"" /> HADEJIA A YAU!: 2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Thursday, December 27, 2012

SAKON GODIYA DAGA MAI MARTABA SARKIN HADEJIA.

HADEJIA A YAU! Assalamu alaikum! Bayan gaisuwa irin ta Addinin musulunci tare da fatan Alkairi. Ina meka godiya da ban gajiya zuwa ga Mai girma Gwamnan Jihar Jigawa da Sanatoti da 'yan -Majalissu da Sarakunan Jihar Jigawa da sauran sarakunan Jihohi makwabta, Game da taya murna da akayi ta cika shekaru Goma a Kan Gadon Sarautar Hadejia! Kuma muna meka sakon godiya ga Jami'an tsaro da Mutanen Gari da Al'ummar Masarautar Hadejia sakamakon Hadin kai da suka bada aka gabatarda taro Lafiya. Allah ya saka da Alkairi. Hadejia A yau.
Kuma Muna meka sakon Godiya da ban gajiya ga Hakimai da Dagattai da Masu Unguwanni na wannan Masarauta mai Albarka. Allah ya saka da alkairi.

Muna kara godiya ga 'yan kwamitin wannan taro wadanda suka bada gudunmawa aka Gudanarda wannan taro Lafiya.

Kuma muna kara Addu'ah Allah ya kawo ci Gaba mai Amfani a Masarautar Hadejia! Allah ya tsaremu daga Masifu da fitintinu a kasarmu baki daya. Ameen. Hadejia A yau!

Friday, December 21, 2012

MAI MARTABA SARKIN HADEJIA (alh. Adamu Abubakar Maje) YA CIKA SHEKARU GOMA A GADON SARAUTA

HADEJIA A YAU! Muna farawa da sunan Allah wanda da Ikonsa ne Komai ya Kasance da kuma Abinda zai kasance! Tsira da Aminci su kara tabbata ga Manzo (s.a.w.) wanda Allah ya aikoshi da zance Mafi dadi wato Alqur'ani.

A ranar Asabat 22/december/2012, Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje (c.o.n.) zaiyi bikin cika shekar Goma yana Mulkin kasar Hadejia, A karkashin Daular Usmaniyya.

A ci gaba da kawo Muku Tarihin wadanda suka baiwa Kasar Hadejia Gudunmawa wajen ci Gabanta, yau zamu kawo muku Takaitaccen Tarihin Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje. Hadejia A yau!

An haifi Mai Martaba Sarkin Hadejia a shekarar 15/october/1960, a cikin garin Hadejia. Ya fara Makarantar primary a Abdulkadir pri.school Hadejia a shekarar 1967-1972, sannan Ya shiga Makarantar Secondary a Garin Ikot Ekpene Cross-river a shekarar 1973-1976, sannan ya koma Govt.sec.school Danbatta a shekarar 1976-1979.
Mai Martaba Sarki ya samu Nasarar shiga Makarantar Gaba da Secondary ta school of Rural and social science dake Rano ta jihar kano a shekarar 1981-1982, da kuma 1983-1985.

By Ismaila A sabo

Mai Martaba Sarki ya fara Aikin Gwamnati a tsohuwar Jihar Kano a ministry of social wellfare a shekarar 1982-1988, sannan ya koma Kano state pilgrim wellfare board a shekarar 1988-1991.

Bayan da aka kirkiro Jihar Jigawa Mai Martaba Sarkin Hadejia ya koma Jigawa state pilgrim board a shekarar 1991-1998. Sannan ya koma Ma'aikatar Kananan Hukumomi ta jiha a shekarar 1998-1999 Inda ya rike mukamin senior personnel officer.

A wannan shekarar ne Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya nadashi sarautar IYAN HADEJIA dan majalissar Sarki. Hadejia A yau!
A shekarar 2000-2002, ya rike Mukamin Sakataren Alhazai a Jigawa state pilgrim board.

A ranar Laraba 11/september/2002 Allah yayiwa sarkin Hadejia rasuwa Alh. Abubakar Maje Haruna, sakamakon zaben 'yan majalissar Sarki suka zabi Alh. Adamu Abubakar a Matsayin Sarkin Hadejia Na Goma sha shida (16).

Kuma an Nadashi ranar Asabat 14/september/2002. A karkashin jagorancin Galadiman Hadejia Alh. Habibu Adamu.

A ranar Asabat 23/march/2003, An baiwa Mai martaba Sarki Sanda, a karkashin Jagorancin Gwamnan Jihar Jigawa na wancan Lokacin Alh. Ibrahim Saminu Turaki. Hadejia A yau!

Muna Taya Mai martaba Sarki Murnar cika shekara Goma yana Mulkin Masarautar Hadejia.



Tuesday, December 18, 2012

THE ESTABLISHMENT OF FULANI JIHAD DYNASTY IN HADEJIA (Page one)

HADEJIA A YAU!
In 1808, Sarkin Fulani Umaru, his son and successor Muhammadu Kankiya died. Muhammadu Sambo was appointed as the new Sarkin Fulani of Hadejia. The Fulani leader's In Rinde decide to send a delegation to Sokoto to inform the Shehu of the developments in Hadejia region. Shehu Usman Danfodiyo accept the appointment of Muhammad Sambo as the New Leader of The fulani in Hadejia, condole the people over the death of Umaru and Muhammadu Kankiya, and formally installed Sambo as their new Sarkin Fulani Hadejia. After his formal installation, Muhammadu Sambo decided in 1810 to shift his base from Rinde to Hadejia but before he carried out his plan Habe Ruler of Hadejia Abubakar got the security report of Sambo's intention. Hadejia A yau.

Conscious of the Fulani's military success in the area, Abubakar decided to withdraw from the town without resistence.
Therefore, on the date Sambo decided to occupy Hadejia, on reaching the town, he found the town deserted and so occupied it without any resistance. From that time onwards, Hadejia became the base of the Fulani and eventually the capital of the emirate. An important development that followed the shifting of the Fulani base was the Installation of Sambo as the first Fulani Jihadist Emir of Hadejia in 1810. Thus, Sambo established the first Jihadist dynasty in Hadejia from which sprang all subsquent emirs of Hadejia to date.http://bit.ly/K2WOg4

He also unified all the territories formerly under the Habe administration, under a single central administration to the Emirate of Hadejia. Hadejia A yau!

At the time Sambo moved the Jihadists base from Rinde to Hadejia and formally established the emirate, the structure of the emirate's administration was by far modest andd until mid-century, the capital appeared to have been lesss developed.

At the time of the establishment of the emirate, Muhammadu Sambo relied on a much less formally structured organization and therefore surrounded himself with a relatively small entourage of co-favourite most of whom lacked either titles or fiefs. Therefore, Sambo had to face the difficult task of establishing the apparatus of Centralized administration in his domain. As a firs step towards the establishment of an emirate government, he appointed Yusuf his younger brother as Sarkin Auyo, and his eldest son Muhammadu Garko as Chiroman Hadejia and Makama Lele as the Galadima.
Each of the new title holders was given a specific function to perform in the administration. For example Chiroma, was the crown prince while Galadima was the prime Minister. Sambo's other appointments were those of Madaki (war commander), Ma'aji (Treasurer), Sarkin yari (chief prison supretendant), and Sarkin Wanzamai (chief Barbear). All these state officials were chieftaincy status and performed a specific assignment in the administration. Hadejia A yau!

By Musa Usman Mustapha.

Sunday, December 16, 2012

SABON GWAMNAN KADUNA DA TARIHIN RAYUWAR SA.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music A yau Lahdi Za'a rantsar da Alh. Mukhtar Ramadan yero a matsayin Gwamnan Jihar Kaduna! An haifi Muktar Ramalan Yero a ranar 1 ga Mayun shekarar 1968 a birnin Zazzau. Ya halarci makarantar Firamare ta karamar hukumar wadda ke Unguwar Kaura daga shekarun 1974 zuwa 1980. Ya shiga ta Sakandire dake Ikara daga shekarun 1980 zuwa 1985, sannan ya wuce Cibiyar Koyon Mulki wadda ke karkashin Jami’ar Ahmadu Bello ta Zaria, inda ya samu takardar shaidar digiri na farko da na biyu, wato Masters, a fannin Akanta daga 1986 zuwa 1991. Ya wuce Kwalejin Koyon Aikin Akanta ta Jos. Muktar ya yi aikin NYSC a jihar Ogun, a hukumar saye-sayen Kayayyaki masu muhimmanci a shekarar 1991. Da ya karasa, sai ya fara aiki sashen Kudi na Jami’ar Ahmadu Bello, a matsayin mai kula da hada-hadar sashen da bankuna. Bayan shekaru biyu, sai ya koma bankin Universal a matsayin mai kula da asusun masu hudda da bankin daga shekarun 1993 zuwa 1997. A wannan bankin saida ya kai matsayin Babban Akantan bankin. A shekarar 1997 ne ya mayar da aikinsa zuwa Kamfanin Nalado Nigeria Limited, kamfanin Namadi Sambo a matsayin Babban Akanta, daga baya ya zama Shugaban Ma’aikata, Shugaban Sashen Kudade da Shugabancin Ma’aikata. Cikin hukuncin Ubangiji, da Namadi Sambo ya zama gwamnan jihar Kaduna a 2007, sai ya nada shi kwamishinan ma’aikatar kudi, mukamin da ya rika shekaru uku. Shi memba ne na kungiyoyi da dama, daga cikinsu akwai Kungiyar Akantoci ta Kasa da Cibiyar Shugabannin Kamfanoni da ta Akantocin Kididdiga da Riritawa Kudade da ta Masu ilmin fasaha da Injiniyoyi da sauransu. Yana da aure da ‘ya‘ya, kuma mutum ne mai sha’awar karance-karance da hawan dawaki da sauraren kade-kade da kuma yin mu’amala da mutane, shi ya sanya yake da tausayi. Wani abin lura shi ne, Muktar Yero ya baiwa marada kunya, inda ya gudanar da ayyukan Ma’aikatar Kudin jihar Kaduna cikin rikon amanar da aka san shi da shi, a duk wuraren da ya yi ayyuka a baya. Saboda haka ne, aka ba shi mukamin mataimakin gwamna a lokacin da Shugaba Namadi Sambo ya zama Mataimakin Shugaban Kasa a 2010. Bayan Mutuwar Gwamna patrick Yakowa Ranar Asabat 15/12/2012. sakamakon Hatsarin Jirgin sama a yau. Alh. Muktar Yero ya zama Gwamnan Jihar Kaduna. An rantsar dashi ranar Lahdi 16/12/2012. ALLAH YA TAYAKA RIKO.

Friday, December 14, 2012

ALHAJI TIJJANI DODO HADEJIA.

