content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: 2016

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, November 1, 2016

TARIHIN GARIN KANO.....


               TARIHIN GARIN KANO….


Tarihin Birnin kano yana da tsawo kwarai yana nan kuwa a Rubuce, Munji ance wani mai suna Bagauda ne ya fara Sarautar Kano, kuma ance jikan Bayajidda ne wadda ya kashe Macijiyar Daura. Tun daga zamanin Bagauda har karshen zamanin da Habe suka yi Sarauta anyi sarakuna Arba’in da takwas (48) a kano.

FARKON SHIGOWAR MUSULUNCI…
Ganuwar Kano ta farko an gina ta wajen shekara fiye da Daari takwas da tamanin (880) da suka wuce, amma a lokacin Birnin bashi da girma kamar yanzu, amma ban samu labarin sarakunan lokacin ba sai dai ance a lokacin Maguzawa ne. sai wajen tsakanin 1300 da 1400, wajen shekara dari bakwai da suka wuce, a zamanin wani Sarki da ake kira Yaji, a lokacin ne Addinin musulunci ya shigo kano. Watakila Fulani ne suka shigo dashi, nan da nan mutanen kano suka karbi Addinin musulunci hannu biyu-biyu suka shiga gina masallatai wannan shi yasa mutanen kano suka fara yaki da mutanen da suke kusa dasu da wasu kasashe na Hausa, suka shiga kai hari ga mutanen da suke kudu dasu wato mutanen Bakin Kwara har Biniwai.
      Daga baya sai mutanen da kano taci da yaki suka ture mata Ganuwar suka kuma kore mutanenta, ganin haka sai Ban gaskiyarsu ga Addinin musulunci yayi sanyi suka koma addinin maguzancinsu. Daga nan suka shiga yaki da Zazzau, wani lokaci suyi Nasara wani lokaci ayi Nasara a kansu. A wajen  shekarar 1420, watau shekarar 527 da suka wuce, a wannan lokacin ne  mutanen kano suka fara gamuwa da mutanen Barno, A lokacin ne kuma Rakuma suka fara shigowa kasar Hausa. Sukazo da Ilmi da Littatafai da suka samo daga Timbuktu, daga nan ne hanyar ci gaba ta bude a kasar Hausa musamman Kano.

ADDININ MUSULUNCI YA ZAUNA.
Muhammadu Rumfa yana daya daga cikin shahararrun sarakunan kano, yayi Sarauta tsakanin 1463 zuwa 1493, A zamaninsa ne malamai sukazo daga kasar Masar suka gyara Addinin musulunci a Kano. Muhammadu Rumfa ya ginawa kansa Fada ya kuma gina sabuwar Ganuwa mai kofofi Bakwai (7), a lokacin Birnin ya cika kwarai da jama’a har wasu suna gina gidaje a bayan Ganuwa. Kano kuma sai ta juya yake yake da Katsina, har akwai wani yaki da suka shekara goma sha daya suna bugawa, daga baya Kano taci Nasara. Wani shahararren Sarkin Kano kuma shine Muhammadu kisoki a farkon sarautarsa abin bai yiwa kanawa kyau ba, don wadansu mutanen wajen Timbuktu sun kawowa kasar hari kuma sukaci birnin, amma daga baya kano ta murmure harma suka fara yake yake da Barno. Wannan yaki anyi ta bugashi har kusan zuwan Turawa, mutanen Jukun kuma sun kawowa kano hari har sun cisu, suka saka musu Haraji suna biya amma Jukunawa basu dade ba.

          Daga su fa sai Barno ta lakume kano, duk wadda yasan Birnin kano sosai yasan  gidan da ake kira Gidan Shettima. Nan ne gidan Razdan na cikin Birni, to nan ne gidan da Wakilin Shaihun Barno ke zaune a kano a lokacinda kano ke karkashin Barno.

        FULANI SUN KARBE MULKI…….
Cikin shekarar 1806, watau wajen shekara 216 kenan sai Tawayen Fulani ya kai kano. Anan wani shugaban Fulani da ake kira Dan Yahya ya buga da sarkin kano a wani wuri mil 25 daga Arewacin Birnin kano, yaci Nasara a kansa. Amma dukda haka hargitsi bai kwanta ba. Gidajen Sarauta biyar na Fulani kowa ya kawo gwaninsa yace shi za’a yiwa Sarautar kano. Da aka rasa tayi sai aka kai maganar gaban Shaihu Usman Danfodiyo, shikuwa yaki zaben kowa a cikinsu. Sai ya tambayesu ko wanene yafi kowa Ilmi a kano? Sai suka ce masa wani ne da ake kiransa Sulaimanu, ba ma wadda ya san shi sosai, Da jin haka sai Shaihu Usmanu yayi masa Sarautar kano.

             ZUWAN TURAWA…..
Duk wadda ya karanta Tarihin Nigeria ta Arewa da yadda ta koma hannun Turawa, yaji labarin yadda Magajin Kafi ya kashe Razdan din da ake kira da suna Moloney, da yaga abinda yayi lalle zai janyo bubban Tashin hankali sai ya gudu yaje gaban Sarkinsa Sarkin Zazzau, kunsan da can kasar na cikin kasar Zazzau ne. a zamanin Gwamna Lugga ne akayi abin kafin ya zama Gwamna, sai Lugga yace Sarkin Zazzau ya bada Magajin Kafi ayi masa Shari’ah, amma Sarki yaki. Suka taru da Magajin Kafi suka gudu kano. Sai Gwamna Lugga da Sojojinsa suka bi zuwa kano, kano tace babu wata maganar a bada wadannan mutane sai dai ayi yaki. Gashi ma tana samun riba wajen sayar da Bayi, Turawa suna neman hanawa. Bugun farko anyi shi a cikin 1903 a Bebeji ta kasar kano, Turawa suka make Bebeji suka wuce zuwa Kano. Dama Birni a shirye yake an kulle duk kofofi, Dakaru kuma suna shirye, Amma Sarki da Magajin Kafi sun gudu sun nufi Sakkwato. Turawa suka daidaici  Ganuwa suka buga mata Igwa sai ta Rushe, suka shiga Birni. Da shigarsu sai aka waste fada yak are kowa ya kama gabansa. Kashegari kowa na ta harkarsa kamar ma babu abinda ya faru, in mutum yaje kasuwa sai ya iske mutane suna ta saye da sayarwarsu, babu abinda ya damesu. Amma nan da nan Turawa suka rufe kasuwar sayar da Bayi suka bude Kurkuku aka fidda wadanda suke ciki. Daga nan fa kano ta shiga sabuwar hanya ta ci gaba a cikin mulkin Turawa.

MADOGARA....
Razdan  C.R Niven
Muhammadan Emirate.
Assessment report by colonial Administration. 

Sunday, October 30, 2016

TARIHIN GARIN BARNO (MAIDUGURI)...

HADEJIA A YAU!
        
Mutanen  Barno suna da yawa qwarai, ita kuwa Barno tana kusa da Tafkin Chadi ne, wannan Tafki yana da ban mamaki qwarai don baya da zurfi har mutum yana iya tuqa kwale-kwale ya ratsa Tafkin na Chadi saboda Ruwan Kogi kaxan yake shiga Tafkin kuma iska tana hura shi daga gefe zuwa gefe. Da ka matso kusa da Tafkin sai kayi ta ganin abin mamaki, in kana gabar tafkin bazakaga Ruwa ba sai kayi ta ganin Ciyayi har fiye da Mil biyu gabanka. Mazauna wurin Larabawa ne da suka Dogara da tafkin don rufawa kansu Asiri. In ka duba kewaye da tafkin sai kaga kasa ce shimfidaddiya, ta ko ina kuwa shimfidaddiyar kasar nan ta kai Mil dari da wani abin, amma in ka matsi tafkin sai kaga gangara kadan zuwa tafkin. 

