content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, January 15, 2017

SARKIN MUSULMI SIR. ABUBAKAR III.

HADEJIA A YAU!


SARKIN MUSULMI ABUBAKAR. 
Cikin 1902, ana kamar badi Turawa zasu zo Sokoto anka haifeni a wani gari wai shi Dange. Tun ina dan shekara Bakwai (7) Marigayi Sarkin Musulmi Hassan ya riĆ™e ni, da na dan yi wayo na isa fara karatu, da yake Sarkin Musulmi Malami ne bai kai ni kowace makaranta ba, sai ya tsareni nan gaba nai shina koya min karatu. Shina kuma kula dani da hana ni yawan Shedana irin ta yara. 

Lokacin da Sarkin Musulmi Hassan ke Mallamin Uban Kasar Dange (Hakimin Dange),  da na fara ido wajen Karatu sai nayi ta taimako nai wajen Aikinga. Muna nan haka cikin Shekarar 1923, Sarkin Musulmi Hassan ya sami Sarautar Sarkin Bauran Dange. Da ya sami wannan Sarautar ni kuma sai ya maishe ni matsayi nai na zama ni am Mallami nai. (Malamin Hakimi). 

Muna nan haka har cikin shekarar 1931, Allah ya nufa Sarkin Musulmi Hassan ya zama Sarkin Musulmi. Da anka natsa sai ya dauko ni daga Dange ya maida ni Sokoto ya nada ni Sardauna, na zama daya daga cikin mataimaka nai ga harkokin kasa.  A cikin Birni kuma ya sa in rinka kula da dukkan wurare na Aiki, kamar su Gidan Yari,  Gidan Ayyuka, likitocin Shanu, Gandun Daji, Dagarawa da dai Sauransu. A wannan lokacin har Kaduna nazo koyon Aikin 'yan Doka dan in samu sanin hanyar taimakonsu. In ko na fita Rangadi in ka jini a wajen wanga Uban kasa yau gobe sai ka jini a wajen wancan, musamman lokacin Haraji ko Jangali. Wani lokaci nakanyi wata biyar ko shida ban leko cikin Birni ba. 

Muna nan haka sai anka yi mani  Uban Kasar Talatar Mafara, nayi watanni hudu (4) ina wagga Sarauta, sai Allah ya yiwa Sarkin Musulmi Hassan rasuwa cikin Shekarar 1938, Allah shi gafarta masa Amin. Bayan rasuwa tai ni kuma Allah ya kawo ni wagga Matsayi. Ina fatan Ubangiji Allah shi taya ni rikawa. 

Sarkin Musulmi Abubakar shine dan Usman,  Usman dan Sarkin Musulmi Mu'azu (wato uban Marigayi Sarkin Musulmi Hassan) Sarkin Musulmi Mu'azu dan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, Sarkin Musulmi Bello dan Shaihu Usman Dan Hodiyo. Allah shi gafarta musu baki daya Amin. 

Sarkin Musulmi Abubakar bai shiga makarantar Turawa ba amma ya koyi Rubutu da Karatu irin nasu. Sarkin Musulmi Abubakar  shine Sarkin da yafi kowa dadewa a Sarautar Sarkin Musulmi, domin ya shekara Hamsin yana kan Halifar Shehu  Usman Dan Hodiyo. Ya fara Sarauta tun lokacin Turawa,  An nada shi ranar 17/yuni/1938, Razdan na Sokoto  Commander J. Carrow shine ya nada shi. Sarkin Musulmi Abubakar yayi Aiki da Gwamnatoci  Takwas (8), a Nigeria bayan samun 'yancin  Kai.  Bayan zamansa Sarkin Musulmi shine ya Baiwa Ahmadu Bello Sarautarsa ta Sardauna a cikin shekarar 1938. Ya rasu yana da shekaru 85 a Duniya,  ya rasu a cikin shekarar 1988. Allah ya Gafarta masa da rahma tare da Al' ummar Annabi baki daya. 


Madogara....... 
1. Sultan Abubakar lll, Littafin Jean Boyd da Hamzat M. Maishanu.
2. Sultan Muhd. Maccido  in the shadow of his Ancestors,  Littafin Hassana Isma'ila Bichi.
3. Gaskiya ta fi Kobo ta Hudu (4) 1939.

Tuesday, November 1, 2016

TARIHIN GARIN KANO.....


               TARIHIN GARIN KANO….


Tarihin Birnin kano yana da tsawo kwarai yana nan kuwa a Rubuce, Munji ance wani mai suna Bagauda ne ya fara Sarautar Kano, kuma ance jikan Bayajidda ne wadda ya kashe Macijiyar Daura. Tun daga zamanin Bagauda har karshen zamanin da Habe suka yi Sarauta anyi sarakuna Arba’in da takwas (48) a kano.

