"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Thursday, June 21, 2012

SAKO ZUWA GA MASU AMFANI DA FACEBOOK


Malam Yusuf Audi, ya
rubuta cewa kamar haka...
Shafukan INTERNET da
Wayar hannu ta
GSM...... Bincike ya nuna
cewa shafin internet na
FACEBOOK da wayar hannu
ta GSM suna
daga cikin ababen dake
kara rura wutar
fadan addini a Nigeria.
Hakan yana faruwa
sakamakon irin yadda
mutane ke amfani da su
wajen isar da
sako atsakanin su.
Mutanen mu suna da son
bayar da labari,
ingantacce ko mara
inganci don neman
addu'ar 'yan uwansu ko
don nuna bajintar
su ko kuma don wata
manufa ta su ta
daban. Wannan yasa
dayawa sukan fidi abin da
ba
su da tabbas akan shi, ko
kuma suyi kari
cikin labarin na su. Ya kai
dan uwana me son bayar
da labari!
Kaji tsoron Allah, kada
kafadi, kada
karubuta sai abin da kaji
ko kagani ko
kuma kake da tabbas akan
shi. kasani za ka amsa
tamyar Allah akan abin
da kake fadi ko kuma kake
rubutawa
duniya(facebook), wacce
amsa katanada?
Ba wani abin birgewa
bane afara jin
labarin dake tayar da
hankali agurinka. Na ji
ance sun ce, wannan ba
dalili bane.
Addinin muslunci ya hore
mu da yin
magana ba tare da ILIMI
ba. Mu kiyaye ko Allah
(S.W.A) ya kiyaye mu. Ya
Allah! Kakiyaye mu,
kabamu zaman
lafia, amin.
To Jama'a sai mu kula da
fadar jita jita, domin karya
haramun ce. Allah ya kare
mu ameeeeeeeeen

Wednesday, June 20, 2012

MAI MARTABA SARKIN HADEJIA ALH.ADAMU A.MAJE

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU! A Ranar Asabat 3/january/1999 Mai martaba Sarkin Hadejia Alh.Abubakar Maje Haruna ya Nada Alh.Adamu Abubakar A matsayin IYAN Hadejia.

kuma shine Iyan Hadejia Na farko a tarihin Hadejia!
kuma Ranar Asabat 20/september/2002 An nada Alh. Adamu Abubakar A matsayin Sakin Hadejia na Goma sha shida (16) karkashin jagorancin Galadiman Hadejia Alh.Habib Adamu.

kuma an nadashi a cikin fadar Hadejia. kwanaki Uku bayan Mutuwar Sarkin Hadejia Alhaji Abubakar Maje. yayi Hawan sallah na farko a Matsayinsa na Sarkin Hadejia wato:

Hawan sallar Azumi Dec. 2002. wato kafin a Bada Sanda. Ranar Asabat 29/March/2003 Akayi bikin bada sanda A filin wasa na Hadejia Karkashin Jagorancin Gwamnan Jigawa Alh.Ibrahim Saminu.

Ranar 14/september/2012 Zai shekara Goma(10) yana sarautar Hadejia.

zamu rinka kawo muku Irin Gudunmawa da ya bayar ta ci Gaban Wannan Masarauta. Daga yanzu har zuwa 14/september Na wannan Shekarar wato 2012. Hadejia A yau.