"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Monday, September 29, 2014

TARIHIN RAYUWAR GALADIMAN KANO A TAKAICE! Alhaji Tijjani Hashim.

Hadejia A yau!< p> An haifi Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim a cikin garin Kano, a shekarar 1932. Mahaifinsa shine Turakin kano Hashim dan sarkin kano Abbas jikan sarkin Kano Ibrahim Dabo. Ya fara karatun Elementary  a garin Bebeji a cikin shekarar 1944. sannan ya shiga makarantar Middile ta Kano inda ya kammala a  shekarar 1951.

A shekarar 1952 Galadiman kano ya fara aiki a  hukumar N. A. (Native Authority) ta Kano a matsayin Malamin Dabbobi, mai kula da tsafta da lafiyar dabbobi. A 1956 aka zabe shi  a matsayin dan majalissa mai wakiltar Sumaila a majalisar dokoki ta Arewa dake kaduna.

A zaman sa a wannan majalisa ne ya rike mukamai da dama ciki har da shugaban hukumar bada kwangila ta Kaduna sannan ya rike shugaban kwamitin tabbatar da jamiyyar NPC ta lashe zabe a lardin Sardauna. Sannan ya rike mukamin Ministan Ayyukan cikin gida na Jihar Arewa. Yayi Kwamishinan lardi mai kula Lardin Kabba wandda yana kan wannan mukamin ne sojoji suka yi juyin mulki.

Bayan ya dawo gida sai  Sarkin Kano Ado Bayero ya nada shi sarautar Dan-isan Kano kuma kansila mai kula da ayyukan gayya da taimakon kai da kai.

A cikin shekarar 1976 ne ya samu karin girma zuwa sarautar Turakin Kano da bashi kulawa da gundumar Kumbotso. sannan A 1980, ya sami canji zuwa kansila marar ofis saboda yawan  harkokinsa na kasuwanci. A shekarar 1989, ya samu karin girma zuwa sarautar Dan-iyan Kano, kuma ya ci gaba rike mukamin kansila marar ofis.

A shekarar 1992, ya samu karin girma a sarauta inda aka nadashi Galadiman Kano kuma shugaban kwamitin kudi na majalisar Sarki. A shekarar 2012 Sarki ya kara masa aikin hakimcin birnin Kano. Wannan aiki ya ke rike dashi har Allah ya masa rasuwa.

Galadiman Kano Tijjani mutum ne mai hakuri da juriya da Alkairi. Kuma yana da daraja a Idanun mtane sakamakon amfani da yayi da damarsa ya kafa mutane a Gwamnati. kuma babu inda zai nemi Alfarma a gwamnati bai samu ba, wannan tasa ake masa Laqabi da GAJERE WAN GWAMNATI.

A ranar28/september/2014, Allah ya yiwa Galadiman kano rasuwa ya rasu ya bar 'ya'ya da Matan Aure da 'yan-uwa da dama. Muna Addu'a Allah ya gafarta masa.

Friday, August 15, 2014

TARIHIN DAN-AMAR DIN HADEJIA M. USMAN GINSAU.

MARIGAYI DAN AMAR ( ALH. MALAM GINSAU) 1917 -1997……………………………..
Marigayi Dan Amar din Hadejia Alhaji Malam Usman Ginsau dan Chiroman Hadejia Ali, dan Sarkin Hadejia Haruna Maikaramba dan Sarki Muhammadu Maishahada ne. Yayi karatun makaranta a garin Hadejia.Yana daga cikin yan makaranta na farko da suko ka bude Clerical College da ke Congo a garin Zaria, kafin ta rikide ta koma ABU Zaria.

Malam ya koma England (UK) domin karin karatu a harkar Community Development. Marigayi Dan Amar ya zama Community Dev. Secretatry na Hadejia N.A. Bayan wannan aiki Marigayi ya kama aikin Gona gadan gadan har zuwa1980.

Ya zama Representative Na Hadejia NA a Old Kano State wanda ya bashi damar shiga Co -operative Society na Nigeria shi da Sarkin Ringim Alh. Sayayadi Mahmudu.Marigayi ya zama 2nd Vice President na Co-operative Society of Nigeria. Yayi Ritaya daga wannan aiki a 1980.

Daga nan Marigayi ya kafa Makarantar Islamiyya da ta Karatun Alkura’ani a Gidansa, shi da kansa yake karantar da mutane, wato manya da yara. Malam yayi ta yin wannan aiki har zuwa 1983 a lokacin da aka nada shi Dan Amar din Hadejia, Hakimin Kafin Hausa.Malam yana daya daga cikin dattijan da suka tsaya wa Kasar Hadejia da addu’a da kuma bada gudummawa wajen duk wani aiki na dattako a Kasar Hadejia. Malam ya rasu ya bar ‘ya ‘ya ashirin da shida.. Daga cikinsu Akwai Dan-Amar din Hadejia na yanzu Alh. Aliyu Usman Ginsau, Hakimin Kafin-hausa, da Baraden Hadejia, Alh. Haruna Usman Ginsau.

Allah ya jikansa ya gafarta masa, ya kara sa albarka a zuriyar da ya bari. Ameen.Posted from WordPress for Android via Hadejia A yau.