan takakar muƙamin shugaban
ƙasa na Jam'iyar PDP bayan ya samu
taimakon tsohon shugaban ƙasa Cif
Olusegun Obasanjo ya zama shugaban
ƙasa a ranar 29 ga watan Mayun 2007.
To sai dai rashin lafiya da tsohon shugaban
yayi fama da ita ta sanya bai samu sukunin
gudanar da harkokin mulki kamar yadda
yayi fata ba musanman ƙudirorinsa guda
bakwai daya tsara na ciyar da ƙasar gaba
kafin nan da ƙarni ta 2020.


Marigayi Malam Umaru Musa 'Yar'Adua ya
rasu a ranar 5 ga watan Mayun shekara ta
2010 da muke ciki a fadar gwamnati dake
Abuja watanni biyu bayan komowarsa gida
daga Saudiya inda yake jinya.
Ya kuma rasu ya bar mahaifiyarsa da
'yan'uwa da matar aure guda Hajiya Turai
tare da 'ya'ya bakwai da ya haifa da ita da
suka haɗa da mata biyar da maza biyu.
Haka kuma yana da wasu 'ya'ya biyu maza
da matarsa ta biyu Hajiya Hauwa Umar
Radda.

Thursday, June 7, 2012

ZUWAN TURAWA KASAR HADEJIA KASHI NA (2)


HADEJIA A YAU! A kashi na farko Na baku Labarin yadda Turawan mulkin mallaka suka yiwa Hadejia Leken Asiri, wadda hakan ta basu dama suka kama garin.

Yanzu zamu dora! Koda yake Sarkin Hadejia Muhammadu ya samu labarin Turawa sun ci Kano da Katagum duk sun koma karkashin mulkinsu yace da yabi Kafiri Gara yayi shahada,Turawa basu fasa ba shima bai fasa ba.

Ranar Talata 1906 Turawa suka shigo Hadejia Gadan gadan akayi ta gwabza fada, dukda dawakan Hadejia basu taba jin kukan Igwa ba da sunji wannan kukan sai su turje haka nan akayi ta fama da su. jama'ar Hadejia manya da yara kowa yayi shirin yaki haka nan akayi yaki har Zuwa Azahar,  kuma Turawa suna kara shigowa Hadejia, saboda makaman su ba irin namu bane. An kashe manyan fadawan Hadejia da hakimai:

kamar yadda na fada a baya Sarkin Hadejia Muhammadu saida aka ce masa Kada Hadejia ta kare saboda shi Tukuna ya rusuna har Turawa suka cim masa. Allahu akbar!

koda Hadejiawa suka samu labari an kashe sarki sai kowa ya Rusuna,  Turawa suka shigo Hadejia suka Fara shirin tafiyar da mulki irin nasu. Hadejiawa sukayi Jana'izar wadanda suka mutu, wadanda kuma sukaji rauni aka kaisu Gidajensu. Turawa suka Nada Sarkin Hadejia Haru mai karamba 1906. 

To akwai sarkin yaki cilin Yana daga cikin wadanda suka samu raunuka a yakin kuma shi Captai phillips ya sanshi dama can. to kullum sai yaje Gidan sarkin yaki Yana Masa Izgilanci yana ce masa ina yakin? Ashe Sarkin yaki yana jin ciwon hakan. Wata rana sai yacewa matarsa Idan zata Kawo masa Abinci tasa wuka a cikin Tuwon.

haka kuwa tayi. saida captain phillips yazo yana masa Izgili Sai yasa hannu kamar mai cin tuwo sai ya dauko wuka ya Burmawa captain phillips a tumbinsa ya kasheshi. Kabarinsa yana can a Gabas Da Bariki Hanyar Tandanu. Shi ake cewa Kabarin mai tumbi. Wadanda suka rasa rayukansu a yakin suna da dama Amma ga kadan daga Sunayensu. Muhammadu Sarkin Hadejia, Madacima shi suka fara kashewa, Galadima, Ma'aji salihu, Furya, Barwa da Tarno, Bori na Salihu, Kaura Amadu, Mabudi zakar, Jarma warkaci, Sabo jikan Tete, Dandalma, Abdulwahabu sarkin Baka, Sarkin Arewa, Alkali, Farau farau, Sarkin Dawaki Dan gazau, Da dai Sauransu! Allah yaji kansu da Rahma.