"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, November 4, 2012

WAKAR TARIHIN YAKIN HADEJIA DAGA LIMAN MUHAMMADU (Fassara daga Alh. Ibrahim katala).

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau. 1, Allahu sarki shi kadai yake wahidun, sammai da kassai jalla bashi da kishiya. 2, Shi ba fari shi ba baki ba ubangiji ba ja ba ba alkashi bashi ga rawaya. 3, Ba sake sake ba ba kamar yarani ba shudi da kore jalla bashi da mai kama. 4, Zatinsa baya tattara bai rarraba da kawai da motsi bayayi ko sau daya. 5, Sarkinda ba na biyunsa ba na uku nasa ka dadan basira zanyi waken shahidu. 6, Ranar talata munga tashin duniya Rannan Muhammadu yai shahada zahira. 7, Shi yai jawabi ya fada shi bai gudu kuma bashi mai kamu a darul duniya. 8, Raggo ake kora a bishi a cim masa amma sadauki bai gudu sai faduwa. 9, Sarki Muhammadu yai jawabi ya cika shi bashi mai kamu a jashi ya tunkiya. 10, Dan melle sarkin yaki shima ya fada in dai da rai sarkinmu baya kamuwa. 11, Ma'ajin Hadejia saleh shima ya fada mun dau shahada zahira bahakikiya. 12, Manya da yara duk shirin yaki suke kowa yana wanka yana yin alwalah. 13, Kowa yana yin sallama a gida nasa sunsa gabansu a lahira ba dawaya. 14, Jama'ar Hadejiawa fa duk sun hallara kowa yana cewa fa mun zama shahidai. 15, Sarki Muhammadu mai shahadar zahiri ba badili ko dai cikin tawaga tasa. 16, Shi bai kamar tsoro ba baya razana kan ya ije ma babu sauran hanzari. 17, Ajali idan yayi babu kwana duniya kai dai zamo kullum shiri duka safiya. 18, Shi bai kamar tsoro a baya razana baya gudu dan Garba sarkin jarumai. 19, Mutuwa tafarki wanda kowa zayabi ai kulli nafsin dukka rai zai dandana. 20, Aka daura sirdi nai ya hau bisa ya tsaya yace mu dau himmar shahada zahira. 21, Sarki Muhammadu baya tsoro ko kadan Allah ma'aiki su take tsoro kadai. 22, Hauninsa linzamin mayani ya rike damansa tasbihi salatin annabi. 23, Dan mai karatu tudun kasa ba dawaya dan garba jikan sambo sarkin adalai. 24, Duk mai shahada auwalinsa madacima suka barace da fari ya mutu shahidi. 25, Farkon hawa yaki galadima sai haru ranar talata sun ka sauka a barzahu. 26, Alkali sarkin yaki kaura amada sarkin arewa da sunkaje can sun tsaya. 27, Suka jeru sunka tsaya a nan kofar gabas kafin suje har mai ruwa ya taddasu. 28, Kasan igwa dokinmu shi bai santa ba duka dokuna na faduwa ba lissafa. 29, Igwa tana tashi madafa na zuba yau sai ta Allah babu sauran shawara. 30, Jaruman Muhammadu basu tsoro ko kadan sun gwammace mutuwa da dai subi kafiri. 31, kuma sabo jikan tete harbi nai ake anan a kofar fada duk suka tuntsure. 32, Firyan Hadejia shi da bori na salihu kofar gabas suka fadi nan aka cim musu. 33,Dan Dodo Barwa da shi da gwanki baran nufe, sun karbi hartashi a kwaryar kai nasu. 34, Ai babu mai mutuwa gaban ajali nasa kan surfa gero kan daka wasu sun fice. 35, iko idan Allahu yayi nufi nasa ai ba tsimi balle dabara ko daya. 36, Tamkar kamar inuwarka baka guje mata in kai gudun ta bika harma ka tsaya. 37, Hartashi na yawo kamar burduduwa tamkar zubar wake a can a masussuka. 38, Ya ratsa soraye ya ratsa katanguna tamkar kabewa ko kamar tumfafiya. 39, Yasha zarar soro ya keta katanguna da kago da zaure sun zube ba tambata. 40, Tsarnu da kurna har kasa durumi dada ya kar dabinai cediya da itatuwa. 41, Rannan Hadejia munga tashin hankali Allah da manzo su kadai ne magani. 42, Abdulwahabu baka tana hannu nasa artashi ya samar ya tsinke tsirkiya. Edited by (Idris M. Eddy) DA SAURAN BAITI SAI A SAURAREMU A GABA.

Tuesday, October 30, 2012

TAKAICACCEN TARIHIN LIMAMIN HADEJIA M. YUSUF IMAM.

