"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, July 6, 2012

THE ESTABLISHMENT OF SOME OF THE OLD SETTLEMENTS IN HADEJIA EMIRATE


HADEJIA A YAU!
We are severely constrained in the producing a coherent, meaningful and definite pattern of the process of the evolution of Hadejia emirate due to the limitation by our main source-oral tradition. Most of the traditions collected hardly touch on the process of the evolution of Kasar Hadejia. But in spite of this difficulty, we intend to take a second look at the source through a new-interpretation in the hope of coming out with a better understanding of the process of the evolution of Hadejia emirate. Towards this end, we shall attempt to discuss the process of the evolution of certain Old settlement in the emirate, with a view to paving way towards grasping the process of the evolution of Kasar Hadejia as whole.

Prior to the jihadist conquest at the beginning of the 19th century, the territory now known as Hadejia emirate consisted of several separate and distinct Kingdoms whose rulers received titles from and owed allegiance to the Habe Galadima of Borno.

The former Habe Kingdoms included Auyo,Garin Gabas(Biram),Hadejia,Kazura,Gaturwa,Marma,Dawa and Fagi. The process of the evolution of these Kingdoms of seems to be obscure except perhaps for the Kingdoms of Hadejia,Auyo and Garin Gabas.

At the time of the foundation of Hadejia,a number of small settlements were said to have existed in the territory that came to be known as Hadejia emirate. For example,on the North-eastern side of Hadejia town, there was Madagwaigwai, whose present site is near Rubban Dakata a village about 10kilometres east of Hadejia Kiri kasamma road. While on the eastern side of the town was Maskangayu (kulunfardu), a village said to have been established by Damagarawa immigrants whose ancestors now live in Hadejia (ILALLAH).

The old site of Kulunfardu was located near Tandanu, just by the valley of River Hadejia, about 15kilometres from TURABU.

There was a tradition in Turabu which said that, at the side of kulunfardu, there was a large Tamarind (Tsamiyar linzamai) whose branches were said to have bent due to the weight of the Luggage of soldiers of Mai Ali of Borno when they camped there on their way to attack Kano during the reign of Sarkin Kano Muhammadu Kambari Dan shariff(1731-1734) By the western side of Hade's camp was KADIME (still located to the site) which was about 9kilometre from Hadejia. By the Northern side of Hadejia was Majeri a few kilometre from Mallam madori, and by the southern side were Auyakayi(Tunawa), Unik(Arki), Majawa and Auyo.

These settlement were clearly established in the surrounding areas much earlier than Hadejia town.
End of page One.

A short History of Hadejia 1800-1906. By Musa Usman Mustapha.
Ana saida shi a k.liman.

Thursday, July 5, 2012

SARKIN HADEJIA BUHARI DA WAZIRIN SOKOTO A KATAGUM KASHI NA (2)

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU!

A kashi na farko kunji yanda Buhari suka kare da Wazirin sokoto da Mutanen Katagum: da kuma komawar sarki Buhari shabawa wato iyakar Hadejia da Gumel da kuma Damagaram.

YAKIN TAKOKO:- Bayan an Nada Ahmadu a matsayin Sarkin Hadejia, sauran Magoya bayan Buhari sai suma suka bar Hadejia suka koma Shafowa inda Buhari yake suka zauna tare. Sarkin Hadejia Buhari anan ya zauna tsakanin Takoko da Shafowa a Arewacin Hadejia da mutanensa kuma yake tafiyar da wannan yankin. Kuma iyakar Hadejia ce da Damagaram da Machina ta Arewa maso Gabas wato yankin Niger da kuma Borno. Kuma Buhari ya bada Gudun mawa sosai a wannan Yankin wajen Maidasu Musulmi. Inda yayi ta jihadinsa a yankin, kuma a wannan zama da yayi a Shafowa Buhari ya samu kyakkyawar dangantaka da Sarkin Machina da kuma Shehun Borno Umar wanda ya mulki Borno a wannan shekara (1835-1880) wannan dangantaka ta kara baiwa Buhari karfin gwiwa.


A shekarar 1851, Sarkin Musulmi Alu Bubba ya yanke shawarar daukan matakin Karshe akan Buhari, saboda yana tunanin Shehun Borno zaiyi amfani da Buhari ya rusa Daular Sokoto saboda ya zame musu Barazana a Arewa Maso Gabas. A wannan lokacin kuma DanGaladiman Sokoto ya hada Mayaka daga Hadejia,Kano,Katagum,Misau da Jama'are zuwa shafowa.

A wannan lokacin kuma Buhari ya fita kudu da shafowa shi da Sarkin Machina yana garin Takoko shida Jarumansa. A lokacinda Dangaladiman sokoto suka fito su yaki Buhari sai ya zabi Sarkin Jama'are Samboli ya jagoranci yakin, saboda shi ya fisu sanin Yankin. A ranar da zasu yaki buhari kuma a ranar Buhari ya shirya mamaye Garuruwanda suke kudu da Hadejia, sai aka hadu a Garin Takoko. Yayin da aka hadu aka gwabza fada Buhari yaci Galaba a kansu duk suka gudu, Sarkin Hadejia Ahmadu yayi kokarin ya Gudu Kasar Kano amma sai Barde Risku ya bishi ya Kashe shi.

Bayan Yakin Takoko yazo karshe kuma an kashe Sarkin Hadejia Ahmadu Amma ba'a son ran Buhari ba kuma aka masa Sallah aka kaishi Hadejia aka binne shi, sannan sai Buhari ya koma Hadejia yaci gaba da Mulki. Sakamakon wannan yakin, dangantaka ta sake baci tsakanin Hadejia da Sokoto, kuma Sarkin Musulmi yaki yarda da ya nada Buhari Sarkin Hadejia. Sai ya nada Tukur Na yayari, kanin Sarki Ahmadu kuma yace ya zauna a Mashama a Kasar Katagum a Matsayin sarkin Hadejia ya Gaji wansa Ahmadu. Amma Tukur bai yarda ya zama Sarkin Hadejia ba saboda yana tsoron Buhari, sai yaga bazai iya yin haka ba. Kuma saboda Gudun kar Buhari ya kasheshi sai Tukur ya Gudu daga Mashema yayi kaura zuwa Kano Lokacin Sarkin Kano Usman Na1(1846-1855) Sai aka Turashi ya Mulki Yayari a Kasar Birnin Kudu. (Yayarin Tukur) Tukur ya zauna acan Har zuwa lokacinda ya Mutu 1909. Buhari kuma yaci gaba da mulkin Hadejia yana kai hare hare a matsayin Jihadi Har saida yakai Gabasawa,Sankara,Ringim da Kuka kwance A Arewa maso yamma. A Kudu saida ya mamaye Kununu,Takalafiya, Kafin baka, Doma, Ruba, Itas da Kwanda. A Gabas kuwa saida ya Mamaye Babuwari, Kazura, Dawah, Gatare da Margadu. Saida Sarki Buhari ya fadada kasar Hadejia tafi Ko ina fadin Kasa a karni na19.

GAMON KAFUR:-