Image Hosted by ImageTitan.com 
Hadejia a yau!
A ci gaba da kawo muku tarihin wadanda suka bada Gudun mawa a Kasar Hadejia, yau Aji kima ya kawo mana Kadan daga Irin Gudunmawar da Alh. Tijjani Dodo yake bayarwa!

Dattijo Alhaji Tijjani Dodo Hadejia Dan Baiwa ne, Wanda ba kowa ya san hakan ba.Wannan mutumin baya kasa a gwiwa ganin al'uma sun ci gaba. Wannan yasa ya wajabtarwa kansa fafatawa a harkokin rayuwa daban-daban domin samarwa al'uma mafita. Duk wurin da ka leka zaka hango shi saboda Jajircewa da gina rayuwar sa da yayi akan Gwagwarmaya. 

1.Dan kasuwa ne,

2.Dan siyasa ne,

3.Ba sarake ne,

4.Dan kungiyar aikin gayya ne,

5.Dan kungiyar Achaba ne,

6.Dan kungiyar matasa ne,

7.Dan kungiyar yan kasuwa ne,

8.Dan kungiyar ma'aikatan gwamnanti ne

9.Dan kungiyar kwallon kasa ne,

10.Dan kwamatin hawan sallah ne,

11.Dan kwamatin gyaran makabirta ne.

12.Dan kwamatin jinga ne,

13.Dan kwatin gayaran masallaci

14.Dan kwamatin gyaran gari.

15.Dan kungiyar raya al'adun Gargajiya.


Yanzu haka shi ne shugaban aikin gayya na Hadejia,
shi ne kuma shugaban yan Achaba, haka kuma dogari ne a fadar Hadejia. Lalle Juyi Goma sai Wake Inji masu Iya magana.

A hannu daya kuma dan siyasa,dan kasuwa, Jama'a ya kamata mu jinjinawa wannan bawan Allah, Allah ya bamu dubu masu amfani irinsa.

Wannan hotonsa ne yana bada hannu. Bai yadda yaga abu bai yi iya bakin kokarinsa ba. Idan na magana ne zaiyi idan da karfinsa ne zaiyi idan da aljihunsa ne sai yayi.

Allah ya saka da alherinsa.

Monday, December 10, 2012

TARIHIN SHEIKH JA'AFAR MAHMOOD ADAM.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music MARIGAYI SHEIKH JA'AFAR MAHMUD ADAM. GIDANSU, HAIFUWARSA DA .TASHINSA. Babban Shehin Malami, Kwararren mai Tafsiri, Gawurtaccen mai Da’awah,Baban Salim Ja’afar dan Mahmoodu dan Adamu, An haifeshi a yankin Daura a jihar Katsina a Shekara ta 1961. Gidansu Malam Ja’afar, Gidane da su ke kulawa da Ilimin Addini da Haddar Alqu’ani, Kakansa ya kasance yana karantar da Littattafan Fiqhu da Yaren Larabci, Wasu cikin ‘Ya’yansa kuma har sun haddace Alqur’ani. Malamin farko da ya fara dorawa Malam Ja’afar karatun Alqur’ani, Wani Malami ne mazaunin gari Daura mai suna Malam Magaji, yana masa matsayin Babban Yaya ne, domin sun hada dangantaka da shi a Kakanninsu, Shine farkon wanda ya fara koya masa Bakaken Larabci, Wannan Malami, Mahaddacin Alqur’ani ne tun a wancan Lokaci. Baban Salim ya fara koyon karatun Alqur’ani ne a hannun Mijin Babbar Yayarsa mai suna Malam Haruna, wanda shima yana masa matsayin Dan’uwa ne, Daga hannun wannan Malamin ne aka maida Malam Ja’afar hannun wani Malamin kuma Dan’uwansa a kauyen Kuza mai suna Baba Rabe, Wannan Malamin shine ya kaurato tare da Baban Salim zuwa garin Kano a shekarar 1971 ko 1972, Sun sauka a gidan wani Gawurtaccen Mahaddacin Alqur’ani dan kasar Nijer ne mai suna Malam Abdullahi dan Zarmu a unguwar Fage a cikin birnin Kano. Baba Rabe yayi fatar ganin Malam Ja’afar ya haddace Alqur'ani tun yana raye, Amma Allah bai so hakan ya faru a Idanunsa ba, Wannan Malamin ya rasu a shekarar 1977 ne, Shi kuma Malam Ja’afar ya haddace Alqur’ani ne a shekarar 1978 DAGA KARATUN ALLO ZUWA JAMI’A Baban Salim ya haddace Littafin Allah mai girma bai wuce da shekara sha Bakwai ba. Ya fara karatun Alqur’ani gadan-gadan ne a hannun Malam Abdullahi Mutumin Nijar, Malami ne da aka san shi da tsanantawa Almajiransa da matsa musu kan inganta haddar Alqur’ani, Ina ganin wannan matsawar ta shafi har Baban Salim, Domin sakamakonta shine wannan ingantacciyar haddar Alqur’ani da Allah ya baiwa Baban Salim, wacce ba kasafai a ke samun Mahaddata Alqu’ani da irinta ba, In ban da ‘yan kadan cikin Tsarakunsa. Malam bai haddace Alqur’ani a hanun Malam Rabe dan Zarmu ba kamar yadda Malamin yayi fata, Dalili kuwa shine Malam Ja’afar da Tsarakunsa a wancan lokaci, wasan kwallon kafa da zuwa kallonta ya dauke musu hankali kan tsayuwar daka kan haddar Alqur’ani, Wannan ya sa, Malam Rabe ya daukeshi daga hanun Malam Dan Zarma ya maida shi garin Hadejiya ya damka shi a hannun wani Malami dan asalin gari Daura amma Mazaunin Hadejiya mai suna Malam Safiyanu,wanda shima Dan’uwa ne ga Malam Ja’afar domin sun hada dangi da shi ta Kakanninsu. Malam Rabe yayi masa haka ne don ya raba shi da kayaniyar Birni da kuma damuwa da Lamarin kwallon Kafa, Maiyiwuwa hakan zai sa shi ya maida hankali kan haddar Alqur’ani, Lalle kuwa hakan ya faru, domin Baban Salin a can ya kamala haddar Alqur’ani bayan rasuwar Malam Rabe. Bayan fara baiyyanar Kungiyoyin Musulunci a Nigeria, Musamman ma Kungiyar Izala, Sai jayayya ta yi yawa tsakanin Mutane kan wassu Mas’aloli kamar ; Hukuncin Salatul Fatih, matsayin Darikun Sufaye, Hukuncin Durkuso a gaisuwa, Sadakar Fida’u bayan Mutuwa, Taron Suna da wassu Al’adun kasar Hausa, Wannan ya tilasta Malam Ja’afar neman Ilimin Littattafai. Malam Ja’afar ya shigar da kansa Makarantu Biyu lokaci guda. Ta farko a wata cibiya ta kasar Masar da ke garin Kano, Ta Biyu kuma wasu Azuzuwa ne da aka bude don yaki da Jahilci. Malam Ja’afar bai shiga Makarantar Firamare ba saboda a wannan lokaci sun yiwa wannan matakin karatun girma. Ya yi karatu a wadannan Makarantu na tsawon shekara Uku a jere daga 1980 zuwa 1983.

Tuesday, November 27, 2012

MANYAN 'YAN SIYASAR HADEJIA

Hadejia A yau. Wadannan mutane sune Ruhin siyasar Hadejia! Gudunmawar da suka bayar a siyasa da ci gaban yankin Hadejia sai dai Allah ya saka musu da Alkairi. Sunyi siyasa a lokacinda ba'a san Daga kai sai 'ya'yanka ba! Domin sun kafa mutane da dama a Hadejia da kewaye. Duk unguwa zakaga akwai mutanenda suka kafa a siyasa. Lalle sun cancanci yabo. Idan muka fara da Marigayi Alh. Bello Auyo zamuga cewa Ayyukanda yayi a Hadejia har yanzu babu wani ko wata gwamnati da tayi makamancin nasa. Kama da Secretaria, Maternity, da sauran abubuwanda har yau ana amfana dasu a Hadejia. Allah ya kyauta kwanciya. Mallam Ibrahim Kwatalo shima ya gina mutane daban daban a Tarihin siyasar Kasar Hadejia. Duk Wanda yanzu yake Cikin Gwamnati, in ba yaronsa ba sai wanda shine ya kafashi. Allah ya kyauta kwanciya. Alh. Shehu Mujaddadi (Alkali) shehu Illa shehu, shima kamar M. Ibrahim Kwatalo, ya gina mutanenda suka gina Mutane a Tarihin siyasar Hadejia. Kuma Har yau Taswirar siyasarsa ce take Tasiri a Hadejia. Allah ya kyauta Kwanciya. Alh. Muhammadu Danjani Hadejia tarihin siyasar Hadejia bazai manta da kai ba! Shi ya fara Dan majalissar Wakilai a Jamhuriya ta biyu. Kuma jigo ne a jam'iyyar NEPU. Wadanda sukayi yaki da mulkin Danniya da kama karya. Shaho birkita kaji na Garba, Bauna wanda ya dosheta babu maduhu sai wani ba tasa ba. Allah ya kyauta kwanciya. Ahmed Garba (M.K.) ko an kika irinka akeso. Har yau Taswirar siyasar Hadejia tana Hannunsa. Duk unguwarda kaje a Hadejia to akwai mutanen da a kafa kuma suka kafu. Ya samawa matasa aikin yi bansan Adadi ba! Amma nasan babu wanda yayi kamarsa kawo yanzu. Zabgai yabin Bauchi da kare dangi Maza sai kui Hankali, Mai tulu kaji tsoron fad da mai sanda ko yana a kwance! Kainuwa dashen Allah yaya zakuyi? Ruwa sai ya kare Kainuwa ta kare ba dai kaga bayanta ba. An karawa kogi Ruwa mai jinga kayi jingarka zai karya Inda yakeso yabi. Masu fura da zuma sun kula da gwangi, idan gwangin zakusha to, Allah ya bamu zuma ku ya baku Gwangin baya tana son gaba. Hadejia A yau.

