content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, November 12, 2013

ZUWAN AMINU ALA HADEJIA.KADDAMARDA LITTAFIN WAKOKIN HARUNA UJI...

Aminu Ala.
Free Web Proxy

1, Mun gode Aminu Ala, Barka da zuwa Hadejia, gun taron kaddamar da littafin Aji kima.

2, Bismillah zana fara waka da yabon gwanina, gwanin kowa a waka lalle Ala babu dama.

3, Nagodewa Ilahi, Nagode Aminu Ala nagode Aji kima.

4, Ranar Asabat a fantai, A filin kaddamar da tarihin Haruna Uji, da wakoki nai masu dama.

5, Haruna Uji Hadejia, ya bada gudunmawa fa, a wakoki da suke kai sako ai nadama.

6, Ko anyi raha a watse, ko a fadakarda kai zaman rayuwarka ina makoma.

7, Taro kuma yayi kyawu, jama'a duk sunji dadi, suna yin jinjina gun shi wannan wanda yayi littafin Aji kima.

8, Ado Ahmed Gidan dabino, dashi da Aminu Ala, Bashir Ahmed blogger, Marubuta baku dama.

9, Yasir Ramadan gwale bai samu zuwa ba saboda nisa, Amma sakonka na san ya iske Aji kima.

10, In zaka fadi fadi gaskiya, wani shafi ne na Yasir, kaje kaga zunzurutun fasaha babu dama.

11, Godiya gun kungiyoyin, facebook na jihar jigawa, shugabannin Dandalin siyasa mun dau sakonku kuma.

12, Gizagawan zumunci, suma ba'a barsu baya, Dandalin marubuta godiya wakilancinku kuma.

13, Dr. Dahiru godiyarmu, bata manta da shi ba, don shine yayi sharhin littafin Aji kima.

14, Ga sakon godiyarmu ga Dr. Abbas na Ringim, shima ya danyi sharhi, jama'armu Ina makoma.

15, Shugaban karamar hukumar Hadejiya Alhajindo, Umar Danjani p.A. Barka da zuwanka kaima.

Alh. Baffa Bura.... Allah yayi ma Mabudi.......
Hadejia A yau.

Sunday, November 10, 2013

SAKON BANGAJIYA DAGA KWAMITIN KADDAMAR DA LITTAFIN TARIHIN HARUNA UJI DA WAKOKINSA.

Comrade Aji Kima Hadejia!
Free Web Proxy
HADEJIA A YAU!
Assalamu Alaikum! Bayan gaisuwa irinta Addinin Musulunci, muna meka sakon godiya da ban gajiya ga wadanda suka halarci taron kaddamar da Littafin Tarihin Marigayi Haruna Uji da Wakokinsa. Wanda akayi a
Ranar Asabat 9th November 2013, a Dakin Taro na sakandare fantai.

Muna Meka sakon bangajiya da fatan Alkairi zuwa ga Shugaban karamar hukumar Hadejia, Alh. Abba Haruna. Da mai baiwa Gwamna shawara akan harkokin dalibai Alh Umaru Danjani.

Gaisuwa da fatan Alkairi ga
Shugaban kwalejin Ilimi ta jihar Jigawa Dr. Dahiru Abdulkadir. Da shugaban Makarantar koyon aikin Alkalanci ta Ringim Dr. Abbas A. Abbas.

Gaisuwa da fatan Alkairi ga
Babban mai kaddamarwa;

Pharm.Hashim Ubale Yusufu

Muna meka sakon godiya ga kungiyoyin facebook da kuma kungiyoyin Marubuta da Mawallafa na Jihohin kano da jigawa.

Sakon godiya da bangajiya zuwa ga Alh Aminu Ladan Ala
da Ado Ahmed Gidan Dibino.

Muna Meka sakon Jinjina da bangajiya zuwa ga Alh Baffa Bura FNICPR.

Muna meka sakon Godiya ga Iyalan Marigayi Haruna Uji da jama'ar Unguwar Gandun Sarki.
Gaisuwa da godiya ga Jami'an tsaro da 'yan jarida da ma'aikatan yada Labarai.
Allah ya huci gajiya.