content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: 11/01/2012 - 12/01/2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, November 27, 2012

MANYAN 'YAN SIYASAR HADEJIA

Hadejia A yau. Wadannan mutane sune Ruhin siyasar Hadejia! Gudunmawar da suka bayar a siyasa da ci gaban yankin Hadejia sai dai Allah ya saka musu da Alkairi. Sunyi siyasa a lokacinda ba'a san Daga kai sai 'ya'yanka ba! Domin sun kafa mutane da dama a Hadejia da kewaye. Duk unguwa zakaga akwai mutanenda suka kafa a siyasa. Lalle sun cancanci yabo. Idan muka fara da Marigayi Alh. Bello Auyo zamuga cewa Ayyukanda yayi a Hadejia har yanzu babu wani ko wata gwamnati da tayi makamancin nasa. Kama da Secretaria, Maternity, da sauran abubuwanda har yau ana amfana dasu a Hadejia. Allah ya kyauta kwanciya. Mallam Ibrahim Kwatalo shima ya gina mutane daban daban a Tarihin siyasar Kasar Hadejia. Duk Wanda yanzu yake Cikin Gwamnati, in ba yaronsa ba sai wanda shine ya kafashi. Allah ya kyauta kwanciya. Alh. Shehu Mujaddadi (Alkali) shehu Illa shehu, shima kamar M. Ibrahim Kwatalo, ya gina mutanenda suka gina Mutane a Tarihin siyasar Hadejia. Kuma Har yau Taswirar siyasarsa ce take Tasiri a Hadejia. Allah ya kyauta Kwanciya. Alh. Muhammadu Danjani Hadejia tarihin siyasar Hadejia bazai manta da kai ba! Shi ya fara Dan majalissar Wakilai a Jamhuriya ta biyu. Kuma jigo ne a jam'iyyar NEPU. Wadanda sukayi yaki da mulkin Danniya da kama karya. Shaho birkita kaji na Garba, Bauna wanda ya dosheta babu maduhu sai wani ba tasa ba. Allah ya kyauta kwanciya. Ahmed Garba (M.K.) ko an kika irinka akeso. Har yau Taswirar siyasar Hadejia tana Hannunsa. Duk unguwarda kaje a Hadejia to akwai mutanen da a kafa kuma suka kafu. Ya samawa matasa aikin yi bansan Adadi ba! Amma nasan babu wanda yayi kamarsa kawo yanzu. Zabgai yabin Bauchi da kare dangi Maza sai kui Hankali, Mai tulu kaji tsoron fad da mai sanda ko yana a kwance! Kainuwa dashen Allah yaya zakuyi? Ruwa sai ya kare Kainuwa ta kare ba dai kaga bayanta ba. An karawa kogi Ruwa mai jinga kayi jingarka zai karya Inda yakeso yabi. Masu fura da zuma sun kula da gwangi, idan gwangin zakusha to, Allah ya bamu zuma ku ya baku Gwangin baya tana son gaba. Hadejia A yau.