Thursday, November 15, 2012

TAKAITACCEN TARIHIN SHETTIMAN HADEJIA DA M. BILYAMINU USMAN.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Musichttp://www.MyspaceImageCodes.net">Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau! Assalamu alaikum! Barkanmu da shigowa sabuwar shekarar Musulunci. A daidai lokacinda muke kokarin Bankwana da shekarar 2012, Allah cikin Ikonsa wannan shekara tazo mana da wani bubban Rashi wanda bazamu manta dashi ba! Wannan rashin kuwa shine na Alh. Bilyaminu Usman da Alh. Hassan Hadejia (shettiman Hadejia). A ranar Asabat 20/october/2012 Allah yayiwa M. Bilyaminu Usman Rasuwa yana da shekaru 83. Kafin rasuwarsa ya rike mukamai da dama musamman a hukumar Ilmi. M. Bilyaminu ya fara koyarwa a Middle school wato Abdulkadir a shekarar 1948, kuma yayi sakataren Ilmi a Hadejia kuma a shekarar 1976 yayi kwamishinan Ilmi a tsohuwar jihar Kano a lokacin Gwamna Sani Bello. Kuma M. Bilyaminu yayi ministan Ilmi a Jamhuriya ta biyu Lokacin shehu shagari. Kuma ya rike Mukamin Chairman primary Education Board a shekarar 1999. Allah ya kyauta kwanciya. Kuma ya bar mana abin koyi a sha'anin zaman rayuwa, wato Gaskiya da rikon Amana. Ko wadanne Irin darasi muka koya daga Rayuwarsa? Hadejia a yau. http://www.facebook.com/Ismailaasabo Haka kuma Ranar laraba 7/November/2012 Allah yayiwa Shettiman Hadejia Rasuwa Alh. Hassan Abbas, sakamakon 'yar gajeriyar jinya, Shettiman Hadejia tarihin Hadejia bazai manta da irin Gudunmawar da ya bayar ba ta hanyar ci Gaban garin Hadejia da Taimakon Addini, masu iya magana suna cewa ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Wannan Haka yake Kasar kago bata Maida Kago. Shettiman Hadejia ya rike mukamin Minista a lokacin Jamhuriya ta daya, bayan nan ya rike mukamin Ministan Man fetur a zamanin Ibrahim Babangida, kuma shine shugaban Kaduna polo club, sannan shine Chairman Board of Directors a kamfanin Leadway Assurance! Sannan Board member A Masallacin sultan Bello dake Kaduna. Allah ya kyauta kwanciya! A cikin abubuwanda ya bari wadanda zamuyi koyi dasu akwai kyautatawa al'umma da taimakawa Addinin musulunci da zumunci. Hadejia a yau. Muna rokon Allah ya bamu Albarkar wadannan mutane, Allah ya maida mana makamantansu, Allah ka kara mana Gaskiya da Rikon Amana da taimakon Al'umma. HADEJIA A YAU.

Monday, November 5, 2012

SULE LAMIDO SAI GODIYA.

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU! Alhamdulillahi Godiya ta tabbata ga Allah wanda yake bada Mulki ga wanda yaso, kuma a lokacinda yaso, Tsira da Aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu wanda Allah ya aikoshi da shiriya da rarrabewa tsakanin Karya da Gaskiya!

Bayan haka muna kara Godiya ga Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Dr. Sule Lamido, wanda Allah ya bashi Mulkin Jigawa domin ya Gudanar dashi bisa Gaskiya da Adalci. Alhamdulillahi Jigawa a yau.

Ranar Litinin 5/11/2012. Mai Girma shugaban kasa ya kawo mana ziyara Hadejia a karkashin mulkin Gwamna Sule Lamido, Inda kuma akayi hawan Daba kasaitacciya. Hakika wannan abin Alfahari ne a garemu Hadejiawa kuma babu abinda zamucewa Mai Girma gwamna sai godiya.

Bayanda shugaban kasa yazo Hadejia ya ziyarci fadar Mai martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje, bayan yaga Hawan Daba da aka shirya masa ya gana Da Mai martaba Sarki. Kuma ya nemi Alfarma guda Uku wadda zata kara Inganta wannan yanki na Hadejia. Na farko ya nemi Alfarmar Gwamnati da ta ci gaba da aikin B.E.C. Wanda a halin yanzu ya dakata, na Biyu ya nemi Alfarmar da ayi mana Maganin Ambaliyar Ruwa da ta Addabi wasu sassa na Hadejia.

Na uku ya nemi Alfarmar a Sake Inganta Jingar Kogi wadda ake samun Asarar Dukiyoyi da amfanin Gona.

Muna kara Godiya ga Wannan Gwamnati wadda A zamaninta ne Jigawa ta tabbata Jigawa. Hakika duk wanda yasan Jigawa shekara Bakwai baya Idan yazo zai tabbatarda Jigawa ta samu Uba. Jigawa abar Alfaharinmu, Sule Lamido Abin Alfaharin Jihar Jigawa.

Hakika abubuwanda mukeji a baya kunnenmu ne yaji Idonmu bai gani ba. Dan haka ka bada saida akan abinda Idonka ya gani yafi akan abinda kunnenka yaji. Muna kara jinjina ga Mai Girma Gwamna Wanda ya daga Darajar wannan Jiha tamu. Jigawa ada take Jaririya amma a yanzu Uwace a zamanin Sule Lamido.

Ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Jigawa ta tattara Manyan Mutane masu hazaka! kama daga Gwamnan zuwa comishinoni da sauransu. Jigawa tarin Allah Lamido Ikon Allah.

Allah ya huci gajiya, Allah ya maida kowa Gidansa Lafiya. Ameen. Hadejia a yau.

Sunday, November 4, 2012

WAKAR TARIHIN YAKIN HADEJIA DAGA LIMAN MUHAMMADU (Fassara daga Alh. Ibrahim katala).

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau. 1, Allahu sarki shi kadai yake wahidun, sammai da kassai jalla bashi da kishiya. 2, Shi ba fari shi ba baki ba ubangiji ba ja ba ba alkashi bashi ga rawaya. 3, Ba sake sake ba ba kamar yarani ba shudi da kore jalla bashi da mai kama. 4, Zatinsa baya tattara bai rarraba da kawai da motsi bayayi ko sau daya. 5, Sarkinda ba na biyunsa ba na uku nasa ka dadan basira zanyi waken shahidu. 6, Ranar talata munga tashin duniya Rannan Muhammadu yai shahada zahira. 7, Shi yai jawabi ya fada shi bai gudu kuma bashi mai kamu a darul duniya. 8, Raggo ake kora a bishi a cim masa amma sadauki bai gudu sai faduwa. 9, Sarki Muhammadu yai jawabi ya cika shi bashi mai kamu a jashi ya tunkiya. 10, Dan melle sarkin yaki shima ya fada in dai da rai sarkinmu baya kamuwa. 11, Ma'ajin Hadejia saleh shima ya fada mun dau shahada zahira bahakikiya. 12, Manya da yara duk shirin yaki suke kowa yana wanka yana yin alwalah. 13, Kowa yana yin sallama a gida nasa sunsa gabansu a lahira ba dawaya. 14, Jama'ar Hadejiawa fa duk sun hallara kowa yana cewa fa mun zama shahidai. 15, Sarki Muhammadu mai shahadar zahiri ba badili ko dai cikin tawaga tasa. 16, Shi bai kamar tsoro ba baya razana kan ya ije ma babu sauran hanzari. 17, Ajali idan yayi babu kwana duniya kai dai zamo kullum shiri duka safiya. 18, Shi bai kamar tsoro a baya razana baya gudu dan Garba sarkin jarumai. 19, Mutuwa tafarki wanda kowa zayabi ai kulli nafsin dukka rai zai dandana. 20, Aka daura sirdi nai ya hau bisa ya tsaya yace mu dau himmar shahada zahira. 21, Sarki Muhammadu baya tsoro ko kadan Allah ma'aiki su take tsoro kadai. 22, Hauninsa linzamin mayani ya rike damansa tasbihi salatin annabi. 23, Dan mai karatu tudun kasa ba dawaya dan garba jikan sambo sarkin adalai. 24, Duk mai shahada auwalinsa madacima suka barace da fari ya mutu shahidi. 25, Farkon hawa yaki galadima sai haru ranar talata sun ka sauka a barzahu. 26, Alkali sarkin yaki kaura amada sarkin arewa da sunkaje can sun tsaya. 27, Suka jeru sunka tsaya a nan kofar gabas kafin suje har mai ruwa ya taddasu. 28, Kasan igwa dokinmu shi bai santa ba duka dokuna na faduwa ba lissafa. 29, Igwa tana tashi madafa na zuba yau sai ta Allah babu sauran shawara. 30, Jaruman Muhammadu basu tsoro ko kadan sun gwammace mutuwa da dai subi kafiri. 31, kuma sabo jikan tete harbi nai ake anan a kofar fada duk suka tuntsure. 32, Firyan Hadejia shi da bori na salihu kofar gabas suka fadi nan aka cim musu. 33,Dan Dodo Barwa da shi da gwanki baran nufe, sun karbi hartashi a kwaryar kai nasu. 34, Ai babu mai mutuwa gaban ajali nasa kan surfa gero kan daka wasu sun fice. 35, iko idan Allahu yayi nufi nasa ai ba tsimi balle dabara ko daya. 36, Tamkar kamar inuwarka baka guje mata in kai gudun ta bika harma ka tsaya. 37, Hartashi na yawo kamar burduduwa tamkar zubar wake a can a masussuka. 38, Ya ratsa soraye ya ratsa katanguna tamkar kabewa ko kamar tumfafiya. 39, Yasha zarar soro ya keta katanguna da kago da zaure sun zube ba tambata. 40, Tsarnu da kurna har kasa durumi dada ya kar dabinai cediya da itatuwa. 41, Rannan Hadejia munga tashin hankali Allah da manzo su kadai ne magani. 42, Abdulwahabu baka tana hannu nasa artashi ya samar ya tsinke tsirkiya. Edited by (Idris M. Eddy) DA SAURAN BAITI SAI A SAURAREMU A GABA.

Tuesday, October 30, 2012

TAKAICACCEN TARIHIN LIMAMIN HADEJIA M. YUSUF IMAM.

Hadejia A yau.
Hadejia A yau. HADEJIA A YAU!Hadejia A yau. A ci gaba da kawo muku Tarihin wadanda suka bada Gudunmawa a Hadejia, yau Zamu baku takaitaccen Tarihin Bubban Limamin Hadejia MALLAM YUSUF ABDURRAHMAN. Muna farawa da sunan Allah wanda da ikonsane komai ya kasance da kuma Abinda zaya kasance! Tsira da Aminci su tabbata ga Manzon Allah (s.a.w.) wanda ka aiko dashi bil’haqqi da Gaskiya.

An haifi Limamin Hadejia M. Yusuf Imam a unguwar Rumfa da ke cikin Garin Hadejia, a shekarar 10/1/1980, kuma ya fara karatun Addini a Gurin Mahaifinsa M.Abdurrahman Ya’u, bayan ya kai shekaru bakwai (7) shi da ‘yan uwansa an kaisu Makarantar Allo a unguwar Yayari, wato makarantar Mallam Muhammadu Dan birni. Bayan yakai shekaru Ashirin (20) ya koma Makarantar Malam Garba Dake ‘Yankoli, kuma anan ne ya sauke Alqur’ani mai tsarki.