Hadejia A yau.
Hadejia A yau. HADEJIA A YAU!Hadejia A yau. A ci gaba da kawo muku Tarihin wadanda suka bada Gudunmawa a Hadejia, yau Zamu baku takaitaccen Tarihin Bubban Limamin Hadejia MALLAM YUSUF ABDURRAHMAN. Muna farawa da sunan Allah wanda da ikonsane komai ya kasance da kuma Abinda zaya kasance! Tsira da Aminci su tabbata ga Manzon Allah (s.a.w.) wanda ka aiko dashi bil’haqqi da Gaskiya.

An haifi Limamin Hadejia M. Yusuf Imam a unguwar Rumfa da ke cikin Garin Hadejia, a shekarar 10/1/1980, kuma ya fara karatun Addini a Gurin Mahaifinsa M.Abdurrahman Ya’u, bayan ya kai shekaru bakwai (7) shi da ‘yan uwansa an kaisu Makarantar Allo a unguwar Yayari, wato makarantar Mallam Muhammadu Dan birni. Bayan yakai shekaru Ashirin (20) ya koma Makarantar Malam Garba Dake ‘Yankoli, kuma anan ne ya sauke Alqur’ani mai tsarki.

A shekarar 1998 Malam Yusuf ya samu nasarar shiga Makarantar koyon karatun Addini ta Hadejia (S.A.I.S.) inda kuma anan ne ya sake sauke Alqur’ani a Ruwayar Hafsi. Tare da Na’ibinsa M. Habibu Aminu.

A shekarar 2002 Malam Yusuf ya samu nasarar shiga Makarantar Horar da Malamai dake Gumel (ATC.GUMEL) Inda ya samu saidar N.C.E. A bangaren Arabic. Kuma ya samu aikin koyarwa a ma’aikatar Ilmi dake Auyo, bayan shekaru ya dawo yaci gaba da koyarwa a Makarantar S.A.I.S. Dake garin Hadejia.

Malam Yusuf yayi karatun Ilmin Addini a gurin Malamai da dama kamar M. Usman danyaro, Malam Tela Majema, M. Akilu, M. Aminu Ibrahim Daurawa da sauran Malamai.

A ranar Asabat 5/1/2002 Malam Yusuf Imam ya fara bada Ilmi a soron Gidansu, Inda ya fara da Dalibai kamar haka:-

Mohd. Abubakar Malam namu, Ismaila A sabo, Baffale Muhd. Furdi (Baffaliya), Idris Baffa (Liyan), Yusuf abdulkadir wakili, da Adamu A Amar.

Ranar 12/feb./2006 an gayyaceshi da ya gabatar da Maudhu’i a masallacin Juma’a, Inda kuma yayi fadakarwa akan Alamomin tashin Alqiyamah. Wanda kuma wannan fadakarwa ta jawo hankalin mutane akan ranar tsayuwa,wato Alqiyamah.

A ranar Talata 29/Aug./2006 Malam Yusuf ya fara jan Sallah a masallacin juma’a. Sakamakon Rashin lafiyar Limamin wancan lokacin Malam Shehu Qassim.

Haka kuma ranar juma’a, 8/ september/2006 Malam Yusuf ya fara fassara Huduba a Masallacin Juma’a Kuma a wannan lokacine aka tabbatar dashi Na’ibi na biyu.

Ranar Litinin 2/june/2008 Allah yayiwa Limamin Hadejia rasuwa Malam shehu Qassim, kuma bayan mutuwarsa ne Ranar Litinin 23/june/2006 aka tabbatarwa Malam Yusuf Imam ya zama Bubban Limamin Hadejia. Da misalin karfe tara (9:m) na dare.

A Ranar Juma’a 27/June/2008 Mai martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu A. Maje ya nada Malam yusuf a Matsayin Bubban Limamin Hadejia. Da misalin karfe (10:am) na safe. Sannan a ranar ya fara sallar Juma’a Inda kuma yayi Huduba mai daidaita hankali da kuma tabbatar da Ikon Allah shine abinda za’abi a zauna lafiya.

A Gudunmawar da Mallam Yusuf Imam ya bayar a cikin Garin Hadejia ta bangaren Ilmi, Harda karatuka da littatafai da ya karantar A masallacin Juma’a. Kamar:- 1,UMDATUL-AHKAM 2, MUWADDA MALIK 3, LU’U-LU’U WAL MARJAN, IHYA-USSUNNAH Da sauran Littatafai. Da kuma Lecture da yayi a Gurare da dama a cikin garin Hadejia da kewaye.

A watan August na wannan shekara Malam Yusuf ya tafi kasar Sudan Domin Karo Ilmi. Muna Addu’a ga Malam Allah ya haskaka zuciyarsa ya kyautata jinsa da Ganinsa ya kara masa Ilmi da Basira. Ameen.

Allahumma badi’ussamawati wal’ardhi, zaljalali wal’Ikrami, wal-izzatullati la tarami, As’aluka ya Allahu, ya rahman bi jalalika, wa nuru wajhika, antalzim qalbi hifzu kitabuka, kama allamtani, warzuqni antilawahu alannahwullazi yardhika anni. Ameen. Hadejia A yau. HADEJIA A YAU!