Wannan shimfidaddiyar kasa ta zama kamar hanya tsakanin  kasashen Afrika ta yamma da tsakiyar Afrika da Dafur da kuma kwarin kogin Nil. Ta nan ne matafiya na Afrika na shekaru suke wucewa. Hanyar nan tana da wuyar bi amma bata da wuya kamar hanyar da take Arewacinta, wadda sai an ratsa Hamada ko wadda sai an bi tsakanin Duwatsu  daga kudu. Wurin nan kana ma kamar fadama lokacin Ruwa, amma kuma in Ruwan ya janye ana iya wucewa. Iyakar saninmu wadansu mutane ne an ace musu ‘SO’ suka fara ama a wurin nan, kuma ana cewa mutanen suna da Girman jiki da tsawo kamar wadanda suka fara ama a Kano. Amma cikin Tarihi abinda aka iya samu nasu shine manya manyan Tukwane, wadda akace matansu suna dibar Ruwa dasu. Tukwanen suna da nauyi har sai mutane da dama sun hadu zasu iya daga su daga wurin da suke. Kowace Tukunya kuma tayi misalign kafa biyar a tsaye, wadannan mutane a Gabar Tafkin Chadi suka zauna. Babu dai wadda yasan daga inda suka fito, kuma da wuya a kara gano wani abu game dasu, sai dai in an kara hako irin abinda suka bari…


WADANDA SUKA FARA MULKI A WURIN….
Wadanda suka fara mulki a kewayen Tafkin Chadi, wadansu mutane ne ana ce dasu SEF. Asalinsu kuwa Berber ne, watakila sunzo ne da kansu ko kuma sun hade ne da mutanen da sukazo daga kudancin Bahar Rum ne. sune suka kafa Mulkin Kanem, suka zauna sukayi mulki a wurin yau misalin Shekara 1,225 kenan da suka wuce, sai wasu Kabilu suka kara zuwa suka zauna har suka kara girman wurin. Cikin 1250, shekara ta 697 kenan Dunama  Dabalemi, Mai na Kanem ya mulki makekiyar kasa wadda tun daga Kogin Nil taa kai Kogin Kwara, har wani yankin Hamada Kasar nan ta mamaye. Daga Fezza (A Kudancin Tarabulus) har Duwatsun nan na Mandara na kudu da Chadi duk kasarsa ce. Kasarsa tayi iyaka da Songhai wajen kogin Kwara, har dai kasar Hausa duk cikin Kasarsa take a da. Masu mulkin wannan kasa suna saduwa da masu mulkin kasar Masar da Tarabulus harma wakilan waccan kasar suna zuwa wannan kasar don wani muhimmin Al’amari. A lokacin nan ana tsammanin Kanuri wadda Hausawa ke kiransu Barebari, sun gauraya da wasu kabilu ne daban. Ana tsammani su Kanuri tare sukazo da kakannin kakannin Hausawa.

Bayanda masu mulkin Kanem watau Sef, suka kaura sai suka koma kano, bayan shekara saba’in (70) sai Mai Ali Ghaji ya sake kafa wani mulkin amma a yammacin Chadi ya kafa. Bubban Garinsa shine Birnin Ngazargamu, yanzu garin ya zama kango amma da ganin kangon Garin kasan bubban gari ne. misalin shekara dari uku (300) da suka wuce anyi sarakuna masu hikima a Barno, kamar yadda akayi a sauran kasashe. Cikin Sarakunan Barno akwai wani wai shi Idris Alooma, yana da wani Malami wadda ya rubuta labarai iri iri na lokacin nan, wadda da taimakonsu muna iya gane abinda ya faru a lokacin nan. Amma a lokacin nan Barno ba kamar Barnon da muka sani a yanzu take ba, lokacin nan daga Nguru sai ka fada kasar Hausa. Nguru  tana da muhimmanci kwarai a Daular Kanem, saboda haka sai aka damkata ga Galadiman Barno, daya daga cikin manyan Hakiman Barno…..

       FULANI SUN YAKI BARNO……….
Fulani sun baiwa Barno Kashi har fiye da yadda suka ba Kasashen Hausa, Fulani sun ci Bubban Birnin Kanuri. Koda yake Kanuri sun kori Fulani amma daga baya sun dawo, to da suka sake dawowa sai Mai na Barno ya nemi Taimako daga Kanem. Muhammad Al-Amin El-kanemi wadda aka fi sani da Shaihu Laminu, shine shugaban wadanda sukazo taimakon nan. Shi Shaihu Laminu Haziki ne kwarai, kuma yana da Ilmi mai yawa. Ya taba zuwa Hajji kuma ya taba zama a Masar, lokacin da zaizo yayi ta Gargadi ga mutanen Kanem don suzo su taimaki mutanen Barno. Da sukazo kuwa sai suka samu sa’a suka kori Fulani, amma Fulani basu dade ba sai suka sake cin Birnin Ngazargamu a cikin shekarar 1810. Har yanzu Shaihu Laminu ya sake zuwa Taimakon Kanuri, a wannan lokacin sai ya gayyaci Larabawa suka taimakeshi ya sake korar Fulani. To sai Shaihu Laminu ya zauna a Kukawa, koda yake Sarakunan Barno suke kula da Al’amarin kasar, dukda haka Shaihu Laminu shine Uban kasar Barno.
Umaru dan Shaihu Laminu shine ya gwada sosai don yana so yazama Mai na kasar Barno, amma Mai na karshe wani yaro dan shekara Goma sha bakwai (17), yayi kokarin hana Umaru ya zama Mai. To sai yaki ya tashi, Yakin nan fa shine karshen Sarakunan nan da akayi a Barno daya na bin daya har misalign shekara dubu (1000).

  SHIGOWAR RABEH AZ-ZUBAYR……
Cikin shekarar 1893 sai Rabeh yazo daga Sudan da shiri na gaske, ya afkawa Barno nan da nan yayi Karin kumallo da ita. Allahu Akbar! Cikin yakin nan ne aka kashe Kakan Shaihun Barno na yanzu, wajen shekara shida (6), Rabeh da mutanensa sai abinda sukaga dama a Barno. Wani yaki da akayi a kusa da Farlomi, nan faransawa suka kori Rabeh har suka kashe Dansa Foldlellah. Bayan lokaci kadan sai Ingilishi suka ci kasar da yaki kuma suka mayar da zaman Lafiya da Salama. 

   RIKICIN BOKO HARAM......... 

Saturday, October 15, 2016

BUPOLY HADEJIA... TRIBUTES TO PROF. M.A.HUSSAINI. By Auwal Abu Daud.

HADEJIA A YAU!


The narratives of Binyaminu Usman College of Agriculture, Hadejia now Binyaminu Usman Polytechnic, could not be complete without identifying with the former Provost and Rector.
Prof. Muhammad Auwal Hussaini . The
journey begins four years ago, precisely on 19th September, 2012 when he took over as the 2nd Provost of the former autonomous College of Agriculture. His arrival at the scene brought hope and revolutionized the institution to stand tall among its contemporaries.