A shekarar 1998 Malam Yusuf ya samu nasarar shiga Makarantar koyon karatun Addini ta Hadejia (S.A.I.S.) inda kuma anan ne ya sake sauke Alqur’ani a Ruwayar Hafsi. Tare da Na’ibinsa M. Habibu Aminu.

A shekarar 2002 Malam Yusuf ya samu nasarar shiga Makarantar Horar da Malamai dake Gumel (ATC.GUMEL) Inda ya samu saidar N.C.E. A bangaren Arabic. Kuma ya samu aikin koyarwa a ma’aikatar Ilmi dake Auyo, bayan shekaru ya dawo yaci gaba da koyarwa a Makarantar S.A.I.S. Dake garin Hadejia.

Malam Yusuf yayi karatun Ilmin Addini a gurin Malamai da dama kamar M. Usman danyaro, Malam Tela Majema, M. Akilu, M. Aminu Ibrahim Daurawa da sauran Malamai.

A ranar Asabat 5/1/2002 Malam Yusuf Imam ya fara bada Ilmi a soron Gidansu, Inda ya fara da Dalibai kamar haka:-

Mohd. Abubakar Malam namu, Ismaila A sabo, Baffale Muhd. Furdi (Baffaliya), Idris Baffa (Liyan), Yusuf abdulkadir wakili, da Adamu A Amar.

Ranar 12/feb./2006 an gayyaceshi da ya gabatar da Maudhu’i a masallacin Juma’a, Inda kuma yayi fadakarwa akan Alamomin tashin Alqiyamah. Wanda kuma wannan fadakarwa ta jawo hankalin mutane akan ranar tsayuwa,wato Alqiyamah.

A ranar Talata 29/Aug./2006 Malam Yusuf ya fara jan Sallah a masallacin juma’a. Sakamakon Rashin lafiyar Limamin wancan lokacin Malam Shehu Qassim.

Haka kuma ranar juma’a, 8/ september/2006 Malam Yusuf ya fara fassara Huduba a Masallacin Juma’a Kuma a wannan lokacine aka tabbatar dashi Na’ibi na biyu.

Ranar Litinin 2/june/2008 Allah yayiwa Limamin Hadejia rasuwa Malam shehu Qassim, kuma bayan mutuwarsa ne Ranar Litinin 23/june/2006 aka tabbatarwa Malam Yusuf Imam ya zama Bubban Limamin Hadejia. Da misalin karfe tara (9:m) na dare.

A Ranar Juma’a 27/June/2008 Mai martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu A. Maje ya nada Malam yusuf a Matsayin Bubban Limamin Hadejia. Da misalin karfe (10:am) na safe. Sannan a ranar ya fara sallar Juma’a Inda kuma yayi Huduba mai daidaita hankali da kuma tabbatar da Ikon Allah shine abinda za’abi a zauna lafiya.

A Gudunmawar da Mallam Yusuf Imam ya bayar a cikin Garin Hadejia ta bangaren Ilmi, Harda karatuka da littatafai da ya karantar A masallacin Juma’a. Kamar:- 1,UMDATUL-AHKAM 2, MUWADDA MALIK 3, LU’U-LU’U WAL MARJAN, IHYA-USSUNNAH Da sauran Littatafai. Da kuma Lecture da yayi a Gurare da dama a cikin garin Hadejia da kewaye.

A watan August na wannan shekara Malam Yusuf ya tafi kasar Sudan Domin Karo Ilmi. Muna Addu’a ga Malam Allah ya haskaka zuciyarsa ya kyautata jinsa da Ganinsa ya kara masa Ilmi da Basira. Ameen.

Allahumma badi’ussamawati wal’ardhi, zaljalali wal’Ikrami, wal-izzatullati la tarami, As’aluka ya Allahu, ya rahman bi jalalika, wa nuru wajhika, antalzim qalbi hifzu kitabuka, kama allamtani, warzuqni antilawahu alannahwullazi yardhika anni. Ameen. Hadejia A yau. HADEJIA A YAU!

Monday, October 29, 2012

HAWAN ZIYARA..


HADEJIA A YAU!
Kamar yadda aka sani Æ™asar Hadejia tana gabatar da Hawa guda uku a kowace shekara, wato Sallar Azumi, Sallar Layya da kuma Maulidi. Sannan kuma a kowace Sallah ana gabgaba da hawa guda biyu...  Hawan sallah da Hawan Bariki, Sannan  rana ta uuku yara suyi Hawan daushe da La'asar.

Kamar yadda Tarihi dai ya nuna Sarkin Hadejia Mallam Abdulkadir shine ya kirkiro Hawan Bariki, a wata fira da mukayi da Galadiman Jauje ya tabbatar mana cewa Sarki Abdulkadir mutum ne Mai son nishadi,  hakan yasa a zamanin sa aka kirkiri Hawan Bariki. Sarki yaka je washegarin sallah da hakimansa da Dagatai su kaiwa D.O. Ziyara.

Ranar Laraba 20/April/2005 Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu AbuAbuba Maje ya kirkiro Hawan Ziyara kokuma Hawan Mai Bubban Daki, wannan hawa an fara yinsa ne a sallar Mauludi, wadda kuma za'a rinka yinsa ko wace sallah da yamma. Wato za'a hau washe garin Hawan Bariki.

Ranar Juma'a 22/April/2005, Mai martaba ya hau da yamma. Inda yabi ta tudun mabudi Har zuwa Tudun Barde ya shiga yayi ziyara ga Mai bubban Daki, Bayan ya fito sai yabi ta makera ta Dubantu ta Ganuwar kofar yamma, sannan sai yabi ta bakin kasuwa ta Makwallah ta kofar Jarma sannan In yazo kofar Fada sai ya Tsaya Hakimai kuma su Fara zuwa daya bayan daya suna Jafi. Bayan sun Gama sai ya shiga Gida ya sauka. Hadejia A yau.
Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music
HADEJIA A YAU!
Kamar yanda aka sani kasar Hadejia tana Hawan sallah da Hawan Bariki a kowace sallah. Sannan kuma yara suyi Hawan daushe da La'asar.

Kamar yanda Tarihi ya nuna Sarkin Hadejia Abdulkadir shine ya kirkiro Hawan Bariki, a wata fira da mukayi da Galadiman Jauje ya tabbatar min cewa Sarki Abdulkadir mutum ne Mai son Hawa. Kuma shine ya kara hawa ake yin Hawan Bariki, zaije da hakimansa da Dagatai su kaiwa ( Resident) da D.O. Ziyara.
Ranar Laraba 20/April/2005 Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Maje ya kirkiro Hawan Mai Bubban Daki, A sallar Mauludi, wanda kuma za'a rinka yinsa ko wace sallah da yamma. Wato za'a hau washe garin Hawan Bariki.
Ranar Juma'a 22/April/2005, Mai martaba ya hau da yamma. Inda yabi ta tudun mabudi Har zuwa Tudun Barde ya shiga yayi ziyara ga Mai bubban Daki, Bayan ya fito sai yabi ta makera ta Dubantu ta Ganuwar kofar yamma, sannan sai yabi ta bakin kasuwa ta Makwallah ta kofar Jarma sannan In yazo kofar Fada sai ya Tsaya Hakimai kuma su Fara zuwa daya bayan daya suna Jafi. Bayan sun Gama sai ya shiga Gida ya sauka. Hadejia A yau.

Friday, October 26, 2012

BARKA DA SALLAH. (Layya)

Free Web Proxy HADEJIA A YAU! HAWA LAYYA
Yin layya sunnah ce mai karfi da ta kasance
wajibi ga dukkan musulmi. Maza da mata
kowacce shekara. Ta kan fadi a kan mutum in
ba shi da sarari. To ko maras sarari da ya
sauka a wannan shekara ko bai taba hawa
ba . Ya shiga cikin daya daga raguna 2 da
Annabi(s) ya yanka. Ya ce daya nasa ne daya
na masu karamin karfi cikin al'ummarsa har
zuwa tashin kiyama.
Ya tabbata daga ma'abuta ilmi cewa in kana
da riguna 2 ka sayar guda ka yi layya. Annabi
(s) ya ce duk wanda ya ke da dama kuma ya
ki yin layya to kada ya kuskura ya zo wuraren
sallar Idin mu. Annabi(s) ya ce za a ba mai
layya lada kan kowanne gashi guda na adadin
gashin da ke jikin dabbar da ya yanka.

Monday, October 22, 2012

KWANAKIN HAJJI DA GURARE GOMA MASU ALBARKA. DAGA (M. AMINU DAURAWA)

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music HADEJIA A YAU!

Na daya ranar takwas ga watan hajji, sunanta yaumuttarwiyya,
shine alhazai suke zuwa mina su wuni su kwana,
Na biyu ranar tara ga wata itace ranar arfa, itace alhazai suke wuni a
filin arfa zuwa faduwar rana, daganan su tafi Muzdalifa su kwana
Na uku ranar goma ga wata, itace alhazai suke gabatar da aiyuka
guda biyar a cikinta, jifa, yanka, aski, dawafi, saayi,
Na hudu ranar sha daya , da sha biyu, da sha uku, sune ranakun
kwanan mina da jifa, Abubuwa goma masu daraja a Macca
wadanda suke da alaka da aikin hajji, wadanda ake aiwatar da aikin
hajji, daura da su sune, na daya, Ka'aba ana kewaya ta sau bakwai,
na biyu, alhiji (wanda ake cewa hijri isma'ila) ana shiga ciki ayi
salla,daidai yake da yin sallah a cikin Ka'abah, na uku, makamu
ibrahim, wanda ake sallah Raka'a biyu a bayansa bayan gama
dawafi, na hudu, Alhajrul'aswad, (dutsen aljannah) ana sunbatarsa
(kiss) a shefeshi, ayi sujjada akansa, ko anunashi daga nesa ayi
kabbara, na biyar ruwan zamzam, ana sha a shafa a fuska, a zuba
ajiki, ayi addu'a, aroki Allah bukarar duniya da lahira hadisi ya
tabbata, akan haka, na shida Dutsen safa da marwa, wanda ake
zirga-zirga tsakanin su sau bakwai a fara daga sama a kare a marwa,
na takwas, mina wajen kwana da ranakun jifa, na tara arfa da
muzdalifa, a wuni a arfa a kwana a muzdalifa, na goma wajen jifa
guda uku, inda ake jefa tsakuwa guda saba'in, Allah ta'ala yace
wanda ya girmama alamomin addinin Allah, yana daga cikin tsoran
Allah na zuci, wanda duk yayi sallah a masallacin macca yana da
lada dubu dari, wanda ladan ya shafi dukkan fadin iyakokin harami,
tun daga ka'abah, Manzon Allah saw yace :Duk wanda yayi hajji,
baiyi kwarkwasaba (maganar batsa da mata) baiyi fasikanciba, zai
dawo kamar ranarda mahaifiyarsa ta haifeshi, kuma yace, Hajji
kubutacce(shine wanda akayishi akan sunnah da iklasi da ilmi) bashi
da sakamako sai aljannah, ku tayamu da addu'a mu sami wannan
garabasar, Allah ya karbi ibadarmu yasa mu dace da sunnah da
iklasi na gode

Saturday, October 20, 2012

HADEJIA TO DATE!

