"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, September 29, 2012

A SHORT HISTORY OF HADEJIA BY MUSA USMAN MUSTAPHA.

HADEJIA A YAU!According to S.J. Hogben,
Hadejia town was founded in The 15th
Century. The assertion draws some authority
from the manuscript of the Kano chronicles,
where it was stated that, during the reign of
Yakubu Abdullahi Barjo who ruled Kano
from 1452AD to 1463AD. The King of
Machina Algalfati went to Kano with his
three Brothers. Sarkin Kano Yakubu gave
Sarkin Machina Algalfati the right to rule
Gaya and so he became the ruler of the
town. While one of Algalfati's brother went
to Rano where Sarkin Rano appointed him
the ruler of Dal. The second Brother
proceeded to Zazzau, where Sarkin Zazzau
appointed him the ruler of Gayan, And the
third Brother went to Garun Gabas, where
Sarkin Gabas appointed him the Ruler of
HADEJIA.

And established the dynasty which
ruled the town until the outbreak of the
19th century Jihad.
On the basis of this assertion, the town was
said to have been established sometime in
the 15th century, but the tradition which the
assertion was based on, contained certain
short comings which made its authenticity
doubtful. In the first place throughout the
period of our field work, not a single person
mentioned this tradition. And secondly
neither the tradition of Hadejia nor that of
the places (Kano, Gaya, Rano, Dal, Zazzau and
Gayan) mentioned the tradition, connect
their origins with each other.


And finally the fact that one of Algalfati's
brothers was appointed the ruler of the
town in the 15th century did not in any way
indicate that the town was established at
the time. In fact, if any thing, the tradition
only showed that the town was established
earlier than this development because a
ruler can only be appointed to an existing
town not the other way round.


(MUSA
USMAN MUSTAPHA)HADEJIA A YAU!

Friday, September 28, 2012

MUTUWAR SARKIN HADEJIA BUHARI

HADEJIA A YAU!
Bayan Sarkin Hadejia Buhari ya Gama
yake yake kamar yakin Takoko, gamon
kafur da sauransu! Sai ya yanke
shawarar ya fadada Kasar Hadejia daga
Gabas. Kuma a lokacin babu wani Dansa
da ya taso wanda zai bashi wata
sarauta bubba. Dan haka ya Nada
kaninsa Sarkiyo a matsayin Chiroman
Hadejia a shekarar 1863. Da nufin ya
zama Magajinsa, saboda Dansa Umaru
shekarunsa Goma sha Takwas (18).
Buhari yayi Tunanin ya Masa sarauta mai
Girma a Kasar Hadejia, dan haka yayi
kokarin ya masa sarautar Sarkin Auyo,
bayanda ya Kashe Nalara sarkin Auyo
ba'a nada kowa ba! Dan haka yaso ya
nada Umaru a matsayin Sarkin Auyo.
Wato ya kasance ya gajeshi bayan ya
Mutu.
Da wannan kudiri da yake ransa, Buhari
yayi kokarin ya cinye Gogaram (Bedde)
da Yaki don ya Nada kaninsa Chiroma
Sarkiyo a matsayin Sarkin garin. Kuma
dukda yayi haka zuciyarsa daya, wasu
daga cikin 'yan-uwansa sai suka yi
kokarin su baza masa abinda ya tsara!
Dan haka wani daga ciki 'yan-uwan
Buhari sai ya fara yada jita-jita a
tsakanin fadawan Buhari cewa yana so
ne ya kaisu a kashe su don ya cimma
wata manufarsa, su kuma fadawa sai
suka ga Dangantakarsa da Buhari bazai
fadi karya ba sai suka yarda da
maganarsa.
Dan haka fadawa sai suka fara shawara
a junansu ba tare da Sarki Buhari ko
wani ya sani ba, don su yiwa Buhari
tawaye a gun yakin, kuma duk suka
amince da hakan. Bayan kwanaki sai
Buhari ya sanar da fadawa cewa zasuje
suci Gogaram da yaki, amma bai san an
warware masa shirinsa ba. Aka saka
rana Buhari ya jagoranci mayakan
Hadejia don su ci Gogaram da yaki,
sarkin Hadejia Buhari ya shiga Gogaram
ta kofar Garin yamma amma mayakan
Buhari kamar su Sarkin Arewa Tatagana
da Sarkin yaki Jaji da sauran fadawa sai
suka tsaya suka ki su bi Buhari, ko da
ganin Haka sai Buhari ya shiga garin
suka fara dauki ba dadi da Mayakan
Sarkin Gogaram DAN BABUJE. Har suka
sokeshi da Mashi, kuma sai suka fice
daga Garin suka koma Bedde ta yanzu.
Koda mayakan Hadejia suka ga an
raunata Buhari sai suka bisu da yaki,
bayan sun dawo sai suka taho da
Buhari zuwa Hadejia, inda suka yi Gadon
Kara suka Dora shi. Akan hanyarsu ta
dawowa Hadejia Buhari ya musu jawabi
kuma suka fahimci cewa Munafurci ne
akayi tsakaninsu da Buhari. Kuma yace
musu lalle In ya mutu su kaishi Hadejia
su binne shi, kuma Allah ya dauki ransa
a Madaci kusa da Hadejia. Bayan fadawa
sun fahimci 'yan-uwan Buhari ne suka
munafurceshi, sai suka yanke shawarar
cewa dukda Kankantar Dansa Umaru shi
zasu Nada A matsayin Sarkin Hadejia.
Kuma hakan akayi karkashin jagorancin
Tatagana da Jaji. In kazo kayi Gaisuwar
Mutuwar Buhari sai ka Juya kayi
Mubaya'a a gun Sabon Sarki wato
Umaru Dan Buhari. Hadejia A yau.