Prof. M.A.Hussaini as erudite professor
of Agronomy brought his wealth of experience to bear on every sphere of the institution. He came at a time when the College was desperately in need of
leadership with vision to frontally steer the ship of the crisis ridden institution which clearly manifested in low students’ enrolment, low teacher to students ratio, obsolete equipment, low staff moral and a kind of generalized hopelessness. To his credit within shortest time the scenario changed for better. The manifestation of his good leadership style could be recognized through modest achievements recorded in the following areas:

1. Increasing number of academic staff: The academic staff was strengthened by
54.76% rise by recruitment of competent and dedicated staff through open and transparent process for the first time in the history of the College; from 38-84 academic staff.
2. Establishment of new academic programmes: the number of academic programmes of the institution were rised from four(4) National Diploma
programmes to nine (9), 55.55% increase. Also 0-5 Higher National Diploma (HND) programmes were equally established. Eight (8) programmes were granted interim accreditation by National Board for Technical Education (NBTE).
3. Provision of laptop computers to all
academic staff and strategic non- academic staff through National Communication Commission (NCC) ICT
support scheme.
4. Digitization of Student Record and Staff Management System by establishing first website and portal of the institution. 
5. Digitization of admission process, results processing and examinations management.
6. Establishment of Management Information System Unit (MIS) for the institution.
7. Provision of Wireless Internet Service at the institution library.
8. Reinvigorating the institution’s animal farm by providing necessary facilities.
9. Establishment of functional poultry
farm for the institution.
10. Establishment of standard orchard
11. Establishment of Date Palm plantation.
12. Establishment of Moringa plantation.
13. Establishment of Neem Tree plantation at new campus of the institution.
14. Establishment of Guava plantation.
15. Completion of new site of the institution with state of the art facilities.
16. Establishment of modern Digital Metrological Station (DMS).
17. Regular payment of staff development packages.
18. Regular supply of staff welfare package
19. Establishment of Staff Welfare Committee (SWC).
20. Establishment of fish farm and hatchery.
21. Regular training and retraining of staff on areas of strategic interest to the institution.
22. Speeding process of result collection.
23. Landscaping of major roads at new campus.
24. Providing mentorship to staff.
25. Drastically reducing corruption in
admission and examination through the use of Information and Communication Technology (ICT).
26. Establishment of Monthly Bulletin
for the institution in order to improve image of the institution. And above all, on 15th January, 2016 the College was upgraded to status of a Polytechnic by the Jigawa State Government.

Prof Dedication to work is uncommon as he demonstrated by coming to office
regularly; from Monday to Friday sometime even on weekends.
These traits really had endeared him to
many. Unlike contemporary Africans, when his first term was coming to an end many people encouraged him to seek for second term but he told them that he has done his best to the institution and therefore there is need for him give chance for somebody to try and consolidate on his gains. The Polytechnic community will certainly miss his humbleness and dedication to service.

As you retire as our Rector we fervently pray that May Almighty Allah reward your meritorious service to your state and your country and may he give you good health and strength to continue to render selfless service to humanity.
Thank u sir. 

Wednesday, October 12, 2016

THE SHETTIMA OF HADEJIA, BARRISTER IBRAHIM HASSAN HADEJIA. By Muhammad Lawal Yahya.

HADEJIA A YAU!

THE DEPUTY GOVERNOR BARRISTER IBRAHIM HASSAN Born in 1965 into the family of late elder statesman, Alhaji Hassan Hadejia who was until his death, the Shetima of Hadejia, the present Deputy Governor. 

 Barrister Ibrahim Hassan went through the Sacred Heart Primary. School, Kaduna, Barewa College Zaria, School of Basic Studies, ABU zaria, from where he was enrolled into the Faculty of Law, Ahmadu Bello University, Zaria, and the Nigerian Law School Lagos after which he was called to the Bar. He later went to the Department of Continuing Education, at the Oxford University, United Kingdom where he obtained a Diploma in Computing in 2005 Between 1990 and 1999 after serving as a Youth Corper, with the Nigerian Telephones and Transmission, Iganmu, Lagos, as Marketing and dealer relationship manager. 

 Barrister Ibrahim worked at the Credit and Finance Ltd as Company Secretary and legal Adviser as well as Head Recovery Task Force, Liberty Merchant Bank plc, Head Credit Administration, Head Foreign Operations, Member Task force on migration of Bank’s Software from Bancmaster to Kapiti and AS400 environment, Foreign Exchange Dealer, Manager Port Harcourt Branch; responsible for Eastern Region, most profitable branch 3 years in a row, Head International Treasury and Chief Foreign Exchange Dealer, with direct responsibility for a trading open position limit of $5 Million daily.

In 1999 he became the Attorney General and Commissioner of Justice, Jigawa State, a position he held until 2000 when he was appointed the Secretary to the State Government from where he subsequently rose to the position of Deputy Governor in 2002 until 2007 when the Government handed over to a new administration. To his credit during his first coming, Barrister Ibrahim Hassan was responsible for ensuring the inclusion of Jigawa State as one of the 6 DFID focal states, leading to the establishment of the SLGP program (State& local Government Program) in the state and 4 subsequent DFID supported programs namely, PATHS(Partnership for transforming health systems, JEWEL (Jigawa Wetlands livelihood Program) and the Access to Justice Program, introduced and established Integrated Financial Management Information Systems (IFMIS) to accommodate unified budgeting and link the budget ministry with the State treasury and Salaries and pensions department, and organized and produced the Jigawa SEEDS document (J-SEEDS) and translated abridged versions in English & Hausa and a 13 episode Hausa radio drama series to explain and disseminate J-SEEDS as well as supported the production of LEEDS for 9 out of 27 local governments. He also chaired the DFID financed State and Local Government Program (SLGP) to facilitate the implementation of reform in State and Local Government policies and successfully re-organized contracting and tendering process through the reorientation and repositioning of the Finance & General purposes committee (FGPC) and the establishment of the Project Monitoring and Evaluation Unit (PMU). He is a member of the Nigerian Bar Association, and the chartered Institute Of Arbitration, United Kingdom. 

His hobbies include reading, Web research and data mining, squash, and to cap it all,  the Barrister is a Computer adept, proficient in all Microsoft Office applications, Comfortable with both Windows and Mac OS LAN Administration (AS400, NT, Novell) java programming. He is married with children.

Saturday, October 8, 2016

GALADIMAN HADEJIA USMAN.....Daga Suleiman Ginsau.




NAZARI AKAN TARIHI DA RAYUWAR GALADIMAN HADEJIA ALH. USMAN ABDUL'AZIZ. (USMAN II)

(TARE DA SULEIMAN GINSAU)

"SALSALAR HAIHUWA DA KARATUN GALADIMA"

Kamar yadda yake a bayyane an haifi Mai Girma Galadiman Hadejia Alh. Usman Abdul'aziz a cikin garin Hadejia da ke Jihar Jigawa a ranar 23 ga watan Oktoba a shekara ta 1959, wadda yayi dai-dai da 20 ga watan Rabi'ul Sani na shakarar ta 1379. Idan muka dubi rayuwar Galadima a bangaran karatunsa ya halarci Makarantar Hudu Islamiyya dake garin Hadejia a shekarar 1963, ya halarci Makarantar Firamare ta Hadejia Central a cikin shekarar 1965-1971, inda daga nan kuma ya wuce zuwa Kwalejin Geamnati dake Kano wadda a yanzu ta koma Rumfa Kwalej a shekarun 1972-1976, a matakin sakandare daga nan kuma ya wuce Makarantar koyan sana'a dake Kaduna (Kaduna Polytechnic) anan ne ya yi karatunsa na Karamar Diploma ckin shekarun 1976-1979. Yayi Babbar Diploma akan kasuwanci a (Kaduna Polytechnic) cikin shekarun 1979-1981. Yaci gaba da karatunsa a Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa Bauchi a Shekarun 1997-1998 ya sami shaidar Babbar Diploma ta gaba da Digiri a kan kasuwanci, daga nan ya wuce kasar waje domin karo Ilmi inda ya shiga Jami'ar St. Clements da ke kasar Australia a shekarun 1998-1999 a inda ya samu shaidar Digiri na biyu a bangaren Kasuwanci, daga nan ya sake komawa Jami'ar Tafawa Balewa dake Bauchi domin cigaba da karatunsa a inda ya sake samun shaidar wani Digirinsa na biyu a kan kasuwanci na komai da ruwanka wato ( General) a shekara ta 2000-2001. Mai Girma Galadima Usman Abdul'aziz ya yiwa kasa hidima a Jihar Binuwai. daga shekara ta 1981zuwa1982 (Taskar Suleiman Ginsau)



"RAYUWARSA TA AIKI"

Bangaran Rayuwarsa ta aiki kuwa abin abin sha'awa da ban mamaki Mai Girma Galadiman Hadejia Alh. Usman Abdu'aziz ya fara aiki ne a ma'aikatar Ciniki da masana'antu ta tsohuwar Jihar Kano a shekara ta 1982, a matsayin jami'i mai kula da bangaren ciniki.