Hadejia A yau! Hadejia, town and traditional emirate,
eastern Jigawa state, northern Nigeria. It lies
on the northern bank of the Hadejia River (a
seasonal tributary of the Komadugu Yobe,
which flows into Lake Chad). The emirate’s
savanna area originally included Hadejia and
six other small Hausa kingdoms that paid
tribute to the kingdom of Bornu.



About 1805, Umaru, a Fulani leader who held the
title sarkin Fulanin Hadejia,
pledged allegiance to the Fulani jihad (holy
war) leader, Usman dan Fodio.


Umaru's brother and successor, Emir Sambo
(reign 1808–45), officially founded the Hadejia
emirate in 1808, moved his headquarters to
Hadejia town, established a market, and
began to consolidate Fulani rule over the
small neighbouring Hausa kingdoms.


Emir Buhari (reigned
1848–50, 1851–63) renounced Hadejia’s
allegiance to the Fulani sultanate centred at
Sokoto in 1851, raided the nearby emirates
of Kano, Katagum, Gumel, Bedde, and
Jama’are, and enlarged his own emirate.

Hadejia was brought back into the Fulani
empire after Buhari’s death, but wars with
neighbouring Gumel continued until 1872.

In 1906 the British installed an emir, Haruna, (Maikaramba)
and incorporated the emirate into Kano
province.
The emirate became part of newly
created Jigawa state in 1991.


The town is now a market centre handling
cotton, millet, sorghum, fish, and the rice
grown in the river valley. It serves as an
important collecting point for peanuts
(groundnuts), an export crop. Cattle, goats,
guinea fowl, sheep, and donkeys are kept by
the local Hausa and Fulani peoples.
Several
small lime industries exist in scattered parts
of the area. Hadejia town is located on the
secondary highway between Gumel and
Nguru, which links it to the main highway at
Kano and to the railway at Kano and Nguru.
Pop. (2006) local government area, 105,628.

Saturday, October 6, 2012

THE 19TH CENTURY JIHAD AND ESTABLISHMENT OF HADEJIA EMIRATE (PAGE 2)

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU!
The new ideas generated as a result of their policies had brought together people of diverse (descent) linguistic and occupational groups under one
umbrella. Although ever since their migration into Hausa land, some fulani Jihadists in due course became confidants and advisers to some Hausa rulers, there was a strong and persistent tendency among the Jihadists of avoiding close association with HABE SARAKUNA, either because of
the fear or being contaminated with Illigally acquired wealth or because most of the Habe palaces remained a stronghold of various traditional cultssuch as BORI Cult.




This made the devoted Ulamas keep their distance from the rulers (sarakuna). It was the relationship between these two classes the Ulamas and the Habe rulers that
eventually led to the outbreak of the Jihad in Hausa land at the beginning of the 19th Century.
The condition of Hausa society at the eve of Jihad was anything but fair, especially the socio-economic system.




Virtually all the rulers were norminal Muslims and therefore hardly enforced the Sharia system. At the same time enforced excessive taxation. Yet in the midst of the suffering and hardship, the rulers continued to be corrupt, unjust and indifferent to the plight of the oppressed.




There seem to be some confusion as regards the exact time when the fulani Jihadists first came and established their wet-season camps in the plentiful grazing land of the Auyo/Hadejia riverrine savannah land, the confusion is due to the multiple causes of Nomadic Fulani movements in the
Nigerian Savannah in general and the Hadejia area in particular. H.M. Brice Smith, has placed the coming of the Fulani into the Hadejia area at themiddle or late 1700 A.D.




But according to A. Abdu Maigari, the Fulani came to Hadejia area from Machina in Borno during the 15th Century.
An early Fulani settler in Hadejia who became very influential in one Hardo Abdure dan Jamdoyji, wealthy Fulani who traced his Origin to Machina in Borno. Hardo Abdure established his dry season camp in Hadejia at Jarmari during the early 18th Century.
Jarmari is located few kilometres from Hadejia town. As the case will all Nomadic Fulani camps the one established by Hardo Abdure at Jarmari was not meant to be permanent abode.





Rather it was ment to serve the
purpose of their seasonal movements.
HADEJIA A YAU!

Thursday, October 4, 2012

THE 19TH CENTURY JIHAD AND THE ESTABLISHMENT OF THE HADEJIA EMIRATE. (page 2)


HADEJIA A YAU!
The new ideas generated as a result of their policies had brought together people of diverse (descent) linguistic and occupational groups under one umbrella. Although ever since their migration into Hausa land, some fulani Jihadists in due course became confidants and advisers to some Hausa rulers, there was a strong and persistent tendency among the Jihadists of avoiding close association with HABE SARAKUNA, either because of the fear or being contaminated with Illigally acquired wealth or because most of the Habe palaces remained a stronghold of various traditional cults such as BORI Cult. This made the devoted Ulamas keep their distance from the rulers (sarakuna). It was the relationship between these two classes the Ulamas and the Habe rulers that eventually led to the outbreak of the Jihad in Hausa land at the beginning of the 19th Century.


The condition of Hausa society at the eve of Jihad was anything but fair, especially the socio-economic system. Virtually all the rulers were norminal Muslims and therefore hardly enforced the Sharia system. At the same time enforced excessive taxation. Yet in the midst of the suffering and hardship, the rulers continued to be corrupt, unjust and indifferent to the plight of the oppressed.

There seem to be some confusion as regards the exact time when the fulani Jihadists first came and established their wet-season camps in the plentiful grazing land of the Auyo/Hadejia riverrine savannah land, the confusion is due to the multiple causes of Nomadic Fulani movements in the Nigerian Savannah in general and the Hadejia area in particular. H.M. Brice Smith, has placed the coming of the Fulani into the Hadejia area at the middle or late 1700 A.D. But according to A. Abdu Maigari, the Fulani came to Hadejia area from Machina in Borno during the 15th Century.

An early Fulani settler in Hadejia who became very influential in one Hardo Abdure dan Jamdoyji, wealthy Fulani who traced his Origin to Machina in Borno. Hardo Abdure established his dry season camp in Hadejia at Jarmari during the early 18th Century.

Jarmari is located few kilometres from Hadejia town. As the case will all Nomadic Fulani camps the one established by Hardo Abdure at Jarmari was not meant to be permanent abode. Rather it was ment to serve the purpose of their seasonal movements.

Monday, October 1, 2012

MOVEMENT FOR CREATION OF HADEJIA STATE SINCE 1975.

HADEJIA A YAU! The struggle for the creation of
Hadejia State traces its history back
to 1975 when the community
forwarded its request to the then
military head of state, the late
General Murtala Ramat Muhammad.
Since then, the community has
never failed in exploiting every
opportunity offered by the government for
the creation of more states.
According to findings, the request for the
creation of Hadejia State received a boost
between 1982 and 1983 when the then
National Assembly endorsed the request for
the referendum, but due to a change of
government, the long-awaited dream could
not be actualised.
Also in 1991, a similar request was put
before the then Military Head of State,
General Ibrahim Badamasi Babangida. In
1994 another request was submitted to the
then National Constitutional Conference
under late General Sani Abacha.
Pyramid Trust learnt that when the National
Constitutional Conference submitted its
report to the Provisional Ruling Council (PRC)
, the proposed Hadejia State was among the
seven states recommended for early
creation by the PRC.
The community, our correspondent learnt,
made a fresh request for the creation of
Hadejia state in 1996 through the Local
Government and Boundary Adjustment
Committee, a committee set up by the
federal government to re-examine the
recommendations of the National
Constitutional Conference on creation of
states and local governments as well as
border adjustments.
However, following the PRC’s
recommendation that suggested the
creation of one state in each of the six geo-
political zones, Hadejia community lost their
bid to the present Zamfara State being the
only state created from the North-West zone
then.
In October, 2009, the request for the
creation of Hadejia State was also
forwarded to the National Assembly for
endorsement and onward conveyance to
the executive arm of government for the
final approval. Furthermore, in 2009, a
memorandum requesting the creation of
Hadejia State was also presented to the
NASS. The community also requested the
creation of 11 additional local governments
that included Bualngu, Biram, Diginsa,
Dakaiyawa and Fadama local governments.
Others are Sarawa, Jarkasa, Kadira, Ruba,
Jabo and Ayama local government areas.
This makes the number of local
governments for the proposed Hadejia State
to 19, as initially, the Hadejia Emirate
comprises of only eight local government
that include Auyo, Birniwa, Guri, Hadejia,
Kafin-Hausa, Kaugama, Kirikasamma and
Mallam-Madori.
Findings indicated that the proposed
Hadejia State has a land mass of not less
than 7000sq km with a population of
1,245,571 according to the statistics of the
2006 National Population Census. The
population might have increased by now
given the average national growth rate of
2.83% per annum.
Under the provincial system of
administration, Pyramid Trust gathered,
Hadejia Emirate was the second largest
emirate in the then Kano province in terms
of size, economy, population and other
socio-economic indices. The area was also
blessed with enough human and natural
resources that include water and fertile soil
suitable for all kinds of agricultural activities.
However, just last Wednesday, the July 28,
2010, Hadejia community under the auspice
of Movement for the Creation of Hadejia
State again put another request before the
National Assembly for the creation of
Hadejia State.
The delegation was led to the NASS from
Jigawa State by the Speaker, Jigawa State
House of Assembly, Alhaji Adamu Ahmad
Sarawa.
In a separate presentation, the Speaker
informed the leaders of the NASS that, “From
the information available to us, each of the
requests previously put before the
concerned authorities made progress
towards realisation of our proposed state,
but only to be scuttled apparently due to the
undemocratic nature of the situation.”
Alhaji Adamu further recalled that the
proposed Hadejia State and its people were
the most unfairly treated in the history of
state creation exercise of the military
nationwide. He added that although
pessimistic Nigerians have the belief that
due to the cumbersome provision of the
constitution, new states could not be
created under a democratic setting, the
people of Hadejia do not share this
pessimism.
“We believe the National Assembly can break
that jinx and create more states during the
lifetime of the present administration. And
we hope that Hadejia State would be one of
the new states to b

Saturday, September 29, 2012

GAMON KAFUR

HADEJIA A YAU!
Bayanda Sarkin Hadejia Buhari da jarumansa suka kare Yakin Takoko inda kuma anan ne Allah yayiwa sarkin Hadejia Ahmadu Rasuwa Inda wani Jarumin Buhari mai suna Barde Risku ya kasheshi. Dukda Umarnin da Buhari ya bayar cewa kar a kasheshi, Buhari da jarumansa sai suka shigo Hadejia wato ya zama shine Sarkin Hadejia. Sarkin Hadejia Buhari ya Rubuta wasika Zuwa ga Sarkin Musulmi, ya masa Ta'aziyyar Sarkin Hadejia Ahmadu, kuma ya nuna cewa yanzu shine Sarkin Hadejia yana neman sarkin Musulmi ya amince dashi. Kuma hakan bata samu ba.


