content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, February 5, 2014

EMIRE OF HADEJIA ALH.HARUNA ABDULKADIR.

Emir of HADEJIA Alh. Haruna Abdulkadir ruled from 1950, before he was appointed as Chiroma as Distric head of Guri at the age of 12 in 1921, he experienced a poor health for some years, during which the emirate council ischaired by successive Galadimas, the decendent of Jaji on his behalf who takes charge on the administration of HADEJIA town, just like Sarkin Arewa is district head of Birniwa and Sarkin Dawaki administers kirikasamma district.

But while previously, during colonial period, the Tafida administered Kafin Hausa as district head, until more recently when it was given to Chiroma, a son to the Emir. Fallowing Chiroma’s appointment as a chairman of the Kano state local government service commission he was unfortunately obliged to reside at Kano city, leaving Kafin Hausa to be administered by his deputy while he retain the title.

The old emirate council from 1971 – 1975meet more frequently under the chairmanship of the Galadima Yusuf and Adamu, the major responsibilities of that administration rested firmly with Dan’iya,M. abdulkadir Maidugu, himself a grandson a grand of the Emir Abdulkadir and formally Sarkin Auyo and district head of Auyo, he represented HADEJIA inthe Federal House of Assembly. In his return after the abolition of a civilian rule, he was appointed Senior Executive Councillor of the Emirate council in charge of finance, the native administration,works, rural water supplyand community development.

TheTafida alh. Abdulkadir Maigari, another grandson of the emir Abdulkadir was appointed a councillor in charge of Agric and Natural resourses.The Danburan muhammadu Hurdi……………….

.(Culled from “Local Government at Hadejiia 1977” By M. G. Smith)
By Ma'aji I Abubakar.

Monday, January 13, 2014

HAWAN SALLAR GANI (MAULUDI) A HADEJIA 13/01/2014.

HADEJIA A YAU!
Sallar Mauludi ko Gani a Hadejia ya samo asali ne shekara 90 da suka gabata, wato 1910-1925. A lokacin Sarkin Hadejia Abdulkadir aka fara hawan Mauludi ko Gani a Hadejia, kuma ya kirkiro wannan hawa na Gani ne daidai sabuwar shekarar Musulunci, a Inda yake Ganawa da Hakimansa na waje (District heads) domin suyi jawabin Nasarori da Matsalolinda suka samu a kasarsu a shekararda ta gabata.

Saboda bikin yazo daidai da shekarar Mauludin Manzon Allah (s.a.w.) Sarkin Hadejia Abdulkadir sai yakan hau da Yamma tare da Hakimansa kamar yanda abin yake har yanzu. Kuma a ranar da safe akan gudanarda bukukuwa na Nadin sarautar Hakimi idan ta kama. Sarkin Hadejia Abdulkadir yakan yi hawa da hakimansa inda ake zagaya gari kuma a lokacin yakan bi ne ta Unguwanninda suke da Tsangaya domin ya taya Malaman murnar zagayowar ranar haihuwar Manzon Allah (s.a.w.).

Kamar yanda Abin yake har yanzu Sarki zai fito daga fadarsa da yamma, zai bi ta Tudun mabudi ta Kasuwar kuda sannan yabi ta Kasgayama zuwa Kwarin madaki, sai ya fito ta bayi zuwa Magama hudu zuwa Unguwar Dukawa zuwa Hudu, sannan zai wuce ta Tagurza zuwa Majema zuwa bakin kasuwa, sannan sai ya biyo ta Makwallah zuwa Baderi zuwa Kofar Liman. Sannan ya koma fadarsa. Hadejia A yau.