Thursday, November 15, 2012

TAKAITACCEN TARIHIN SHETTIMAN HADEJIA DA M. BILYAMINU USMAN.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Musichttp://www.MyspaceImageCodes.net">Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau! Assalamu alaikum! Barkanmu da shigowa sabuwar shekarar Musulunci. A daidai lokacinda muke kokarin Bankwana da shekarar 2012, Allah cikin Ikonsa wannan shekara tazo mana da wani bubban Rashi wanda bazamu manta dashi ba! Wannan rashin kuwa shine na Alh. Bilyaminu Usman da Alh. Hassan Hadejia (shettiman Hadejia). A ranar Asabat 20/october/2012 Allah yayiwa M. Bilyaminu Usman Rasuwa yana da shekaru 83. Kafin rasuwarsa ya rike mukamai da dama musamman a hukumar Ilmi. M. Bilyaminu ya fara koyarwa a Middle school wato Abdulkadir a shekarar 1948, kuma yayi sakataren Ilmi a Hadejia kuma a shekarar 1976 yayi kwamishinan Ilmi a tsohuwar jihar Kano a lokacin Gwamna Sani Bello. Kuma M. Bilyaminu yayi ministan Ilmi a Jamhuriya ta biyu Lokacin shehu shagari. Kuma ya rike Mukamin Chairman primary Education Board a shekarar 1999. Allah ya kyauta kwanciya. Kuma ya bar mana abin koyi a sha'anin zaman rayuwa, wato Gaskiya da rikon Amana. Ko wadanne Irin darasi muka koya daga Rayuwarsa? Hadejia a yau. http://www.facebook.com/Ismailaasabo Haka kuma Ranar laraba 7/November/2012 Allah yayiwa Shettiman Hadejia Rasuwa Alh. Hassan Abbas, sakamakon 'yar gajeriyar jinya, Shettiman Hadejia tarihin Hadejia bazai manta da irin Gudunmawar da ya bayar ba ta hanyar ci Gaban garin Hadejia da Taimakon Addini, masu iya magana suna cewa ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Wannan Haka yake Kasar kago bata Maida Kago. Shettiman Hadejia ya rike mukamin Minista a lokacin Jamhuriya ta daya, bayan nan ya rike mukamin Ministan Man fetur a zamanin Ibrahim Babangida, kuma shine shugaban Kaduna polo club, sannan shine Chairman Board of Directors a kamfanin Leadway Assurance! Sannan Board member A Masallacin sultan Bello dake Kaduna. Allah ya kyauta kwanciya! A cikin abubuwanda ya bari wadanda zamuyi koyi dasu akwai kyautatawa al'umma da taimakawa Addinin musulunci da zumunci. Hadejia a yau. Muna rokon Allah ya bamu Albarkar wadannan mutane, Allah ya maida mana makamantansu, Allah ka kara mana Gaskiya da Rikon Amana da taimakon Al'umma. HADEJIA A YAU.

Monday, November 5, 2012

SULE LAMIDO SAI GODIYA.

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU! Alhamdulillahi Godiya ta tabbata ga Allah wanda yake bada Mulki ga wanda yaso, kuma a lokacinda yaso, Tsira da Aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu wanda Allah ya aikoshi da shiriya da rarrabewa tsakanin Karya da Gaskiya!

Bayan haka muna kara Godiya ga Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Dr. Sule Lamido, wanda Allah ya bashi Mulkin Jigawa domin ya Gudanar dashi bisa Gaskiya da Adalci. Alhamdulillahi Jigawa a yau.

Ranar Litinin 5/11/2012. Mai Girma shugaban kasa ya kawo mana ziyara Hadejia a karkashin mulkin Gwamna Sule Lamido, Inda kuma akayi hawan Daba kasaitacciya. Hakika wannan abin Alfahari ne a garemu Hadejiawa kuma babu abinda zamucewa Mai Girma gwamna sai godiya.

Bayanda shugaban kasa yazo Hadejia ya ziyarci fadar Mai martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje, bayan yaga Hawan Daba da aka shirya masa ya gana Da Mai martaba Sarki. Kuma ya nemi Alfarma guda Uku wadda zata kara Inganta wannan yanki na Hadejia. Na farko ya nemi Alfarmar Gwamnati da ta ci gaba da aikin B.E.C. Wanda a halin yanzu ya dakata, na Biyu ya nemi Alfarmar da ayi mana Maganin Ambaliyar Ruwa da ta Addabi wasu sassa na Hadejia.

Na uku ya nemi Alfarmar a Sake Inganta Jingar Kogi wadda ake samun Asarar Dukiyoyi da amfanin Gona.

Muna kara Godiya ga Wannan Gwamnati wadda A zamaninta ne Jigawa ta tabbata Jigawa. Hakika duk wanda yasan Jigawa shekara Bakwai baya Idan yazo zai tabbatarda Jigawa ta samu Uba. Jigawa abar Alfaharinmu, Sule Lamido Abin Alfaharin Jihar Jigawa.

Hakika abubuwanda mukeji a baya kunnenmu ne yaji Idonmu bai gani ba. Dan haka ka bada saida akan abinda Idonka ya gani yafi akan abinda kunnenka yaji. Muna kara jinjina ga Mai Girma Gwamna Wanda ya daga Darajar wannan Jiha tamu. Jigawa ada take Jaririya amma a yanzu Uwace a zamanin Sule Lamido.

Ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Jigawa ta tattara Manyan Mutane masu hazaka! kama daga Gwamnan zuwa comishinoni da sauransu. Jigawa tarin Allah Lamido Ikon Allah.

Allah ya huci gajiya, Allah ya maida kowa Gidansa Lafiya. Ameen. Hadejia a yau.

Sunday, November 4, 2012

WAKAR TARIHIN YAKIN HADEJIA DAGA LIMAN MUHAMMADU (Fassara daga Alh. Ibrahim katala).