Sarkin Musulmi Alu Bubba
sai ya gayyaci duk sarakunan dake
Karkashin Daular sokoto da su hadu su
yaki Buhari. Ko a kamashi da rai ko a
kashe shi. Wannan kuwa ta faru ne a
shekarar (1853). An hada wannan
rundunar yakin ne karkashin Jagorancin
Galadiman Kano Abdullahi maje Karofi
kafin ya zama Sarkin Kano. An gayyaci
mayaka a Garuruwa daban daban kamar
Kano,zamfara,Bauchi,Katagum,Misau,zaria
da sauran garuruwan Daular Sokoto.


Masana tarihi sunce an tara mutum A kalla
Dubu Ashirin (20,000) Abdullahi Maje
Karofi ya Umarci Sarkin Miga da ya zame
musu Jagoran Tafiya, ganin cewa ya fisu
sanin Kasar Hadejia saboda Iyakarsu daya.
Koda suka shirya sai aka Umarcesu da su
shiga Hadejia ta Kudu Maso Yamma, wato
kar su shiga kai tsaye ta yamma. Akan
Hanyarsu ta zuwa Hadejia ne Sai suka
Yada Zango a Kafur, kusa da Hadejia.
Domin su kwana da safe su shiga Hadejia
su Yaki Sarki Buhari. Sai dai da zuwansu
Kafur Buhari ya samu Labari, Ance wani
makiyayi ne yana kiwo ya Gansu, kuma
Har ya bar gurin baiga Iyakarsu ba. Sai ya
rugo ya sanarda Sarki Buhari Abinda ya
gani. Sai Buhari ya Umarci Mayakansa
cewa "Tunda ance Basu da iyaka kuma ga
Magariba ta shigo, mu shirya muje mu
shiga cikinsu ba tare da sun ganemu ba"
hakan sukayi yace Duk Lokacinda sukaji
Dan fatima ya Buga Ganga to su fara
Bugun mayaka.

Haka akayi Mayakan
Buhari suka shimmace su suka shiga
cikinsu ba tare da sun gane ba,Saboda
Garuruwa da dama ne suka Hadu. Ance
wasu mayakan nasu Dauresu akayi wai
dan kar su shiga Hadejia kafin Gari ya
waye. Ashe Ajali ne ya dauresu.
Koda Sarkin Hadejia Buhari yayi shirinsa
yayi Addu'ah sai ya Daga Kai sama.
Sai Dan-fatima ya zuba Kirari:-

(Fasa maza dan
Sambo, Garba Bakin Tandu da Man Madaci,
wanda ake jira yazo, fasa Maza gagara
gasa, sai ya buga Gangar yaki).

Anan
Mayakan Hadejia suka fara bugun
mayakan Daular Sokoto suna kashewa.
Wadansu duk suka razana suka fita a guje
kowa yana kokarin ya ceci Ransa.
Wadanda aka dauresu dan kar su shiga
Hadejia da wuri, duk anan aka kashesu.
Sauran kuwa suka zubar Makamansu suka
Gudu. Dawakai suka Razana, su kuwa
mayakan Hadejia Suna bi suna kashewa
suna kama Bayi.

A SHORT HISTORY OF HADEJIA BY MUSA USMAN MUSTAPHA.

HADEJIA A YAU!According to S.J. Hogben,
Hadejia town was founded in The 15th
Century. The assertion draws some authority
from the manuscript of the Kano chronicles,
where it was stated that, during the reign of
Yakubu Abdullahi Barjo who ruled Kano
from 1452AD to 1463AD. The King of
Machina Algalfati went to Kano with his
three Brothers. Sarkin Kano Yakubu gave
Sarkin Machina Algalfati the right to rule
Gaya and so he became the ruler of the
town. While one of Algalfati's brother went
to Rano where Sarkin Rano appointed him
the ruler of Dal. The second Brother
proceeded to Zazzau, where Sarkin Zazzau
appointed him the ruler of Gayan, And the
third Brother went to Garun Gabas, where
Sarkin Gabas appointed him the Ruler of
HADEJIA.

And established the dynasty which
ruled the town until the outbreak of the
19th century Jihad.
On the basis of this assertion, the town was
said to have been established sometime in
the 15th century, but the tradition which the
assertion was based on, contained certain
short comings which made its authenticity
doubtful. In the first place throughout the
period of our field work, not a single person
mentioned this tradition. And secondly
neither the tradition of Hadejia nor that of
the places (Kano, Gaya, Rano, Dal, Zazzau and
Gayan) mentioned the tradition, connect
their origins with each other.


And finally the fact that one of Algalfati's
brothers was appointed the ruler of the
town in the 15th century did not in any way
indicate that the town was established at
the time. In fact, if any thing, the tradition
only showed that the town was established
earlier than this development because a
ruler can only be appointed to an existing
town not the other way round.


(MUSA
USMAN MUSTAPHA)HADEJIA A YAU!

Friday, September 28, 2012

MUTUWAR SARKIN HADEJIA BUHARI

HADEJIA A YAU!
Bayan Sarkin Hadejia Buhari ya Gama
yake yake kamar yakin Takoko, gamon
kafur da sauransu! Sai ya yanke
shawarar ya fadada Kasar Hadejia daga
Gabas. Kuma a lokacin babu wani Dansa
da ya taso wanda zai bashi wata
sarauta bubba. Dan haka ya Nada
kaninsa Sarkiyo a matsayin Chiroman
Hadejia a shekarar 1863. Da nufin ya
zama Magajinsa, saboda Dansa Umaru
shekarunsa Goma sha Takwas (18).
Buhari yayi Tunanin ya Masa sarauta mai
Girma a Kasar Hadejia, dan haka yayi
kokarin ya masa sarautar Sarkin Auyo,
bayanda ya Kashe Nalara sarkin Auyo
ba'a nada kowa ba! Dan haka yaso ya
nada Umaru a matsayin Sarkin Auyo.
Wato ya kasance ya gajeshi bayan ya
Mutu.
Da wannan kudiri da yake ransa, Buhari
yayi kokarin ya cinye Gogaram (Bedde)
da Yaki don ya Nada kaninsa Chiroma
Sarkiyo a matsayin Sarkin garin. Kuma
dukda yayi haka zuciyarsa daya, wasu
daga cikin 'yan-uwansa sai suka yi
kokarin su baza masa abinda ya tsara!
Dan haka wani daga ciki 'yan-uwan
Buhari sai ya fara yada jita-jita a
tsakanin fadawan Buhari cewa yana so
ne ya kaisu a kashe su don ya cimma
wata manufarsa, su kuma fadawa sai
suka ga Dangantakarsa da Buhari bazai
fadi karya ba sai suka yarda da
maganarsa.
Dan haka fadawa sai suka fara shawara
a junansu ba tare da Sarki Buhari ko
wani ya sani ba, don su yiwa Buhari
tawaye a gun yakin, kuma duk suka
amince da hakan. Bayan kwanaki sai
Buhari ya sanar da fadawa cewa zasuje
suci Gogaram da yaki, amma bai san an
warware masa shirinsa ba. Aka saka
rana Buhari ya jagoranci mayakan
Hadejia don su ci Gogaram da yaki,
sarkin Hadejia Buhari ya shiga Gogaram
ta kofar Garin yamma amma mayakan
Buhari kamar su Sarkin Arewa Tatagana
da Sarkin yaki Jaji da sauran fadawa sai
suka tsaya suka ki su bi Buhari, ko da
ganin Haka sai Buhari ya shiga garin
suka fara dauki ba dadi da Mayakan
Sarkin Gogaram DAN BABUJE. Har suka
sokeshi da Mashi, kuma sai suka fice
daga Garin suka koma Bedde ta yanzu.
Koda mayakan Hadejia suka ga an
raunata Buhari sai suka bisu da yaki,
bayan sun dawo sai suka taho da
Buhari zuwa Hadejia, inda suka yi Gadon
Kara suka Dora shi. Akan hanyarsu ta
dawowa Hadejia Buhari ya musu jawabi
kuma suka fahimci cewa Munafurci ne
akayi tsakaninsu da Buhari. Kuma yace
musu lalle In ya mutu su kaishi Hadejia
su binne shi, kuma Allah ya dauki ransa
a Madaci kusa da Hadejia. Bayan fadawa
sun fahimci 'yan-uwan Buhari ne suka
munafurceshi, sai suka yanke shawarar
cewa dukda Kankantar Dansa Umaru shi
zasu Nada A matsayin Sarkin Hadejia.
Kuma hakan akayi karkashin jagorancin
Tatagana da Jaji. In kazo kayi Gaisuwar
Mutuwar Buhari sai ka Juya kayi
Mubaya'a a gun Sabon Sarki wato
Umaru Dan Buhari. Hadejia A yau.

Thursday, September 27, 2012

MUTUWAR SARKIN HADEJIA BUHARI...

HADEJIA A YAU! Bayan Sarkin Hadejia Buhari ya Gama yake yake kamar yakin Takoko, gamon kafur da sauransu! Sai ya yanke shawarar ya fadada Kasar Hadejia daga Gabas. Kuma a lokacin babu wani Dansa da ya taso wanda zai bashi wata sarauta bubba. Dan haka ya Nada kaninsa Sarkiyo a matsayin Chiroman Hadejia a shekarar 1863. Da nufin ya zama Magajinsa, saboda Dansa Umaru shekarunsa Goma sha Takwas (18). Buhari yayi Tunanin ya Masa sarauta mai Girma a Kasar Hadejia, dan haka yayi kokarin ya masa sarautar Sarkin Auyo, bayanda ya Kashe Nalara sarkin Auyo ba'a nada kowa ba! Dan haka yaso ya nada Umaru a matsayin Sarkin Auyo. Wato ya kasance ya gajeshi bayan ya Mutu.