"AIKIN GALADIMA A KAMFANIN TOTAL"

Daga nan ya kama aiki da Kamfanin Mai na Total a matsayin wakili mai kula da harkokin kasuwanci a watan Augusta na shekarar 1983, bayan samun horo da yayi a Hedikwatar Kamfanin da ke birnin Lagos, daga nan an yi masa canjin aiki zuwa Jihar Kano a matsayin jami'i mai kula da harkokin kasuwanci.

Bayan dawowarsa Kano ansake yi masa canjin aiki zuwa Jihar Barno a shekarata 1988 a matsayin wakilin harkokin kasuwanci mai kula da shiyyar Arewa maso Gabas na Kamfanin Mai na Total. Kasancewarsa a wannan shiyya ya bada gagarumar gudunmawa wajen cigaban wannan Kamfani, hakan ne ya sanya aka sake yi masa canjin aiki zuwa sabon ofishin da aka bude na Kamfanin a Jos, hedkwatar Jihar Filato a matsayin Manaja mai kula sha'anin kasuwanci, zamansa a Jos ya gudanar da ayyukan da suka kai Kamfanin ga samun nasara, a inda aka daga darajarsa a wannan shiyya, hakan ta sa aka kara ciyad dashi gaba aka bashi Manajan kula da kasuwanci a shiyyar Arewa maso Gabas, a shekara ta 1996. A lokacin da yake gudanar da ayyukansa a wannan shiyya a Jos bayan ci gaban da na bayyana mai dorewa ya samar ta fuskar habaka kasuwancin Kamfanin. Lallai Galadima ya tabbatar wa Duniya cewa shi tsayayye ne wanda yasan harkokin kasuwanci bisa gaskiya da rikon amana.

Har ila yau kwarewarsa ce ta sa aka sake karama masa mukami zuwa Manajan yanki wanda ya kunshi Jahohi kamar su:-
1. Bauchi
2. Gombe
3. Barno
4. Yobe
5. Adamawa
6. Taraba
7. Filato
8. Nasarawa
9. Binuwai
10. Kogi
shedikwatar tana nan a matsayinta a Jos. 



A shekara ta 2001 lokacin da Kamfanin Mai na Total da na ELF suka hade an sami canje-canje inda aka kirkiro sabon Ofis mai kula da Arewa mai nisa dake da shedikwata a Kano, tare da nada Galadima a matsayin Manajan shiyya mai kula da Jihohin da suka yi iyaka da kasashen Republic of Benin, Niger, Chad da Cameroon kamar haka:-
1. Kebbi
2. Sakkwato
3. Zamfara
4. Katsina
5. Kano
6. Jigawa
7. Yobe
8. Barno
9. Adamawa
A shekarar 2006 an kuma yi masa canjin aiki zuwa birnin Benin a matsayin Manaja mai kula da shiyyar yamma ta tsskiya. Kamfanin Total ya kirkiro Ofishin kasuwancin Najeriya a Abuja wanda aka bawa Galadima Manajan wannan Ofis mai kula da shi a shekara ta 2008. (Taskar Suleiman Ginsau)

"AIKIN GALADIMA A KAMFANIN MAI NA NNPC"

Dangane da irin gagarumar gudun mawa da jajircewar sane tasa, daga bisani aka yi masa canjin aiki zuwa Kamfanin NNPC a shekara ta 2012 lokacin da Kamfanin na NNPC ya nemi Kamfanin Total da ya basu shi don ya taimaka wajen canja akalar tafiyadda kamfanin NNPC Retail yadda zai yi daidai da sauran manyan kamfanonin mai na kasuwanci irin su TOTAL.

A yayin zamansa a Kamfanin NNPC na kasa ya samar da ci gaba ta fuskar samar da kudaden shiga masu tarin yawa, ya samu nasarar bude kananan gidajen Mai shiryawa tare tabbatar da tsaftace kasafin kudaden Kamfanin, Galadima ya samar da ci gaban Kamfanin NNPC Retail tare da inganta harkokin kasuwanci a matsayin Janar Manaja mai kula da saye da kasuwanci a karkashin NNPC Retail Ltd, a Abuja cikin watan Maris na 2012.

Haka kuma Kamfanin NNPC ya sake ba shi mukami Janar Manaja mai kula da tsare-tsare da dabarun aiki cikin watan Maris na 2013 a dai karkashin NNPC Retail Ltd.

"A JIYE AIKIN GALADIMA"

Alhamdulillah mai Girma Galadima ya yi aikinsa cikin koshin lafiya tare rikon amana da gaskiya wanda hakan ya bashi damar ajiye aikinsa cikin walwala da jindadin, Galadima ya ajiye aiki don kashin kansa a shekara ta 2014, inda ya kafa Kamfaninsa mai suna ENCEE BUSINESS SERVICES, wanda yake gudanar da shawarwari da horo kan yadda za'a bunkasa harkokin kasuwanci Mai da Iskar Gas...

Galadima yana da matan Aure guda biyu da 'ya'ya Goma... Ina mai addu'a agareshi Allah ya tayashi riko, Allah ya daukaka wannan Masarauta ta Hadejia.

Tsarawa
ISMAILA A SABO


Mai Nazari
SULEIMAN GINSAU
Association Of Nigerian Authors (ANA)

Monday, October 3, 2016

TSARIN ZAMAN JAMA'A DA TATTALIN ARZIKI A KASAR HADEJIYA KAFIN ZUWAN TURAWAN MULKIN MALLAKA. (Kashi na 1). Daga Suleiman Ginsau...









Kasar Hadejiya tana da kabilu daban daban, amma duk da haka wannan masarauta a cure take a waje daya. Addinin Musulunci shi ne ya dada hada su da kuma harshen Hausa wadda suke magana da shi a matsayin harshen kasa. Babu wata tababa cewa Addinin Musulunci shine Addinin da mafi yawan jama'a suke bi a wannan masarautar ta Hadejiya. Ka'idoji da dokoki da hukunce-hukuncen Musulunci su ne suke tafiyar da rayuwa da ayyukan mutanen wannan kasa. Addinin Musulunci ya hada kan jama'a kuma ya samar da hanya madaidaiciya ta zaman al-umma. Ta hakane Musulmi masu rinjaye da wadanda ba Musulmi ba marasa rinjaye mazauna kasar Hadejiya kafin mulkin mallaka suna ganin sarkin Hadejiya nada mutukar kima kuma shugaba ne babba duk da yake suna da hakimai da dagatai wadda suke jagorancinsu, Mutanen Hadejiya sukan hadu a kowace shekara su gudanar da bukukuwan Sallah karama da Sallah babba a Hadejiya.

