"" /> HADEJIA A YAU!: Mar 5, 2013

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, March 5, 2013

WA YA KAMATA YA TSAYA A BAYAN LIMAN?

Hadejia A yau! Assalamu Alaikum! Godiya ta tabbata Ga Allah wanda ya Halicci Mutum da Aljannu dan mu bauta masa.

Tsira da Aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu, wanda Allah ya Aikoshi da Alqur'ani da Salloli guda Biyar (5).

Bayan haka Al-ummar Musulmi Musulunci yana da tsare tsare wanda Idan ka bisu zaka rabauta! Hakika Tsayuwa a bayan Liman a yayinda ake sallah ba na kowa bane na Masana ne! Domin Idan Liman yayi kuskure a sallah sune suka san Irin abinda zasu fada masa dan ya gyara.

Idan wanda baida Ilmi ya tsaya bayan Liman kuma aka samu akasi Liman yayi Kuskure kana tunanin zai iya gyara masa? Bazai iya ba, saidai ya sake batawa.

Manzo (s.a.w.) yana cewa :- An sanya muku Liman dan kuyi koyi dashi, Idan yayi Ruku'i kuyi Ruku'i, Idan yayi Sujudi kuyi sujudi.

Danme zakayi abinda Liman baiyi ba?

ZAN BAKU LABARIN MUJRIMI... Mujrimi wani Balaraben Kauye ne! Yazo Birni kuma Sallah ta Magriba ta kamashi sai yazo yayi Alwala ya tsaya a bayan Liman. Sai akayi Sa'a Liman ya karanto Ayar nan da take cewa:-

Alam Nukhliqil Awwalyn? (Fassara) shin bakuga yadda muka Halakarda Mutanen farko ba? Sai Balaraben kauye ya fice daga sahun farko ya koma sahu na biyu.

Sai Liman ya sake karanta Summa Nutbi'uhumul-Akhiriyn. (fassara) sannan haka muka aikata ga mutanen baya. Sai Balaraben kauye ya koma sahun Karshe.

Sai Liman ya kara karanta Kazalika Naf'alu bil- Mujrimiyn. (fassara) sannan haka Muka aikata ga Mujrimai.

Sai Balaraben kauye ya fita a guje yace Ni ake Nema. Domin yaji an ambaci kamar sunansa. To dan Allah me ya janyo haka? Allah yasa mu Gane.