content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, November 13, 2013

KASIDAR MALAMAN MAKARANTA.

Hadejia A yau! 1, Madallah da Mallam Usaini Sulaiman Malamin makaranta.

2, Bismillah mu fara da sunan Allah wanda yayi halittu, shi yayi malamin makaranta.

3, Allah shi ya shirya halitta, yayi ruwa wuta rana da wata yayi malaman Makaranta.

4, Shine yayi Malam Usaini, masu prince ta Eco banki kan hanyar zuwa Makabarta.

5, Sabo na gode sarki Allah, wanda ya bani iko na sa 'yata a Prince farar Makaranta.

6, Nagodewa Mallam Usaini, shine Headmastan Prince makarantar nan dana saka 'yata.

7, Ba shi dai ba har malamansa, koda zasu fishi hazaka sun isa malaman makaranta.

8, Nagodewa duk Malamansu, Yarinya a sati biyar ta haddace duk Jihohin kasata.

9, Ga jinjina ga Malam Usaini, da sauran Malamanda suke a Prince kuma kuna zuciyata.

10, Yarinya ta ban mamaki, tun daga A zuwa Zed idan ta zauna zata kawosu 'yata.

11, Lissafi kamar kalkuleta, kai ko kalkuleta ma nasan da kadan fa zatafi 'yata.

12, Burin duk Uba tarbiyya, to Alhamdulillahi Allah shi yayi malaman Makaranta.

13, Iyaye nai kira a gareku, duk mai Da ya kaishi Prince domin yaga fa'idar Makaranta.

14, Ga koyon Handwritting Idan Munje home work suke baiwa 'yata.

Tuesday, November 12, 2013

ZUWAN AMINU ALA HADEJIA.KADDAMARDA LITTAFIN WAKOKIN HARUNA UJI...

Aminu Ala.
Free Web Proxy

1, Mun gode Aminu Ala, Barka da zuwa Hadejia, gun taron kaddamar da littafin Aji kima.

2, Bismillah zana fara waka da yabon gwanina, gwanin kowa a waka lalle Ala babu dama.

3, Nagodewa Ilahi, Nagode Aminu Ala nagode Aji kima.

4, Ranar Asabat a fantai, A filin kaddamar da tarihin Haruna Uji, da wakoki nai masu dama.

5, Haruna Uji Hadejia, ya bada gudunmawa fa, a wakoki da suke kai sako ai nadama.

6, Ko anyi raha a watse, ko a fadakarda kai zaman rayuwarka ina makoma.

7, Taro kuma yayi kyawu, jama'a duk sunji dadi, suna yin jinjina gun shi wannan wanda yayi littafin Aji kima.

8, Ado Ahmed Gidan dabino, dashi da Aminu Ala, Bashir Ahmed blogger, Marubuta baku dama.

9, Yasir Ramadan gwale bai samu zuwa ba saboda nisa, Amma sakonka na san ya iske Aji kima.

10, In zaka fadi fadi gaskiya, wani shafi ne na Yasir, kaje kaga zunzurutun fasaha babu dama.

11, Godiya gun kungiyoyin, facebook na jihar jigawa, shugabannin Dandalin siyasa mun dau sakonku kuma.

12, Gizagawan zumunci, suma ba'a barsu baya, Dandalin marubuta godiya wakilancinku kuma.

13, Dr. Dahiru godiyarmu, bata manta da shi ba, don shine yayi sharhin littafin Aji kima.

14, Ga sakon godiyarmu ga Dr. Abbas na Ringim, shima ya danyi sharhi, jama'armu Ina makoma.

15, Shugaban karamar hukumar Hadejiya Alhajindo, Umar Danjani p.A. Barka da zuwanka kaima.

Alh. Baffa Bura.... Allah yayi ma Mabudi.......
Hadejia A yau.