Ta haka al'ummar Hadejiya take cudanya da juna cikin walwala, farin cikin, nishadi, jindadi da annashuwa da sakin fuska. Kuma bisa dukkan alamu, kabilun da suke zaune a Hadejiya sun shiga juna, za'a taras bisa asali, Bahaushe, Bababbare ne, ko Bamange, ko babade, ko kuma bafulatani. Haka dai kabilun kasar Hadejiya suka sarki juna.

Jama'ar da ba Musulmi ba suna karkashin kariya ta wannan masarauta, amma su kuma suna bayar da jizya. Al'adun Hausawa/Fulani Hadejiya suna da babban tasiri na mutanen Gabas wato al'adun Barebari. Akwai misali da yawa da za a iya bayarwa a kan haka, kauki misalin sunayen wasu mukaman sarautu kamar Zangoma da Bulama da Kacallah da Maina (dan Sarki) duka daga wajen Barebari a ka samo su.

Hatta ma bikin Sallar maulidi ana gudanar da shi ne dai-dai yadda Barebari suke yi. Ashe ke nan al'adun Barebari sun yi tasiri. (Sulaiman Ginsau )
Kari a kan wadanan kyawawan huldodi na mutanen Hadejiya a tsakanin junansu, tsarin da masarautar ta bi wajen tafiyar da al'amuranta na mulki ya dada kara wannan dankon zuminci. Tun daga farkon kafuwar daular, Sarkin Hadejiya Malam Sambo ya dora kowace kabila daga cikin kabilun kasar a kan wani mukami na sarauta. Wannan tsari da aka ci gaba da aiwatar da shi, ya sanya jama'ar kasar sun zauna a dunkule tamkar tsintsiya domin kowace kabila ta san tana da wakilci a majalissar wannan masarauta.


Ta fuskar tattalin arzikin kasa kuwa, Hadejiya tana da yalwataccen arziki tare da sana'o'i da masana'antu iri-iri, duk da yake harkokin noma sunfi daukar kaso mai yawa. Magidanci shi ne tushen arziki a tsarin zaman jama'a tare da iyalansa a matysayin masu taimakawa. Talakawa sun tsayu sosai wajen yin noma na lokacin damina da noman fadamu a lokacin rani, sannan kuma kamun kifi da kiwo sun zama ruwan dare a tsakanin mazauna kasar Hadejiya. Amfanin gonar da aka fi nomawa sun hada da:-
1. Gero
2. Dawa
3. Shinkafa
4. Wake
5. Masara
6. Gyada
7. Auduga
8. Alkama
9. Ridi da Kankana
10. Rake da sauran kayan lambu kamarsu Timatir da Tatttasai da Taruhu da Rake da sauran kayan lanbu ana noma su ne ta hanyar noman fadama a lokacin rani. Kasar Hadejiya, kamar sauran kasashen wannan nahiya, tana da kyakkyawar kasar noma Gero da Kiwon Dabbobi. Har wa yau kuma wannan yanayin wuri ne mai albarka ya ba da damar aiwatar da wasu sana'o'I kamar su Rini da Saka da Kira da Ginin Tukwane da Jima da Dukanci da Gini da sauransu.


A bangaren saka kuwa kauyen Bangelu wanda yake tsakanin Auyo da Hadejiya ya shahara sosai wajen saka da dinka Rigar Bullamai tare da sauran Rigunan Saki Fari masu inganci. Haka kuma kauyen Hadejia ya yayi suna a sana'ar Rini. Mutanen Hadejiya da suke zaune a daura da kogin Hadejiya sunyi fice a sana'ar Su ta kamun kifi. Haka kuma dajin Hadejiya cike yake da kudan zuma inda ake samun zuma mai tarin yawa. Diban zuma ya zama wata sana'a mai riba ga jama'ar kasar Hadejiya musamman yadda take tallafawa wajen warware matsalolin rayuwar yau da kullum.

Bugu da kari mutanen Hadejiya kamar sauran wurare, sukan sayar da amfanin gona wanda ya yi rara, ta haka suka shiga hada-hadar kasuwancin amfanin gona daga cikin hanyoyin da suka kara habaka Tattalin Arzikin Kasar Hadejiya kafin zuwan turawan mulkin mallaka. Ta wannan hanya masarautar Hadejiya ta zama wata cibiya kuma muhimmiyar mahada ta cinikin kayan amfanin yau da kullum a gabacin kasar Hausa a karni na sha tara (K19). Masarautar ta yi fice wajen fitar da kayayyakin abinci kamar Alkama da Kifi zuwa Kano da wasu wurare, ita kuma sai ta sayo Goro da makamancin abubuwan da masarautar take da bukata. Kamar yadda aka fada a baya, mutanen Hadejiya na kasuwancin Rigunan Saki ko Rigunan Fari da Zuma da Kiraga wato (Fatu) da Shanu, su kuma su sayo Gishiri da Dawakai da Kanwa. Ana kuma jin cewa Hadejiya ta zama wata hanya ta fatauci na fataken da suke ratso Sahara zuwa Kano ta yamma da kuma Barebari da Larabawan Fezzan da Azbinawa da Buzaye daga gabas da kuma yamma. Wadannan fataken sukan hadu a kasuwar Hadejiya su gudanar da harkokin cinikayyarsu na kayayyaki kamar Rigunan kano da kanwa da Shanu da Bayi da kayan Yaji (Sulaiman Ginsau).

A wannan lokacin da ake Magana, a Hadejiya akwai manyan kasuwanni guda biyu (2) daya kasuwar an yi ta a wajen ganuwa, an kakkafa rumfunan da kuma masaukai na baki wadanda aka yi don samar da wuraran zama da jin dadin fatake da sauran yan kasuwa. A cikin ganuwa ta birnin Hadejiya akwai wata kasuwa wadda take kula da bukatun mazauna birnin Hadejiya da makwabtanta. Wannan ya nuna cewa bayan kasancewar Hadejiya cibiyar mulkin da ayyukan jin dadi jama'a, haka kuma tana matsayin ingantacciyar cibiya ta kasuwanci. Wannan kasuwa tana karkashin kulawar Zangoma wato Sarkin kasuwa. Zangoma shi ne yake karbar dukkan haraji na wannan kasuwa tare da masu taimka masa.
A dunkule, wannan yayi bayanin Hadejiya a matsayin masarauta ta mulkin jihadi da kuma fito da tsarin zaman jama'arta da tattalin arzikinta kafin mulkin mallaka na turawan ingilashi a kan daular Usmaniyya ta Sakkwato.

An kuma nuna cewa a fanning Siya sa, Hadejiya gari ne na 'yan Boko da 'yan siya sa masu yawan gaske kuma Hadejiya garine na kasuwanci wadda hakan ya sa mutane suna zuwa siyan kayayyaki daga gurare daban-daban, sannan masarautace mai karfi a tsakanin masarautun da suke gabacin kasar Hausa, musamman yadda take tsoma baki a harkokin cikin gida na makwabtan ta.

Haka kuma nayi wai-waye ta fuskar tsaro ya bayyana cewa Hadejiya kasace jaruma kuma karshen karni na sha tara (K19) sai ta zama kasa mai kyakkawar huldar dangantaka da zama na lumana da abokan taka da sauran masarautu. (Sulaiman Ginsau)

Muhadu a kashi na biyu 2

Friday, August 12, 2016

SARKIN HAƊEJIA ABUBAKAR MAJE HARUNA (1984-2002).