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau. 1, Allahu sarki shi kadai yake wahidun, sammai da kassai jalla bashi da kishiya. 2, Shi ba fari shi ba baki ba ubangiji ba ja ba ba alkashi bashi ga rawaya. 3, Ba sake sake ba ba kamar yarani ba shudi da kore jalla bashi da mai kama. 4, Zatinsa baya tattara bai rarraba da kawai da motsi bayayi ko sau daya. 5, Sarkinda ba na biyunsa ba na uku nasa ka dadan basira zanyi waken shahidu. 6, Ranar talata munga tashin duniya Rannan Muhammadu yai shahada zahira. 7, Shi yai jawabi ya fada shi bai gudu kuma bashi mai kamu a darul duniya. 8, Raggo ake kora a bishi a cim masa amma sadauki bai gudu sai faduwa. 9, Sarki Muhammadu yai jawabi ya cika shi bashi mai kamu a jashi ya tunkiya. 10, Dan melle sarkin yaki shima ya fada in dai da rai sarkinmu baya kamuwa. 11, Ma'ajin Hadejia saleh shima ya fada mun dau shahada zahira bahakikiya. 12, Manya da yara duk shirin yaki suke kowa yana wanka yana yin alwalah. 13, Kowa yana yin sallama a gida nasa sunsa gabansu a lahira ba dawaya. 14, Jama'ar Hadejiawa fa duk sun hallara kowa yana cewa fa mun zama shahidai. 15, Sarki Muhammadu mai shahadar zahiri ba badili ko dai cikin tawaga tasa. 16, Shi bai kamar tsoro ba baya razana kan ya ije ma babu sauran hanzari. 17, Ajali idan yayi babu kwana duniya kai dai zamo kullum shiri duka safiya. 18, Shi bai kamar tsoro a baya razana baya gudu dan Garba sarkin jarumai. 19, Mutuwa tafarki wanda kowa zayabi ai kulli nafsin dukka rai zai dandana. 20, Aka daura sirdi nai ya hau bisa ya tsaya yace mu dau himmar shahada zahira. 21, Sarki Muhammadu baya tsoro ko kadan Allah ma'aiki su take tsoro kadai. 22, Hauninsa linzamin mayani ya rike damansa tasbihi salatin annabi. 23, Dan mai karatu tudun kasa ba dawaya dan garba jikan sambo sarkin adalai. 24, Duk mai shahada auwalinsa madacima suka barace da fari ya mutu shahidi. 25, Farkon hawa yaki galadima sai haru ranar talata sun ka sauka a barzahu. 26, Alkali sarkin yaki kaura amada sarkin arewa da sunkaje can sun tsaya. 27, Suka jeru sunka tsaya a nan kofar gabas kafin suje har mai ruwa ya taddasu. 28, Kasan igwa dokinmu shi bai santa ba duka dokuna na faduwa ba lissafa. 29, Igwa tana tashi madafa na zuba yau sai ta Allah babu sauran shawara. 30, Jaruman Muhammadu basu tsoro ko kadan sun gwammace mutuwa da dai subi kafiri. 31, kuma sabo jikan tete harbi nai ake anan a kofar fada duk suka tuntsure. 32, Firyan Hadejia shi da bori na salihu kofar gabas suka fadi nan aka cim musu. 33,Dan Dodo Barwa da shi da gwanki baran nufe, sun karbi hartashi a kwaryar kai nasu. 34, Ai babu mai mutuwa gaban ajali nasa kan surfa gero kan daka wasu sun fice. 35, iko idan Allahu yayi nufi nasa ai ba tsimi balle dabara ko daya. 36, Tamkar kamar inuwarka baka guje mata in kai gudun ta bika harma ka tsaya. 37, Hartashi na yawo kamar burduduwa tamkar zubar wake a can a masussuka. 38, Ya ratsa soraye ya ratsa katanguna tamkar kabewa ko kamar tumfafiya. 39, Yasha zarar soro ya keta katanguna da kago da zaure sun zube ba tambata. 40, Tsarnu da kurna har kasa durumi dada ya kar dabinai cediya da itatuwa. 41, Rannan Hadejia munga tashin hankali Allah da manzo su kadai ne magani. 42, Abdulwahabu baka tana hannu nasa artashi ya samar ya tsinke tsirkiya. Edited by (Idris M. Eddy) DA SAURAN BAITI SAI A SAURAREMU A GABA.