FARKON SHIGOWAR MUSULUNCI…
Ganuwar Kano ta farko an gina ta wajen shekara fiye da Daari takwas da tamanin (880) da suka wuce, amma a lokacin Birnin bashi da girma kamar yanzu, amma ban samu labarin sarakunan lokacin ba sai dai ance a lokacin Maguzawa ne. sai wajen tsakanin 1300 da 1400, wajen shekara dari bakwai da suka wuce, a zamanin wani Sarki da ake kira Yaji, a lokacin ne Addinin musulunci ya shigo kano. Watakila Fulani ne suka shigo dashi, nan da nan mutanen kano suka karbi Addinin musulunci hannu biyu-biyu suka shiga gina masallatai wannan shi yasa mutanen kano suka fara yaki da mutanen da suke kusa dasu da wasu kasashe na Hausa, suka shiga kai hari ga mutanen da suke kudu dasu wato mutanen Bakin Kwara har Biniwai.
      Daga baya sai mutanen da kano taci da yaki suka ture mata Ganuwar suka kuma kore mutanenta, ganin haka sai Ban gaskiyarsu ga Addinin musulunci yayi sanyi suka koma addinin maguzancinsu. Daga nan suka shiga yaki da Zazzau, wani lokaci suyi Nasara wani lokaci ayi Nasara a kansu. A wajen  shekarar 1420, watau shekarar 527 da suka wuce, a wannan lokacin ne  mutanen kano suka fara gamuwa da mutanen Barno, A lokacin ne kuma Rakuma suka fara shigowa kasar Hausa. Sukazo da Ilmi da Littatafai da suka samo daga Timbuktu, daga nan ne hanyar ci gaba ta bude a kasar Hausa musamman Kano.

ADDININ MUSULUNCI YA ZAUNA.
Muhammadu Rumfa yana daya daga cikin shahararrun sarakunan kano, yayi Sarauta tsakanin 1463 zuwa 1493, A zamaninsa ne malamai sukazo daga kasar Masar suka gyara Addinin musulunci a Kano. Muhammadu Rumfa ya ginawa kansa Fada ya kuma gina sabuwar Ganuwa mai kofofi Bakwai (7), a lokacin Birnin ya cika kwarai da jama’a har wasu suna gina gidaje a bayan Ganuwa. Kano kuma sai ta juya yake yake da Katsina, har akwai wani yaki da suka shekara goma sha daya suna bugawa, daga baya Kano taci Nasara. Wani shahararren Sarkin Kano kuma shine Muhammadu kisoki a farkon sarautarsa abin bai yiwa kanawa kyau ba, don wadansu mutanen wajen Timbuktu sun kawowa kasar hari kuma sukaci birnin, amma daga baya kano ta murmure harma suka fara yake yake da Barno. Wannan yaki anyi ta bugashi har kusan zuwan Turawa, mutanen Jukun kuma sun kawowa kano hari har sun cisu, suka saka musu Haraji suna biya amma Jukunawa basu dade ba.

          Daga su fa sai Barno ta lakume kano, duk wadda yasan Birnin kano sosai yasan  gidan da ake kira Gidan Shettima. Nan ne gidan Razdan na cikin Birni, to nan ne gidan da Wakilin Shaihun Barno ke zaune a kano a lokacinda kano ke karkashin Barno.

        FULANI SUN KARBE MULKI…….
Cikin shekarar 1806, watau wajen shekara 216 kenan sai Tawayen Fulani ya kai kano. Anan wani shugaban Fulani da ake kira Dan Yahya ya buga da sarkin kano a wani wuri mil 25 daga Arewacin Birnin kano, yaci Nasara a kansa. Amma dukda haka hargitsi bai kwanta ba. Gidajen Sarauta biyar na Fulani kowa ya kawo gwaninsa yace shi za’a yiwa Sarautar kano. Da aka rasa tayi sai aka kai maganar gaban Shaihu Usman Danfodiyo, shikuwa yaki zaben kowa a cikinsu. Sai ya tambayesu ko wanene yafi kowa Ilmi a kano? Sai suka ce masa wani ne da ake kiransa Sulaimanu, ba ma wadda ya san shi sosai, Da jin haka sai Shaihu Usmanu yayi masa Sarautar kano.

             ZUWAN TURAWA…..
Duk wadda ya karanta Tarihin Nigeria ta Arewa da yadda ta koma hannun Turawa, yaji labarin yadda Magajin Kafi ya kashe Razdan din da ake kira da suna Moloney, da yaga abinda yayi lalle zai janyo bubban Tashin hankali sai ya gudu yaje gaban Sarkinsa Sarkin Zazzau, kunsan da can kasar na cikin kasar Zazzau ne. a zamanin Gwamna Lugga ne akayi abin kafin ya zama Gwamna, sai Lugga yace Sarkin Zazzau ya bada Magajin Kafi ayi masa Shari’ah, amma Sarki yaki. Suka taru da Magajin Kafi suka gudu kano. Sai Gwamna Lugga da Sojojinsa suka bi zuwa kano, kano tace babu wata maganar a bada wadannan mutane sai dai ayi yaki. Gashi ma tana samun riba wajen sayar da Bayi, Turawa suna neman hanawa. Bugun farko anyi shi a cikin 1903 a Bebeji ta kasar kano, Turawa suka make Bebeji suka wuce zuwa Kano. Dama Birni a shirye yake an kulle duk kofofi, Dakaru kuma suna shirye, Amma Sarki da Magajin Kafi sun gudu sun nufi Sakkwato. Turawa suka daidaici  Ganuwa suka buga mata Igwa sai ta Rushe, suka shiga Birni. Da shigarsu sai aka waste fada yak are kowa ya kama gabansa. Kashegari kowa na ta harkarsa kamar ma babu abinda ya faru, in mutum yaje kasuwa sai ya iske mutane suna ta saye da sayarwarsu, babu abinda ya damesu. Amma nan da nan Turawa suka rufe kasuwar sayar da Bayi suka bude Kurkuku aka fidda wadanda suke ciki. Daga nan fa kano ta shiga sabuwar hanya ta ci gaba a cikin mulkin Turawa.

MADOGARA....
Razdan  C.R Niven
Muhammadan Emirate.
Assessment report by colonial Administration.