Bayan rasuwar Sarkin Haɗejiya Alhaji Haruna sai aka naɗa Ɗansa Alhaji Abubakar Maje Haruna a matsayin Sarkin Haɗejiya na goma sha biyar (15), A jerin sarakunan Fulani, an naɗashi ranar Juma'a 31st/august/1984. Sai akayi Sarki mai farin jini da hakuri da son mutane, a wajen kyauta kuwa ya kasance mai Alheri tun yana ƙaraminsa. Sarkin Haɗejiya Abubakar kafin zamansa sarki yayi Ayyuka da dama, sannan ya kasance Ɗan kasuwa.

A zamaninsa an samu sauye sauye da dama a ƙasar Haɗejiya, musamman Ɓangaren Ilmin Addini dana zamani Kasuwanci da siyasa. Sarkin Haɗejiya Abubakar Maje ya halarci makarantu da dama inda ya fara halartar makarantar Elementary dake Unguwar Dallah a shekarar 1945, sannan ya tafi makarantar Middle School dake Unguwar fantai a shekarar 1949 zuwa 1952. Haɗejia A yau.

Sarkin Haɗejiya Abubakar ya tafi makarantar T.T.C. Maru dake a Lardin Sokoto a wancan lokacin, ya fara a cikin shekarar 1953 zuwa 1956. Sarkin Haɗejia Abubakar ya koma makarantar horar da ma’aikata dake Potiskum ta jihar Borno, wadda yanzu take a jihar Yobe. Kuma ya fara aikin gwamnati a matsayin Malamin Hakimi a Gundumar Bulangu, sannan ya riƙe muƙamin Magatakarda a majalissar Sarki. Saboda iya mu’amala da son jama’a sai yazama duk inda ka ganshi bazaka ganshi shi kaɗai ba sai da jama’a, hakan ya bashi nasarar gogewa wajen tafiyar da shugabancin jama’a. Haɗejia A yau.

A zamaninsa an samu ci gaba da yawa a ƙasar Haɗejia ta kowane fanni na rayuwa, musamman zaman lafiya da Kwanciyar hankali, sannan an samu bunƙasar garin Haɗejia wajen gine ginen zamani da gina sabin Unguwanni. A zamaninsa aka rushe ƙofar Garin Yamma da ta Arewa aka Gina sabi domin dacewa da zamani sannan aka sake gina Sabi guda uku, an gina ɗaya a Kusa da Kadime ɗaya kuma an ginata a hanyar Gumel da kuma hanyar Nguru. A zamaninsa an gina sha tale-tale (Round about) guda biyu ɗaya a yamma da kofar garin yamma, ɗaya kuma a Titin Tashar mota tsohuwa, sannan anyi sababbin hanyoyin mota a ciki da wajen Haɗejia. A zamaninsa....... Hadejia A yau! A duba littafin Fulani da mulkinsu na Ismaila A Sabo.
posted from Bloggeroid

Saturday, July 30, 2016

HADEJIA TOWN WALL AND GATES...

HADEJIA A YAU!BY: SULEIMAN GINSAU


HADEJIA TOWN WALLS AND GATES
"Hadejia was a large town with 5 town gates and excellent walls about 30ft (9. 14m) high, and 30ft(9. 14m) thick " ... (Captain Philips 1909) Hadejia Town walls had a long history dating back to the pre-jihad period. The walls were built to provide security to the people, and to serve as fortification against external invasion. Though mostly in ruins now, with a great proportion having completely disappeared, the walls were
intact up to the time of the colonial invasion in 1906.The construction of the walls was done by direct labour using local building materials. Over the years, the walls have been taken subjected to
several phases of development. 

Expansions and reinforcements were made to accommodate a growing population or to enhance security against attack by powerful enemies. The walls were invariably complimented by gates whose history could be linked to that of the walls. The gates provided the only entry points into the town. They
were made extremely strong, thus making it very difficult for an enemy force to break into the town through them. The gates were manned by
gate-keepers or porters (sarakunan kofa)
appointed by the Emir. These keepers used to close the gates everyday from dusk to dawn, thus controlling the movement of people in and out of the town during these periods. Visitors or
strangers were not allowed in unless with the express permission of the Emir. It was reported that one Emir ordered the gates to be left open permanently, confident that no enemy force would dare attack the town.

The first town wall in Hadejia was believed to have been built during the pre-jihad period. Though the exact date of its construction cannot be determined due to lack of proper records, its
perimeter is marked by certain well-known local pits: Mai kilabo in the west, Atafi in the south, and Dallah in the East.

 It was said to be one mile in circumference, and had four gates. The second wall was built by Sarki Sambo in the early years of the Jihad. It was wider than the previous wall,
with its perimeter approximately put at 2 miles 170 yards. It had 5 gates. The present wall, which was the third, was also built during Sambo's reign. It was built at a time when Hadejia was at
the centre of a bitter rivalry between Sokoto caliphate and Borno Empire. As such it was much stronger and wider than the previous walls. An extension to this wall was later made on the
Eastern side during the reign of Sarki Haruna (1865 -1885), encompassing a large space to harbor fugitives from surrounding villages in times of war. The Habe settlement of Fantai, which hitherto was outside the wall, also became sheltered in the new extension. This brought the wall to its present size of 4 miles 135 yards, with 5 gates, namely:
Kofar Gabas (also known as Kofar Gwani),  Kofar Arewa, KofarYamma
Kofar Kyalesu (also Known as Kofar Kogi), Kofar Mandara (also known as Kofar Talata). Apart from the Kofar Mandara gate, which was destroyed by the British in their attempt to gain
entry into Hadejia town in 1906, the other gates are still standing in their original positions. They have, however, undergone several modifications
over the years, the latest being in1985 which saw the total re-construction of Kofar Arewa and Kofar Yamma. The Hadejia town gates now stand as
historical monuments rather than as security outposts.
BY: SULEIMAN GINSAU

Friday, July 29, 2016

A SHORT HISTORY OF GARUN-GABAS.. (BIRAM)


Garun-gabas generally recognised as the ancient Biram, i believe and Bagdaza to be Baghdad. The legend in another form is connected with that of the Origin of the Hausa Bakwai. Mukhtar or Bayajidda was compelled to flee Bornu with his wife, on his Journey west he left her on the road and she gave birth to Biram who founded Garun-gabas. Bayajidda continued his journey to Daura where the well known encounter with the Snake took place and Bayajidda's marriage with the Queen Daurama.

The Town was founded by Arabs from Baghdad, one Mukhtar and his younger brother Biram migrated West and came to Birnin Bornu (Kukawa). The Shehu of Kukawa gave Mukhtar his daughter in marriage and the town of Kulunfardu where he lived until his death. Biram and his younger brother then migrated further West and founded Garun-gabas.

The following is a list of Chiefs of Garun-gabas.
1. BIRAM

2.BOMI... One of the Biram's follower who came with him from Kulunfardu but no relation.

3. TUNKU... Also one of the Biram's followers. The length of time for which these three held the Sarauta unknown.

4. ABDULLAHI. Called Ajab... He ruled for three days and then miraculously disappeared.

5. ASAWA... Thirty years the grandfather of the present Sarkin Gabas, he was deposed by Sambo Diginsa the first Fulani Emir of Hadejia, on account of his son was murdered.

6. MUSA... Nephew of Asawa Eleven years, appointed by Sambo.

7. GAUYAMA... Not of the ruling family fourty years, half way through his reign he became blind.

8. BARWAI... Younger brother of Sambo, Nine years.

9. USMAN... Son of Barwai, Six years he then Emigrated to Shira.

10. GABDO... One year and Emigrated to Katagum. Hadejia A yau.

11. BURMI... A fulani, one year fled to Katagum in terror of Buhari.

12. SARKIYO... One of the Buhari's "Hakimi" Ten years, Buhari then died and was succeeded by Umaru who remove Sarkiyo to Hadejia and made him Barwa.