Da wannan kudiri da yake ransa, Buhari yayi kokarin ya cinye Gogaram (Bedde) da Yaki don ya Nada kaninsa Chiroma Sarkiyo a matsayin Sarkin garin. Kuma dukda yayi haka zuciyarsa daya, wasu daga cikin 'yan-uwansa sai suka yi kokarin su baza masa abinda ya tsara! Dan haka wani daga ciki 'yan-uwan Buhari sai ya fara yada jita-jita a tsakanin fadawan Buhari cewa yana so ne ya kaisu a kashe su don ya cimma wata manufarsa, su kuma fadawa sai suka ga Dangantakarsa da Buhari bazai fadi karya ba sai suka yarda da maganarsa.

Dan haka fadawa sai suka fara shawara a junansu ba tare da Sarki Buhari ko wani ya sani ba, don su yiwa Buhari tawaye a gun yakin, kuma duk suka amince da hakan. Bayan kwanaki sai Buhari ya sanar da fadawa cewa zasuje suci Gogaram da yaki, amma bai san an warware masa shirinsa ba. Aka saka rana Buhari ya jagoranci mayakan Hadejia don su ci Gogaram da yaki,

sarkin Hadejia Buhari ya shiga Gogaram ta kofar Garin yamma amma mayakan Buhari kamar su Sarkin Arewa Tatagana da Sarkin yaki Jaji da sauran fadawa sai suka tsaya suka ki su bi Buhari, ko da ganin Haka sai Buhari ya shiga garin suka fara dauki ba dadi da Mayakan Sarkin Gogaram DAN BABUJE. Har suka sokeshi da Mashi, kuma sai suka fice daga Garin suka koma Bedde ta yanzu. Koda mayakan Hadejia suka ga an raunata Buhari sai suka bisu da yaki, bayan sun dawo sai suka taho da Buhari zuwa Hadejia, inda suka yi Gadon Kara suka Dora shi. Akan hanyarsu ta dawowa Hadejia Buhari ya musu jawabi kuma suka fahimci cewa Munafurci ne akayi tsakaninsu da Buhari. Kuma yace musu lalle In ya mutu su kaishi Hadejia su binne shi, kuma Allah ya dauki ransa a Madaci kusa da Hadejia. Bayan fadawa sun fahimci 'yan-uwan Buhari ne suka munafurceshi, sai suka yanke shawarar cewa dukda Kankantar Dansa Umaru shi zasu Nada A matsayin Sarkin Hadejia. Kuma hakan akayi karkashin jagorancin Tatagana da Jaji. In kazo kayi Gaisuwar Mutuwar Buhari sai ka Juya kayi Mubaya'a a gun Sabon Sarki wato Umaru Dan Buhari. Hadejia A yau.

Wednesday, September 26, 2012

THE 19TH CENTURY JIHAD AND THE ESTABLISHMENT OF HADEJIA EMIRATE.

Hadejia A yau. In assessing the impact of the 19th century Jihadist movement in Hausa land, (a major development in the History of the region), scholars and students of History have agreed that the movement created a political community much larger than any that had existed in the region before then. The process involved the suppression of several sovereign politics that that have developed over several centuries in the area. There was no doubt that internal forces within Hausa land, such as the widening gap between the ruled and the rulers, as a result of the corrupt policies of the later, contributed to this transformation. It is also our belief that the Jihadists (as Intelligensia of the society) served as agents of the internal development that took place in Hausa land at the beginning of the 19th century. But one still needs to ask the question why and how did the Jihadist come to exert such an important historical influence?

The origin of the Fulani Jihadist is a subject that has given rise to many conroversies. One undisputed fact is that some centuries ago they occupied the region of Tekrur, Futa Toro,and Futa Jallon between the Senegal and Niger Rivers. Since then, it is believed that they have been moving Eastward through Massina and the Hausa states toward chad, Fombina and beyond At the time of their movement, an important political development was taking place in Bilad at Sudan, especially in Borno and Kano in the late 15th century, and early 16th century. The period of the Jihadist migration into the above areas is a period of radical political change associated with Mai Ali Ghaji (1470-1503) in Borno and Muhammed Rumfa (1463-1499) in Kano.

The new ideas generated as a result of their policies had brought together people of diverse (descent) linguistic and occupational groups under one umbrella.

(page one).

By Musa usman Mustapha.

Duk mai bukatar Littafin zai iya tuntubar Baba Ali Najo K.liman.

Sunday, September 23, 2012

HISTORY OF HADEJIA

HADEJIA HISTORY
Prior to the rise of the emirate Council in
Hadejia, the territory now known as Hadejia
Emirate or Kasar Hadejia, was made up of
seven separate and distinct kingdoms namely:
Garun Gabas, Auyo, Dawa, Fagi, Kazura,
Gatarwa and Hadejia. Unfortunately, these
kingdoms possessed neither historical
documents nor codified oral traditions which
could throw light on their histories. Our
knowledge of these Kingdoms therefore
remains obscure and scanty. Available oral
tradition tells us that the rulers of each of
these seven Gudiri States received their titles
from, and owed allegiance to the Mai of
Borno through the Galadima, whose seat was
at Nguru. Furthermore, the same tradition
tells us that Auyo and Garun Gabas were the
oldest of the seven Kingdoms. The kingdom
of Auyo together with Tashena and Shira of
Katagum emirate were said to be founded in
about 1400 A.D. by immigrants from
Baghirmi, while Hadejia and probably the rest
of the kingdoms were founded afterwards.
The founders and early settlers of all the
Kingdoms east of Kano, we are told, were
attracted to this area by its richness in terms
of grazing land, fertile landscape. and fishing
streams. Hadejia town, for instance, owed its
name and origin to a Kanuri hunter from
Machina, Hade, and his wife, Jiya, who, while
on hunting expedition, became attracted to
the area because of its rivers and other
natural endowments. Hade became the
founder of Hadejia and the first in a long line
of Hadejia Kings - thirty-two in all who ruled
the area before the nineteenth century jihad.
Unfortunately, the names of only three of
these kings have been preserved – Baude,
Musa and Abubakar (Gowers, 1921). The
town and the kingdom, and indeed later the
emirate, got their name when Hade and his
wife Jiya settled in the area, and the people in
the surrounding settlements started to
migrate to, or identify the area with, them. It
is said that the people often referred to the
settlement as Garin (town of) Hade and Jiya
and later merged the two names and simply
called it HADEJIYA, after the name of the man
and his wife. Be that as it may, what emerged
from the little we know is that Hadejia
together with the six other kingdoms in the
region were all at one time or the other
brought under the control of Borno Empire.
They constituted what the Bornoans called
the "Nguderi or "Gudiri' territories. They
remained under Borno's imperial control up
till the beginning of the Nineteenth Century
when the Fulani conquered them and
subsequently transformed them into what
became known as the Hadejia emirate.
The founders of the emirate were a group of
nomadic cattle herdsmen who were
descendants of one Hardo Abdure. They were
said to have come from Machina in western
Borno in search of grazing land; and by the
end of the 18th century a sufficient number
of them had settled in the area due to the
availability of rich pasture. Accordingly, owing
to the growing number of Fulani
communities in the area, Sarki Abubakar, the
last Hausa King of Hadejia, appointed one
Umaru B. Abdure as Sarkin Fulanin Hadejia in
about 1788.

Tuesday, July 17, 2012

KASAR HADEJIA DA KABILUN CIKINTA


HADEJIA A YAU! Kasar Hadejia tana da kabilu da dama wadanda kuma suke da yarensu daban-daban: kamar...
1, HAUSAWA
2, ABORAWA (FULANI)
3, MANGAWA
4, GIZMAWA
5, BADAWA
6, KOYAMAWA.

1, HAUSAWA:- Kabilar Hausawa sune kabila mafiya yawa a kasar Hadejia Domin su babu wadda zaice ga wani lokaci da suka shigo Kasar Hadejia, kuma tafi karfi a kasar sakamakon dadewar Garuruwansu. kamar Garun Gabas (Biram), Auyo, da Matsa. kuma ko zuwan Bayajidda Garun Gabas yazo ne ya samu Mutanen Garin suna yin yaren Hausa.

2, ABORAWA (Fulani):- Kabilar fulani sun shigo kasar Hadejia tun a Farkon karni na goma sha biyar (15) kuma sun shigo ne daga yankin Massina wasu kuma daga Katsina, kuma sun Taho ne daga Gabar Kogin SENEGAMBIA wato SENEGAL. Sun fara zama ne a Rinde wasu kuma sun Zauna a Jarmari wasu a Marke wasu a Adiyani da Margadu. Kuma ayarinsu ya kasu biyu Inda wasu suka wuce kasar Kano Karkashin Jagorancin Lamido Usman Kalinwama. A Karni na goma sha Tara (19) Wasu fulanin sun sake shigo Kasar Hadejia daga yankin Machina Karkashin Jagorancin Ardo Abdure Dan Jamdoyi. Kuma ance Kafin suzo Hadejia saida suka zauna a Kankiya ta Jihar Katsina. kuma wadannan fulani suke Sarautar Hadejia har zuwa Yau.

3, MANGAWA:- Kabilar Mangawa ko Barebari wadanda mafi yawancinsu suna zaune a Gabas da Hadejia da kuma Arewacin kasar Sun zo ne A karni na goma sha bakwai (17) sun taho ne daga yankin Borno kuma mafiya yawansu sun zo kasar Hadejia ne Tonon Azurfa da Tagullah. Inda kuma daga baya wasu sun shigo kasar Hadejia A lokacinda RaBe yaci Kukawa da Yaki sai suka kaura suka dawo kasar Hadejia, Kamar garuruwan Birniwa, Baramusa, Kacallari, da Sauransu.

4, GIZMAWA:- Gizmawa suma kamar Mangawa sun shigo ne a Karni na goma sha bakwai (17) kuma suma suna zaune ne a yankin Guri, Marma, Lafiya da sauransu kuma suma yarensu kusan kamar barbarci ne saidai wasu kalmomin da yake canzawa.

5, BADAWA:- Kabilar Badawa basu da yawa a kasar Hadejia, kuma suna zaune ne a Garuruwan Iyakar Hadejia da Bedde, Kamar Gayin, Adiyani, Margadu,da Kadira. wasu sun zauna anan ne tun kafin yakin Gogaram. wasu kuma sunce dama anan suke tuntuni. ganin cewa suna iyaka ne da Kasar Bedde.

