"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, October 26, 2012

BARKA DA SALLAH. (Layya)

Free Web Proxy HADEJIA A YAU! HAWA LAYYA
Yin layya sunnah ce mai karfi da ta kasance
wajibi ga dukkan musulmi. Maza da mata
kowacce shekara. Ta kan fadi a kan mutum in
ba shi da sarari. To ko maras sarari da ya
sauka a wannan shekara ko bai taba hawa
ba . Ya shiga cikin daya daga raguna 2 da
Annabi(s) ya yanka. Ya ce daya nasa ne daya
na masu karamin karfi cikin al'ummarsa har
zuwa tashin kiyama.
Ya tabbata daga ma'abuta ilmi cewa in kana
da riguna 2 ka sayar guda ka yi layya. Annabi
(s) ya ce duk wanda ya ke da dama kuma ya
ki yin layya to kada ya kuskura ya zo wuraren
sallar Idin mu. Annabi(s) ya ce za a ba mai
layya lada kan kowanne gashi guda na adadin
gashin da ke jikin dabbar da ya yanka.

Monday, October 22, 2012

KWANAKIN HAJJI DA GURARE GOMA MASU ALBARKA. DAGA (M. AMINU DAURAWA)

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music HADEJIA A YAU!

Na daya ranar takwas ga watan hajji, sunanta yaumuttarwiyya,
shine alhazai suke zuwa mina su wuni su kwana,
Na biyu ranar tara ga wata itace ranar arfa, itace alhazai suke wuni a
filin arfa zuwa faduwar rana, daganan su tafi Muzdalifa su kwana
Na uku ranar goma ga wata, itace alhazai suke gabatar da aiyuka
guda biyar a cikinta, jifa, yanka, aski, dawafi, saayi,
Na hudu ranar sha daya , da sha biyu, da sha uku, sune ranakun
kwanan mina da jifa, Abubuwa goma masu daraja a Macca
wadanda suke da alaka da aikin hajji, wadanda ake aiwatar da aikin
hajji, daura da su sune, na daya, Ka'aba ana kewaya ta sau bakwai,
na biyu, alhiji (wanda ake cewa hijri isma'ila) ana shiga ciki ayi
salla,daidai yake da yin sallah a cikin Ka'abah, na uku, makamu
ibrahim, wanda ake sallah Raka'a biyu a bayansa bayan gama
dawafi, na hudu, Alhajrul'aswad, (dutsen aljannah) ana sunbatarsa
(kiss) a shefeshi, ayi sujjada akansa, ko anunashi daga nesa ayi
kabbara, na biyar ruwan zamzam, ana sha a shafa a fuska, a zuba
ajiki, ayi addu'a, aroki Allah bukarar duniya da lahira hadisi ya
tabbata, akan haka, na shida Dutsen safa da marwa, wanda ake
zirga-zirga tsakanin su sau bakwai a fara daga sama a kare a marwa,
na takwas, mina wajen kwana da ranakun jifa, na tara arfa da
muzdalifa, a wuni a arfa a kwana a muzdalifa, na goma wajen jifa
guda uku, inda ake jefa tsakuwa guda saba'in, Allah ta'ala yace
wanda ya girmama alamomin addinin Allah, yana daga cikin tsoran
Allah na zuci, wanda duk yayi sallah a masallacin macca yana da
lada dubu dari, wanda ladan ya shafi dukkan fadin iyakokin harami,
tun daga ka'abah, Manzon Allah saw yace :Duk wanda yayi hajji,
baiyi kwarkwasaba (maganar batsa da mata) baiyi fasikanciba, zai
dawo kamar ranarda mahaifiyarsa ta haifeshi, kuma yace, Hajji
kubutacce(shine wanda akayishi akan sunnah da iklasi da ilmi) bashi
da sakamako sai aljannah, ku tayamu da addu'a mu sami wannan
garabasar, Allah ya karbi ibadarmu yasa mu dace da sunnah da
iklasi na gode