content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, August 11, 2013

JAWABIN ALH. BAIDI GAJO YELLEMAN A BUBBAN TARON HADIN KAN AL'UMMAR MASARAUTAR HADEJIA. (KASHI NA BIYU 2)

Free Web Proxy Hadejia A yau.


Anan ina so inyi wasu yan tambayoyi:


1. Kana da kishi ne sai ka jira Mai Martaba Sarki ya tura ma tawaga a gaya maka jamaar Hadejia suna bukatar abu?


2. Kana da kishi ne sai ka jira har jamaa sunyi zanga zanga kafin ka biya musu bukata?


3. Kana da kishi ne baka son zuwa garinku ko cikin jamarka?


4. Kana da kishi ne kake yiwa garinka shigar dare kuma a mota mai tinted glass don kada a ganka?


5. Kana da kishi ne zaka rike mukamin gwamnati har kayi ritaya baka kari jamaarka da komai ba? Da sauransu.


Shi kishi ne zai sa kayi abu ba sai an sa ka ba, kuma in kayi ba sai an gode makaba. Rashin wakilci mai kyau duk rashin kishi ne yake kawo shi. Saboda haka idan dai muka dore akan wadannan abubuwa biyar da na lissafa a sama, to gaskiya babu inda zamu.


A duniyarmu ta yau, da wuya wani ya dafa maka abinci ya sa ma a bakinka. Kai ne zaka yunkura ka nemowa kanka yancinka ko kuma abinda zai amfaneka. Sabida haka dole musa kishi a zukatanmu don mu samowa lardinmu abinda yakamata daga gwamnatin Jiha har gwamnatin tarayya.
Babban burinmu shine mu sami Jiha (Hadejia State). Domin idan ka sami jiha, to duk wasu abubuwa na ci gaba zasu zo da sauki.


To amma kafin mu sami jihar, yakamata muci gaba da amfani da dimbin arzikin da Allah Ya bamu na masu ilimi, Sarakuna, maaikata,
manyan yan siyasa da yan kasuwa domin cimma duk wani cigaba da muke bukata.


Alhamdulillahi muna da Manyan maikata kamar Directors Permanent Secretaries, Ministoci, Soja, Yan Sanda da sauransu. Idan muka hada karfe da karfi muka sa kishi a alaamuranmu babu inda bazamu kaiba. Tarihi ya nuna akwai inda mutum daya mai kishi ya kawowa jamaarsa cigaba.
Saboda haka kara jaddadawa iyayenmu da yayyenmu da kuma musamman matasa manyan gobe gameda duk abinda zasuyi su sa kishi da hadin kai a gaba. Mu zama tsintsiya madaurinki daya muna haduwa da juna muna tattaunawa muna tsaida shawarwari kuma muna daukan dukkan matakin da yakamata don muga cewa mun cimma burinmu.
Matasa kune kunnenmu, kuma kune idanunmu. Saboda haka duk abinda yakamata Jamaa su sani, ku yakamata ku jaddadashi domin a dauki mataki. Har abada yin shiru baya warware matsala sai dai ya kawo rashin jituwa marar amfani Allah Yasa wannan taro ya zama dalilin samarda hadin kai da cigaba ga alummar Hadejia da Jigawa baki daya.

Thursday, August 8, 2013

HAWAN SALLAR AZUMI NA 8/8/2013 ALHAMIS.

Hadejia A yau. Daga Muhd Yawale Hadejia >


kamar yadda Aka sani Hawan sallar Azumi yana da tarihi mai tsawo a cikin Garin Hadejia, wannan sallar ma A bisa al'adar masarautar hadejia ranar sallah maimartaba sarki zai fito daga gida da safe, akafa tareda sauran mutanan fada domin zuwa filin idi. Dukda cewa za'ayi sallar ne a Bubban Masallacin Juma'a na cikin gari. Sakamakon ruwan sama da akayi kuma yayi ta'adi, Mai martaba sarki ya dage Hawan sallah domin Jajantawa ga wadanda ruwa yayi musu ta'adi.


Ga bayanin yanda Hawan sallah yake kasancewa da kuma ta Gurarenda ake bi. Bayan an idar sallar idi liman ya kammala huduba,sai hakimai da sauran mahaya dawaki su hau, sannan maimartaba shima zai hau dokinsa tare da Dandalmu, zai bi ta kasuwar kuda zuwa Titin yahai zuwa makera, sannan zai bi ta makwallah zuwa kofar Liman.


Idan maimartaba sarki yazo daidai kofar liman yakan tsaya domin karfar Jafi daga Hakimai. Wanda hakan ta samo Asali ne Tun Lokacinda Sarkin Hadejia Muhammadu Mai shahada ya dawo daga Yakin Madarumfa, ya tsaya a wannan Gurbin Inda su Jarumansa suke zuwa suke masa Jinjina. Amma a lokacin yana Hakimi ne kafin ya zama sarki. Bayan ya zama sarkin Hadejia sai ya maidata Al'ada wato duk sallar Azumi da Layya zai tsaya Hakimai suzo suyi masa jafi.


Daga nan kuma sai maimartaba sarki ya karasa rumfar manyan baki domin gabatarda jawabin sallah, bayan nan kuma sai maimarta ya karasa gida ya sauka tareda sauran hakimai.


Wannan shine Bayanin Hawan sallar Azumin wannan shekara a takaice da fatan Allah yasa ayi hawa lafiya a sauko lafiya. Allah yaja zamanin maimartaba sarki.