13. MUHAMMAD BAKO... Son of Asawa and thus descendent to the Original Arab founders, Appointed by Haru Bubba. He held the Sarauta for Two years and then went to Mecca.

14.MUHAMMAD DARINGI... A fulani, seven month deposed by the Emir. By Ismaila A Sabo.

15. TUKUR... Son of Gauyama, after five years of his rule Muhammad Bako returned from Mecca, but leave as a private individual. Muhammad Tukur ruled for another five years and was then deposed by Haru for shaving his wife's head.

16. KANKARAU... A fulani appointed by Haru, but deposed after seven month. Muhammad Tukur Was then reinstalled and rule for seven years when he became blind and was deposed. KANKARAU reinstated but after seven years was again deposed by the Emir Muhammadu for having married seven wives.

The Emir then called in all the man of Garun-gabas to choose their own Chief. They unanimously choose Abubakar son of Muhammad Bako a direct descendant of the original Arab founders. Abubakar at first however persistently refused to accept the honour and on being pressed for a reason, told the Emir that as an Arab who had been to Mecca he could not countenance the perversion of the prophet's laws which was rife in Hadejia. The Emir is then stated to have admitted the Truth of this and on condition that he would take the Sarauta to have promised that he should administer according to the true Law at any rate in Garun-gabas.

Abubakar then became Chief and has been Sarkin Gabas for twenty three years to the present day. The famine in common with other Hadejia District, the famine last year was the cause of considerable mortality chiefly among the children. Hadejia A yau.

Reference--- Assessment reports by K. L. Hall, Assistant District officer Hadejia District Kano Province.14th/July/1915.

Friday, July 15, 2016

SIR AHMADU BELLO'S CHRISTMAS MESSEGE IN 1959...


“We are people of many different races, tribes and religions, who are knit together by common history, common interests and common ideals. Our diversity may be great but the things that unite us are stronger than the things that divide us. On an occasion like this, I always remind people about our firmly rooted policy on religious tolerance. Families of all creeds and colour can rely on these assurances. We have no intention of favouring one religion at the expense of another. Subject to overriding need to preserve law and order, it is our determination that everyone should have absolute liberty to practise his beliefs.

It is befitting on this momentous day, on behalf of my ministers and myself, to send a special word of gratitude to all Christian missions. Let me conclude this with a personal message. I extend my greetings to all our people who are christians on this great feast day. Let us forget the difference in our religion and remember the common brotherhood before God, by dedicating ourselves afresh to the great tasks which lie before us.”

Monday, July 4, 2016

AL'ADUN KASAR HADEJIA... Kashi na Daya (1)



WASU DAGA CIKIN AL’ADUNMU KYAWAWA…
Kasar Hadejia mutanen cikinta suna da Al’adunsu kyawawa wadda suka dace da koyarwar Addinin musulunci, wadannan Al’adu saboda kyawunsu yasa mun taso a cikin kyakkyawan tsari da taimakon Junanmu. Shekaru da dama da suka gabata zakaga mutumin Hadejia bubba da yaro yana da Tarbiyyar idan yaga bubban mutum ya gaidashi, kokuma idan yaganshi da kaya a hannu yaje ya karveshi, wannan Al’ada tana da kyau kuma tayi daidai da tsarin Addinin musulunci. Sannan a shekarun baya duk Unguwar da kaje zakaga tsarin zamantakewarsu akwai ban sha’awa, domin wurin zaman manya daban na yara daban sannan idan zaka wuce Bubban mutum yana zaune zaka cire Takalmi sai ka wuce sannan ka saka. Wani abin ban sha’awa shine Lokacin cin Abinci babu yadda zakaga mutum yaci abinci shi kadai ai haduwa ake mutum huxu ko biyar ake ci tare domin neman Albarka. Wannan ya nuna akwai son juna a tsakaninmu, domin wadda Allah bai bashi ikon yin abinci a gidansa ba to bazai wuni da yunwa ba domin idan yazo Dandali zaici tare da ‘yan-uwansa. Haka yara matasa suma kowa yakan dauko abinci daga gidansu a fito a hadu a ci, wannan muke kira da suna Ciyayya.

ZAMANTAKEWA…
Zamantakewa wata kalma ce da take nuni ga yanayin yadda mutum yake rayuwarsa tare da Abokan zamansa wadda Allah ya hadasu, walau a zaman Makwaftaka ko sana’a da sauransu.

TSARIN SHUGABANCHI…
Shugabanci yana nufin rikon on ragamar Al’umma da basu Umarni da kuma yi musu Jagoranci bisa tafarkin da suka aminta dashi, sannan da tsara musu Dokoki da sasanta tsakaninsu. A Kasar Hadejia tsarin shugabanci ya faro ne tun daga cikin gida inda mutum a gidansa shine shugaba mai shirya komai da kuma bada Doka da Oda, sannan sai shugabancin Unguwa wadda ya kasance kowace Unguwa tana da nata shugaban mai sawa da hanawa da bada umarni shine muke kiransa da suna Mai-unguwa. Duk wani umarni yana fitowa ne daga bakin Mai-unguwa kamar hani da kuma sawa. Shi wannan Mai-unguwa duk abinda ya shafi Unguwarsa shine keda iko akai, kamar Umarni, hani, sasanto tsakanin mutane. Kuma duk Bakon da yazo wannan Unguwa akan kaishi gidan Mai-unguwa ne domin shike da Alhakin yaji abinda ke tafe dashi idan mazauni ne shine da hakkin bashi masauki ta haka ake tsaftace Nagari da Mugu a cikin Unguwa. Baya da Mai-unguwa a gari akwai Malami wadda idan wani Bakon malami yazo wurin Wannan malamin za’a kaishi shi zai bashi masauki sannan yaji Dalilin abinda ke tafe dashi. Haka kuma Idan Bakon dan kasuwa ne akan kaishi Gidan Zangoma wadda shine da hakkin saukar Baki musammam masu saye da sayarwa, shi zangoma shine zai tambayeshi irin Hajojin da yake sayarwa kokuma yake saye domin ya sadashi da masu ciniki. Kaga duk wannan yana nuna muna da kyakkyawan tsari na zamantakewa wadda duk mutumin da ya shigo kasar Hadejia ansan Dalilin zuwansa da kuma abinda yazo yi. A duk lokacin da aka samu hakan shi Mai-unguwa shike da Alhakin sanarwa Bulama sannan Bulama ya sanarda Hakiminsa, shi kuma Hakimi zai sanarda Majalissar Sarki.

Wannan tsarin shugabanci shi ake amfani dashi a kasar Hadejia har lokacin zuwan Turawan Mulkin Mallaka. Koda yake Turawa ma da sukazo sai suka lura cewa muna da kyakkyawan tsari na shugabanci, dan haka sai suka nemi Hadin kan Sarakunanmu ya zamanto zasu bada Umarni ne ga Sarakuna sannan Sarakuna su bada Umarni ga Talakawansu. Turawa sunzo sun samemu da Al’adunmu kyawawa sannan muna da tsari na shugabanci kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada mana, wannan dalili yasa Turawa suka samu damar Mulkarmu ba tare da sunsha wahala ba.

Sunday, February 21, 2016

MARIGAYI ALHAJI ADAMU KWANO HADEJIA.....


Daga Mallam Muhammad Rabakaya...

A madadin al'ummar Hadejia da gaba dayan masarautar Hadejia muna addu'a da alhinin Marigayi Alhaji Adamu Kwano (kwano baka karaya) Allah ka gafartawa wannan bawa naka, ka yafe masa kura kurensa da iyayenmu Allah ta'ala kasa aljannah madaukakiya ce makomarsu. Alhaji Adamu Kwano miliyoyin mutane sunyi tarayya da 'ya'yansa wajen gadon dukiyar da Allah ya mallaka masa Allah ka hada mu a Aljannah. zaka\ki so ka\kiji dalili -biyoni..................

