content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: Feb 22, 2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, February 22, 2012

TARIHIN SARKIN HADEJIA HARU BUBBA

Sarkin Hadeji Haru bubba shine Mahaifin Sarkin Hadejia Muhammadu mai Shahada, wanda a zamaninsa Turawa sukaci Hadejia da yaki. Sarki Haru bubba Malami ne kuma mutum ne mai son zaman lafiya, kuma shine ya gina Masallacin juma'a Na Hadejia. Kuma a zamaninsa Gumel sukayi yaki da Hadejia, wato lokacin sarkin Gumel Abdu jatau. Sarkin Gumel ya aikowa Sarkin Hadejia zai wuce ta kasarsa wato ta kudu a gayawa Talakawa kada su tsorata bazai taba kowa ba. To amma koda yazo wucewa sai ya saba Alkawari don yana sawa ana debe kayan talakawan ana kaiwa Gumel. Koda Sarkin Hadejia ya samu labari sai yasa akayi sirdi aka fita, a wannan yakin aka kashe sarkin Gumel Abdu jatau. Galadiman Hadejia yakuba shine ya sareshi. Dama sarkin Gumel yayi mafarki bazai koma gida ba. Sai ya fadawa kaninsa Abubakar in ya mutu to a kaishi Gumel ayi masa jana'iza, kuma hakan akayi. Kuma a zamanin Sarkin Hadejia Haru ne Dansa Muhammadu Yayi yaki da Maguzawan Mada Rumfa ta Sokoto, inda sarkin musulmi ya masa sarautar Sarkin yakin Sarkin Musulmi. Kafin ya Zama Sarkin Hadejia. Allah yaji kansu.

WAKOKIN MALAM AMADU DAN MATAWALLE HADEJIA!

AMSHI- Hakane malam Amadi na idi ka sake shiri duniya ta Allah ce malam Amadi.


1, Ku saurara jama'a zana baku labarin wani shi hakimi wanda bazai iya saukarmu ba.


2, Akwai wani dan sarki anyi mar sarauta shi buri ya cika, gaba daya ya baza yaran gidansu bubba da yaro duk sun tafi.


3, Naje kasarsu na samu hakimi wani mai siffar mujiya, da fadawa da mutanen gari suna ja mar Allah ya isa.


4, Jemage ba tsuntsu ba yai kamar tsuntsu sai halin tsiya, ga tsuntsu da hakora kamar mutum ni ban gane kanka ba.


5, Agarnana masu kahonnin karo, mai zafin rayi sai kace na karya in taso haihuwa.


6, Wanda tuwo yafi karfinsa in ya samu tuwo shima sai yaci, wannan in aka tuka ka bashi tare da fadawan zasuci.


7, Yautai dan yawon duniya, shi aka baiwa sarauta ya kama mulki bai san girmansa ba.


8, Ungulu komai namanki ne, ya hana 'yan mata dan irin wasan nan da ake dandali.


9, Bera mai ta'adin gayya shi haram da halak ma bai sansu ba.


10, Yautai dan yawon duniya, ya shiga tsuntsaye 'yan uwansa an rasa mai ganewa dashi.


11, Kyawun dan sarki ai a sanshi mai kyauta ga mutanen gari.


12, Shi gogana ai nasuma yake karba yayi chacha dashi.


13, Ai ni in baka ban naka ba, nawa fa shima ba naka ba.


14, Dumau nake ba fashi ko cikin sa'a daya bani da dadin gamo.


15, Bangon dutse in kaki masu sarawa da diga sa gaji.


16, Shaho birkita kaji na sidi malam baka da dadin gamo, bauna wanda ya dosheta babu maduhu sai wani ba tasa ba.


18, Tamat wa bi hamdu ilallahi zan yi ban kwana waka ta cika.



DAGA ISMA'ILA A. SABO HADEJIA.