"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, June 27, 2012

TARIHIN SARAUTAR SARKIN HADEJIA NA (16)

Image Hosted by ImageTitan.com


Ranar Asabat 3-january-1999, Mai martaba Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya Nada Alh. Adamu Abubakar A matsayin IYAN HADEJIA, NA FARKO. Kuma Ranar Laraba 11- september-2002, Allah ya yiwa Mai martaba Sarkin Hadejia Rasuwa. Alh. Abubakar maje Haruna.

TO A SAKAMAKON AMINCEWA DA GWAMNATI TAYI DA ZABEN 'YAN MAJALISSAR SARKI WATO (KING MAKER'S) Suka zabi Iyan Hadejia Alh. Adamu Abubakar maje a matsayin sarkin Hadejia, Na Goma sha shida (16). kuma an nada shi Ranar Asabat 14-september-2002. Bisa Al'ada ba'a kwana uku ba tare da an nada Sarki ba.

KUMA HAWANSA NA FARKO A MATSAYINSA NA SARKIN HADEJIA SHINE Hawan sallar Azumi wato A watan Disamba 2002. Sannan sallar Layya February 2002 Bai Hau ba saboda yaje Saudiyya.

29-March-2003.
A YAU ASABAT 29-March-2003 ANYI BIKIN BADA SANDA! An baiwa sarkin Hadejia Sanda a Karkashin shugabancin Gwamnan Jigawa ALH. IBRAHIM SAMINU TURAKI! A STADIUM TA HADEJIA.

Kuma bayan an Bashi Sandar jagorancin Kasar Hadejia A karkashin Tutar Shehu Usman Dan fodio, Mai martaba sarki yayi Hawa Guda Uku Wadanda suka Kayatar da
jama'ar Hadejia.

1, BIKIN GASAR ALQUR'ANI A SECONDARY FANTAI
2,TARON DA AKAYI A MAKARANTAR KOFAR AREWA
3,SAI HAWAN GANDU WANDA SHIMA YANA DA TARIHI A MASARAUTAR HADEJIA.

 Hakiman da ya fara Nadawa sune:
 1, DAN GALADIMA Alh.babbaji Adamu Hakimin waje 
2, SARKIN DAWAKI Alh. Umar IbrahimHakimin kiri kasamma.
3, KATUKAN HADEJIA NA (2) BIYU Hakimin Turabu.

 A gaba zan kawo muku Labarin Fitar sarkin Hadejia Rangadi da yayi da kuma Hakiman da a Nada.

Tuesday, June 26, 2012

RABE DA MUTANEN BORNO


HADEJIA A YAU!
Baramusa wani kauye ne a karamar hukumar Birniwa! Naje ziyara kauyen kuma ganin cewa duk barebari ne a garin, sai na samu damar in tambayi tarihin Rabe dan Fataralle. Na samu wani dattijo mai shekara 76, sai na tambayeshi tarihin Rabe. Kafin ya bani amsa saida ya tsinewa Rabe.
Yace wani mutumin sudan ne wanda ya Addabi bare bari tun daga kukawa Har zuwa Bedde. Sannan yace Rabe ne dalilin zuwansu nan kuma yace duk Babarbare ko bamangenda naganshi a Kasar Hadejia ko wani Guri, to lokacin Rabe ne suka Gudo nan. Yace kamar Kacallari,Kaigamari,kuka Ingiwa,Birniwa.kirikasamma,Jibori, da sauransu duk Gudun Rabe sukayi. A lokacinda Rabe yaje kukawa ya kashe duk mutanen Garin wasu da suka samu labari sai sukayi gudun hijira kasar Hadejia. Wasu kuma suka shigo cikin Hadejia kamar Gagulmari,Kakaburi,zonagalari,kilabakori da sauransu. Yace da can suna da zanen barebari amma yanzu sun canza sai suke zanen a kan fuskarsu wato uku uku. Sauran Labarin sai a Gaba.