Duk wadda ya baka Ilmi ko yayi ma hanyar samun Ilmi ya gama maka alfarma kuma kaci gado daga cikin gadonsa tare da 'ya'yansa. Marigayi Alhaji Adamu Kwano Hadejia Tun kafin a haifeni wannan bawan Allah yana da gida babba mai kallon gidanmu (Gida na a yanzu) Rahama chemist a yanzu ya gina yayi fasalin ajujuwa na Kasa da rufin kwano ya maidashi makarantar  Islamiyya (islamiyyar farko a garin Hadejia), ya tafi kano ya samo Marigayi Malam Aminu Yusuf da Malam Alhaji da Malam Sabo na Madabo da Malam Nasiru Ahli da Malam Rufa'i Kafin Hausa  kuma a matsayin Headmaster da malamai, kuma yabasu mahalli a wancan lokacin mun samu tabbaci daga matar daya daga cikinsu cewa daga gidansa ake dauko musu abinci. Aka saka yara maza da mata aka fara koyarda su darussan addini a tsarin zamani (formal education) mai Allo da Alli.


Daga nan abu ya kara fadada, yasa kudinsa ya cike wani rami mai tarihi wato RAMIN MALAM HUDU inda ya gina ajujuwa na siminti akan ramin da staffroom islamiyya ta koma can ya kara malamai, lokacin duk babu islamiyya sai ita Hudu islamiyya prim. sch. mai tsohon tarihi daga nan gwabnati ta shigo ta taimaka masa da karin Malamai da tsare tsare, Amma gini da gudanarwa nasane.
Bai tsaya nan ba tashinsa zuwa Asibiti inda yake aiki, ya sayi fili anan farin gida ta yanzu ya kara Gina wasu ajujuwan islamiyya ya bude makarantar Islamiyya Garko, duk a lokacin babu Islamiyya sai dai makarantun mu na zaure da na allo, daga nan ya kara fadada niyyarsa da burinsa na habaka ilmin addini a Hadejia ya raba Islamiyya Garko ya Kirkiri Karamar sakandare Islamiyya yasa mata sunan Headmaster na makarantarsa ta farko wato Malam Aminu Yusuf. Ya sake samo wani mutumin Sudan Sheik Ali Fu'ad a matsayin principal inda ya dauka mata malamai itace Aminu Yusuf Junior Islamiyya sec. sch. Hadejia. Wadda daga baya gwabnati ta bashi wani bangare a cikin Buhari primary school Hadejia ta tashi daga Garko ta koma can inda takoma hannun gwamnati kachokam bayan Allah ya masa rasuwa, wannan makaranta yanzu itace babbar sakandaren Islamiyya ta jeka ka dawo ta mata da maza a garin Hadejia.

Daga wancan lokacin zuwa yanzu mutum nawa aka raya? mutum nawa su kuma nawa suka raya da Ilmi? Kuma Bayansa tayi kyau, yana da 'ya'ya da jikoki da sukayi karatun Addini da Boko a fannoni da dama, da wadda yayi digirin farko tun 1977 har zuwa yau agida da kasar waje, sannan kafin yabar aiki yana daya daga cikin wadanda Gen. Olusegun Obasanjo ya baiwa lambar yabo yana shugaban Kasa a shekarar 1977.

Da fatan zamuyi koyi da irinsu a duk bangarorin rayuwa.
posted from Bloggeroid

Friday, February 19, 2016

TARIHIN HADEJIA.



Takaitaccen Tarihin masarautar Hadejia.


Masarautar Hadejia dadaddiyar Masarauta ce wadda ta kafu shekaru aru aru da suka gabata, daga lokacin kafuwarta kawo yanzu masarautar tayi fice da yin suna bisa ga muhimman tarihi da take dashi. Masarautar Hadejia tana daga cikin masarautu da sarakunan HABE suka mulka kafin Jihadin Shehu Usmanu Danfodiyo, kuma tana daga cikin masarautun da ake kira Hausa Bakwai. Masarautar tana daga cikin Masarautu da suke karkashin Daular Usmaniyya, daga Gabas tayi iyaka da Tsohuwar Daular Borno daga yamma tayi iyaka da Masarautar Kano, daga Kudu kuma tayi iyaka da Masarautar Katagum sannan daga Arewa tayi iyaka da Masarautar Gumel. Birnin masarautar yana cikin garin Hadejia dake Arewa maso gabashin Jigawa a Arewacin Nigeria, sunan garin ya samo asali ne daga wani Maharbi wadda shine ya kafa garin wato HADE, da kuma Matarsa JIA. Sunayen wadannan mutane shi aka hada ya zama HADEJIA, domin a lokacin mutanen wasu garuruwa in zasu zo sukan ce mun tafi garin Haden jiya, wato ana masa Lakabi da sunan Matarsa. Saboda takaita kalma ta Hausawa shine yasa aka hade sunan ya zama Hadejia. 

Masarautar Hadejia tana da fadin kasa wadda ta kai Murabba’in kilo mita dubu shida da dari tara da sittin da uku(6963), wannan yanki yana da shimfidaddiyar kasa mai kyau wadda ake kwatanta yanayinta da na kasar Chadi, kuma tana da Jigayi masu tarin yashi da kuma kwari mai tabo da laka amma bada da tsaunuka ko Duwatsu. Kasar Hadejia tana da Kogi wadda ya kasance akwai ruwa kowane lokaci, sannan tana da fadamu masu yawa wadanda suke kafewa lokaci zuwa lokaci.

Kogin kasar Hadejia ya taso ne daga Kudancin Katsina ta Arewa da Zaria sannan ya nufi Arewa maso gabas ya shigo ta Kasar Kano ya ratsa kasar Hadejia, sannan ya nufi Tafkin Chadi. Wannan Kogi ya ratsa ne ta Kudancin Hadejia da Gabashinta, wannan bangare ne da yake samarda ruwan sha da kamun kifi da kuma aiwatar da Noman rani. A lokacin damina kogin yakan cika inda yake samarda kananan fadamu a sassa daban daban wadda ake amfani dasu a wajen noman lambu. A bangaren Noma Masarautar Hadejia tana gabatarda noma a lokuta biyu wato Rani da Damina, inda masana yanayin kasa suka tabbatar cewa duk abinda aka shuka a wannan kasar zai fito yayi kyau saboda yanayin kyawun kasar. 

A bangaren kasuwanci kasar Hadejia ta shahara wajen saye da sayarwa tun kafin Jihadi, domin ta zama wata mahadar kasuwanci ce tsakanin Daular sokoto da Daular Borno. Mutanen Masarautar suna da sana’oinsu da dama kama daga sana’ar hannu zuwa Fatauchi da sauransu. Kasar Hadejia tana da kasuwanni da yawa wadanda suke ci a dukkanin sati sannan da masu ci a kowacce rana.

Masarautar Hadejia tana da Kabilu da yawa wadanda suke yarensu da Al’adunsu sun banbanta kuma suna zaune a yankuna daban daban na kasar, Kabilun kuwa sun kunshi Hausawa, Fulani, mangawa, Ngizmawa, koyamawa, Baddawa, da sauransu. Wadannan Kabilu kowanne da irin yarensa da kuma Al’adarsa da irin tsarin zamantakewarsu, sai dai duka suna bin Tafarkin Addinin Musulunci ne tun bayan Jihadin Shehu Usman Danfodiyo.

posted from Bloggeroid