content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, December 1, 2013

TARIHIN GIZMAWA (NGZIM) DA AL'ADUNSU.

By Comrade Garba Muhd. Hadejia.

GIZMAWA KO NGZIM. Wani sashe ne na Kanuri (Bare-bari) wadanda sukazo daga Borno. Kanuri dai sun kasu gida uku (3), akwai:
Mangawa
Gizmawa
da Larawa.

Mangawa Akasarinsu anfi samunsu a kasar Birniwa da Kirikasamma.

Gizmawa ana samunsu mafi yawa a kasar Guri. A garuruwa irin su Guri, Arin, Dagana, Joriyo, Adiyani, Zugo, Wacakal, Garmaguwa, Garbagal, Margadu,Tukuikui, Dole, Abir da sauransu.

Larawa kuma sunfi yawa a tsakanin Badar, Jigawa, da Bauchi ta kasar Guri. Ana samunsu a Garuruwa irin su: Takazza, Damegi, Gaduwa, Musari da sauransu.

Banbancin da ke tsakanin Gizmawa da Mangawa da Larawa bash da yawa. Kamar banbancin Hausar kano ne da ta katsina ko Hausar sokoto da ta Hadejia. Amma ko wanne yana fahimtar kowane tsakaninsu, wato banbancin a karin harshe ne, kuma a haka suke gane wannan kabilar Ba gizme ne ko Bamange.

Su kuma Kanurin Kadira sun sha bam ban da Gizmawa Larawa da Mangawa. Domin su suna Barbarci ne irin na Borno. Saboda haka ko tsarin zamantakewarsu da sarautarsu ya sha banban.

A bangaren al'adu da zamantakewa basu da bambanci da juna. (Gizmawa Mangawa da Larawa). Tsarin Addinin Musulunci da cudanya da Hausawa ta sa Al'adu da dama na Gizmawa sunyi watsi dasu. Kamar kidan Bango; Rawar Dimas; Rawar biki da al'adun Aurensu duka yanzu ba sosai ake yinsu ba da yawa Hausa ta kwace su.

Wani zaiyi tambaya me yasa aka samu kashe kashen kanuri har gida uku? Dalili shine, zamantakewa da ta bambanta aka samu watsuwarsu a kasar Hausa.

Rabewar Daular Kanem-Borno da Zuwan Rabeh ne yasa wasu daga cikinsu suka tsinci kansu a Daular Usmaniyya, wadda take cike da Hausa Fulani. Kanurinda suke yankin Masarautar Hadejia Musamman ma kasar Guri, sun gauraya da Badawa da fulani da Auyakawa. Hakan tasa karin sautin muryarsu ya sha bamban da kanurin Borno da Yobe. Sannan Al'adunsu sun jirwaye da na Hausawa.

Sannan tsarin Sarautarsu yasa dole suke Amfani da Bulama Maimakon Mai ko Lawan. Amma kuma har yanzu a garin Kadira zaka Iske Kanuri ne suke rike da sarautar garin tare da Badawa da kuma Hausa-fulani kadan.

Sannan ba'a iya bambance Bagizme ko Bamange ko Balare a fuska, domin daga cikinsu zaka iya samun Abubuwa kamar haka:-
*Zube (zane)
*Sutura
*Karin harshe
*Al'adun Aure
*Sana'a
*Tsarin Auratayya
*Addini
*Zamantakewa
*Sunaye
*Son girma
*Kishin yare
*Gardama
*Bajinta
*Ki fadi.

Zane a fuska ya danganta da tsarin iyayen mutum, wadansu iyayen suna da Sha'awar a yiwa 'ya'yansu zube, wasu ko basu da ra'ayin hakan. Saboda haka a cikinsu ana samun mai zube ana samun marar zube.

Barebari ______ Borno

Bamange______ Kirikasamma
Birniwa.

Bagizme________ Guri, Adiyani, Zugo, Gabargal.da sauransu.

Balare__________ Gaduwa, Musari, Takazza, Margadu.da sauransu.

Hadejia A yau.

