content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, February 5, 2013

ME YA HADA ALMAJIRCI DA BARA?

Image Hosted by ImageTitan.com
Hadejia A yau. Ko da kaga wadannan yara kasan su waye? Wadannan su ake cewa Almajirai, ko menene Ma'anar Kalmar Almajiri? Kokuma waye Almajiri?

Almajiri ana nufin Dalibi mai neman karatun Alqur'ani kokuma Ilmin Addinin Musulunci. Domin ya zama malami mai karantarwa! Malamai sune ake yiwa take da :- Masu tsantsanin Duniya saboda kiyamah,
Masu zuyyina Adon Qur'ani.


ALMAJIRI- Idan akace almajiri a kasar Hausa ana nufin mai Neman Ilmin addini.Wadanda idan sukaji Labarin malami a duk Inda yake zasu tashi suje domin neman Ilmi.
Haka kuma Iyaye suma sukan kai 'ya'yansu domin su samu Haddar Alqur'ani ko makamancin hakan.

To a yanzu labarin ya sanja domin Iyaye suna kaiwa 'ya'yansu Almajirci ne don bazasu iya ci dasu ba, zakaga yaro baifi shekara biyar ba (5) an kawoshi wai Almajirci. Anya yaron nan ba gamuwa yayi da ragon Uba ba? Babu ruwansu da'ya'yansu sai damina ta fadi zasu debosusu tayasu Noma.

Zakaga Almajiri ya sato karfunan bakanikai ya kaiwa Makera su saya, Almajiri ya sato gwangwanaye ya kai Jaribola, Almajiri yanzu har kasuwar tsaye! Sun gamu da ragagen Iyaye su dama baburinsu karatu ba, sudai suga babu waninauyi a gabansu.


Allah ya kyauta. Dukda wasu zasuce Ai da sokoto ma kiskadi ce Amma babu wanda ya baka tarihin In sun tashi daga karatu bara suke zuwa. Muma Nan Mai-rakumi ai kiskadi ce da sauran garuruwa.

Amma bamuji cewa suna zuwa bara ba.

Tuesday, January 15, 2013

TARIHIN RAYUWAR SIR. AHMADU BELLO (SARDAUNA) 15/01/2013.

Easily Upload Your Images To Myspace
An haifi Alhaji Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto, a ranar 12 ga watan yuni na 1910 a garin Rabbar na jihar Sokoto dake Arewacin Najeriya. Kakansa shi ne sarkin Musulmi Bello, wadda yana daya daga cikin wadanda suka kafa daular Sokoto, kuma dane ga marigayi Mujaddadi Shehu Usman Dan Fodiyo.


Ahmadu Bello ya fara makaranta a garin Sokoto, sannan ya wuce zuwa makarantar horas da malamai ta Katsina. Kafin daga bisani Sultan ya nada shi malami a makarantar Middle School ta Sokoto.

A shekarar 1938 aka nada shi Sardaunan Sokoto bayan da ya gaza a yunkurin da yayi na zamowa Sultan, wato Sarkin Musulmi. Ya kuma halarci kasar Ingila domin yin karantu kan harkokin mulki a shekarar 1948.

Ya kuma fara shiga harkokin siyasa gadan-gadan bayan dawowarsa daga karatu, inda har aka zabe shi ya zamo mamba a majalisar dokoki ta Arewacin Najeriya. Ya kuma zama ministan ayyuka da raya kasa.

Sir Ahmadu Bello ya kasance Firimiyan farko na yankin Arewa daga shekarar 1954 zuwa 1966. Sannan ya jagoranci jam'iyyar NPC ta lashe kujeru da dama a zaben da aka gudanar bayan samun 'yancin kai..

Bayan kammala zabe, ya zabi ya ci gaba da kasancewa Firimiya, inda ya nada Abubakar Tafawa Balewa ya zamo Fira Minista. Ya taka rawa sosai wajen hada kan yankin Arewacin kasar wanda keda kabilu mabiya addini daban-daban, da kuma aiwatar da ayyuka na ci gaban kasa.


An kashe Ahmadu Bello a ranar 15 ga watan Janairun shekara ta 1966, bayan wani juyin mulki da wasu sojoji 'yan kabilar Ibo suka jagoranta.