Sunday, November 24, 2013

TARIHIN HARUNA UJI DA WAKOKINSA. KASHI NA BIYU (2).

Hadejia A yau!



Littafin Muhd. Aji Hadejia.

A kashi na farko kunji cewa Alh. Haruna Uji ya ci gaba da kidan Gurmi gadan gadan.

A lokacin Gwamnan Kano Abdu Bako, sai yaji labarin Haruna Uji, sai yasa aka nemoshi domin yayi masa waka akan wayar da kan Al'umma akan Noma. Saboda haka Gwamna Abdu Bako sai ya hadawa Haruna Uji kayan wasa, kamar Amsa Kuwwa (Loud speaker) da Abin Magana wato (Microphone) da Injin wuta, wato Generator.
Wannan shine lokaci na farko da Haruna Uji ya fara waka da kayan wasa na zamani, kuma ya kama yin waka gadan gadan a matsayin sana'a.

Wakar da yayi a lokacin Itace wakar Noma. Anyi wakar ne da nufin wayar da kan Talakawa su koma Aikin gona.

3.0. WAKOKIN HARUNA UJI NA FARKO.

Alh. Haruna Uji yayi wakoki masu tarin yawa, kuma a cikin Jerin wakokinsa ga wasu daga cikin wakokin da ya fara yi.

*Wakar Naira da kwabo sabon kudi.

*Wakar Gudaliya.

*Wakar Shamuwa.

*Wakar Noma.

*Wakar Bakar Rama.
Wadannan sune kusan Shahararrun wakokin da ya fara yi.

3.1. Ajin Haruna Uji a tsakanin Mawakan baka.

A cikin wani Littafi da Ibrahim Yaro Yahya da Abba Rufa'i suka tsara, Mamuda Aminu ya kawo rabe-raben Mawakan baka zuwa rukunai kamar haka:
*Mawakan Sarakuna
*Mawakan 'yan mata
*Mawakan Jama'a
*Mawakan Mafarauta. Da sauransu.

Ya kawo misalin Mawakan Jama'a shine wanda zai yiwa Sarakuna da 'yan kasuwa da 'yan mata da Masu kudi da talakawa waka. Misali Mamman shata da Haruna Uji da sauransu.

Hakan ta nuna cewa Haruna Uji ya kasance a cikin Mawakan Jama'a, domin ya tabo duk abinda aka zayyana a sama. Wato yakan yiwa kowa waka.

3.1.1 Dangantakar Haruna Uji da Mawakan Baka.

Alh. Haruna Uji yana da kyakkyawar dangantaka da sauran 'yan uwansa mawakan baka, yana girmamasu shima suna girmama shi, sannan ya hori wasu suma sun zama shahararrun mawaka a kasar Hausa. Yayiwa wasu waka kuma shima wasu sunyi masa. A cikin mawakan da suka masa waka har da Alh. Mamman shata, kuma shima Haruna Uji yayi wa Alh. Garba sufa wakar Ta'aziyya bayan ya mutu.

3.1.2 Jerin wasu daga wakokin Haruna Uji.

Bayan rukunin wakokinsa na farko, ga wasu daga cikin wakokin da yayi.

*Wakar Dankabo
*Wakar Alh. Sani Likori
*Wakar Direban Chiyaman
*Wakar (Air vice marshal) Ibrahim Alpha
*Wakar (kwamishinan 'yan sanda) Daudu Gwalalo
*Wakar Haruna karamba
*Wakar Adamu Hassan Abunabo
*Wakar Ahmed Aruwa
*Wakar Asabe Madara
*Wakar Amadu koloji makwallah
*Wakar Bako Inusa kano
*Wakar Balaraba
*Wakar Jimmai Aljummah
*Wakar Birgediya Abdullahi shalin.
*Wakar Dankamasho
*Wakar Fulanin Jebbi fulato
*Wakar Idiyo Mai kayan Babur
*Wakar Kainuwa.

SAURAN WAKOKIN KU DUBA LITTAFIN.

Ka duba kashi na uku (3)