6; KOYAMAWA:- Kabilar koyamawa suma basu da yawa kuma Dangin Barebari ne, sai dai zanensu ya bambanta. kuma yarensu ma ba iri daya bane. Kuma suna cewa sun taho ne daga Gabas da Sudan. sannan suna zaune ne a Kasar Kafin Hausa, Bulangu, Yayari, koyamari da sauran garuruwan kasar Kafin hausa.

7; TIJJANAI:- Kabilar Tijjanai fulani ne dake zaune a Yelleman kuma Malamai ne masu bin Darikar Tijjaniyya. shi yasa ake ce musu Tijjanai. Sun shigo kasar Hadejia a shekarar 1903, Daga Malo a yankin Tukolar Senegal. sun taho ne bayan Turawan France sun yiwa Yankinsu Mulkin Mallaka. Sun taho karkashin jagorancin Shugabansu Muhammadu El-Bashir, kuma sun fara zama ne a Lokoja. Magajinsa kuma Ahmadu Madaniyyo sai ya sake tasowa daga Lokoja yazo Kasar Hadejia aka basu Wuri suka zauna. wato Yelleman Tijjanai. Alhamdu lillahi. Hadejia A Yau.

Sunday, July 15, 2012

TARIHIN ALH. DANJANI HADEJIA


HADEJIA A YAU! Tun Lokacinda nace zan rubuta tarihin Alh. Danjani Hadejia na samu kiraye kiraye a waya akan cewa ana sauraro na. To matsalar itace muna nan muna tattara Bayanai domin kar muyi garaje bamu kammala ba mu saki. Mai Karatu zaiga na rubuta Tarihin Alh. Danjani Hadejia, Wannan satin in Allah ya yarda zamu Maida Hankali wajen Tarihin Alh. Danjani Hadejia. Da irin gwagwarmaya da yayi. Alh. Danjani yana daya daga cikin Mutanen da suka Daga darajar masarautar Hadejia idan mukayi la'akari da irin gudunmawar da ya bayar wajen ganin Talaka yayi kyakkyawar rayuwa babu Tsangwama daga masu sarauta. Abinda yasa bazamu Rubuta duk tarihin ba sai mun samu Hotonsa wanda yayi da farar riga da bakin takalmi da kuma Jar hula. Hadejia a yau.

Monday, July 9, 2012

TARIHIN KAFUWAR HADEJIA KASHI NA (1)






TARIHIN KAFUWAR Hadejia Ya farune daga wani maharbi mai suna Hade, shi wannan maharbi ya taho ne daga yankin Machina ya yiwo yamma har yazo wannan wuri da yanzu ya zama Hadejia. Lokacin da yazo sai ya iske Daji mai bishiyoyi ga kuma Namun Daji da Tsuntsaye ta ko ina, sai ya zauna yaci gaba da farautarsa har saida wata rana yana tafe da karyar sa sai tayi nisan kiwo ko da tazo sai yaga duk jikinta da ruwa, sai yayi mamakin hakan har ma sai yabi sawunta. Koda yaje sai yaga kogi kuma ga tsuntsaye suna shawagi a wurin. Sai ya yanke shawarar zama a wannan wurin, kuma hakan yayi. Anan ya zauna yayi bukkarsa yake harbe harben Namun daji kuma yayi SU,wato kamun kifi. 

In ya kashe namun daji sai yaje ya sayar da fatun. Harma ya dauko matarsa wato Jia ya dawo da ita wannan wurin. Kuma mutane sai suke zuwa sayen fatu da nama a wurinsa. Duk wanda yazo wurin sai yayi sha'awar zama a wurin, haka nan gari ya fara bunkasa wasu maharba, wasu masinta, wasu kuma mafarauta. Sai gari ya kafu kowa yazo wucewa sai ya yada zango a garin. Kuma makwafta masu zuwa sayen Namun Daji sai suke kiran garin da suna Garin Haden-jia, wato suna masa lakabi da sunan matarsa. 

To kasancewar gari sai da shugabanci ne yasa shi Hade ya zama shugaban garin, duk wanda zaije sayen fatu ko nama sai yace na tafi garin Haden jia.
Wato ana masa lakabi da sunan matarsa. To sakamakon takaita kalma irin ta Bahaushe sai aka dunkule sunan ake cewa Hadejia.

Kuma bayan zamanin wannan mutumin
Hadejia taci gaba da zama gari kuma tare da shugabanci wato mulkin Sarakunan Habawa. Kuma a lokacin akwai kananan Garuruwa masu wadda suke kusa da Hadejia kamar Rubban Dakata, Auyo, Hadagwaigwai da dai sauransu. Wadanda suma suna da nasu sarakunan a wannan Lokacin. Kuma Hadejia sunyi Sarakunan Habe guda talatin da biyu(32),amma sunan mutum uku ake dasu wadanda sukayi mulki kafin zuwan Fulani. 
1, BAUDE 
2,MUSA 
3, ABUBAKAR. 

A zamanin Mulkin Sarkin Hadejia na Habe Abubakar fulani sukazo kasar Hadejia, kuma shine ya basu masauki a Hadejia Lokacin Hadejia tana karkashin Daular Borno, domin tana karbar Umarni ne daga Galadiman Borno. Sarkin Hadejia na Habe shi ya nada Umaru a matsayin Sarkin fulanin Hadejia. Wato kafin Jihadin Shehu usman Danfodiyo. Kuma har yanzu fulanin sune suke sarautar Kasar Hadejia.

A GABA ZAN KAWO MUKU TARIHIN
SARAKUNAN FULANI DA DALILIN KARBAR TUTA DA YADDA SUKA TUNKUDE SARAKUNAN HABE DAGA SARAUTA.

THE ORIGIN OF FULANI (Asalin Fulani)


Who Are the Fulani People? Origins The history of the Fulani seems to begin with the Berber people of North Africa around the 8th or 11th century AD. As the Berbers migrated down from North Africa and mixed with the peoples in the Senegal region of West Africa the Fulani people came into existence. Over a thousand year period from AD 900 - 1900, they spread out over most of West Africa and even into some areas of Central Africa. Some groups of Fulani have been found as far as the western borders of Ethiopia. As they migrated eastward they came into contact with different African tribes. As they encountered these other peoples, they conquered the less powerful tribes. Along the way many Fulani completely or partially abandoned their traditional nomadic life in favor of a sedentary existence in towns or on farms among the conquered peoples.

The nomadic Fulani continued eastward in search of the best grazing land for their cattle. Their lives revolved around and were dedicated to their herds. The more cattle a man owned, the more respect he was given.
Today, some estimate as many as 18 million Fulani people stretch across the countries of West Africa. They remain to be the largest group of nomadic people in the world. What Do the Fulani Believe? Religion and Beliefs:

The Fulani were one of the first African tribes to convert to Islam and are today more than 99% Muslim. The devout Muslim Fulani have seen themselves as the propagators and preservers of the Islamic faith in West Africa from as early as the fourteenth century. Historically it was a Fulani chief named Usuman dan Fodio, along with nomadic Fulani herdsmen who were instrumental in facilitating the spread of Islam across West Africa through evangelism and conquest. At times they would wage "holy wars" or jihad in order to extend and purify Islam. As the Fulani migrated eastward they spread their Islamic beliefs. As they became more powerful and attained more wealth they began to be more aggressive with their religion. 

Their adoption of Islam increased their feeling of cultural and religious superiority to surrounding peoples, and that adoption became a major ethnic boundary marker. Some settled in towns and quickly became noted as outstanding Islamic clerics, joining the highest ranking Berbers and Arabs.

Sunday, July 8, 2012

WAKAR SAUDATU ADO BAYERO






1. Daren jiya ba na yau bane gun kwanan
yaro daban da bubba.

2. Bismillah zana shirya waka sarki Allah
kaban basira inyi wakar saude 'yar nikatau.

3. Ina dada godiya ga Allah sarki shi ya halicci saude.

4. Ga saude sarauniyar kano mai saukin kai ce da son mutane.

5. Ga mai fara'a da son mutane Bata gaji tsiya da tsangwama ba.

6. A kyauta ba kamar ki saude kanwar
sarkin kano na yanzu.

7. Kanwar Sarkin Bichi na yau Nasiru Ado dan uwan ki Saude. 

8. Ga mai haske kamar Azurfa Dadin suna kamar Tagullah.

9. Taurari ko suna da haske basu kai hasken farin wata ba.

10. Inda mata suna sarauta a kano sai mun nada ki saude.

11. A zaria sunyi Quen Amina muma a kano muna da saude.

12. A gabas na dangana da Borno ba
kyakkyawa kamarki saude.

13. A yamma najeni har Ilorin ni banga ba
wadda tayyi saude.

14. A nan kudu har zuwa Adamawa banga ba wadda tayi saude.

15. A arewa na dangana Nijar duka babu
Diyar da tayi saude.

16. Kai duk matan dake Kano nai jam'i duk ba kamar ki saude.

17. Hotonki ana comment akanshi na kirga Comment dubu a yanzu.

18. Ga allura cikin duhu sai mai zurfin
hankali ka tsinta.

19. Ga saude bakin zare a matoya sai mai
hankali ka tsinta.

20. Ni burina a duniya inga kina mulkin
kano sa'ade.

21. Allah ba yadda bai iya ba a zazzau shi ya bai Amina.

22. A Ingila ga Elizabeth nan Allah shi zaya baiwa Saude. 

23. Ansa giwa cikin zubo taci guda bakin
rabonta kelau.

24. Allah in yai nufi ga iko nai babu abinda
zai hana shi.

Friday, July 6, 2012

THE ESTABLISHMENT OF SOME OF THE OLD SETTLEMENTS IN HADEJIA EMIRATE


HADEJIA A YAU!
We are severely constrained in the producing a coherent, meaningful and definite pattern of the process of the evolution of Hadejia emirate due to the limitation by our main source-oral tradition. Most of the traditions collected hardly touch on the process of the evolution of Kasar Hadejia. But in spite of this difficulty, we intend to take a second look at the source through a new-interpretation in the hope of coming out with a better understanding of the process of the evolution of Hadejia emirate. Towards this end, we shall attempt to discuss the process of the evolution of certain Old settlement in the emirate, with a view to paving way towards grasping the process of the evolution of Kasar Hadejia as whole.

Prior to the jihadist conquest at the beginning of the 19th century, the territory now known as Hadejia emirate consisted of several separate and distinct Kingdoms whose rulers received titles from and owed allegiance to the Habe Galadima of Borno.

The former Habe Kingdoms included Auyo,Garin Gabas(Biram),Hadejia,Kazura,Gaturwa,Marma,Dawa and Fagi. The process of the evolution of these Kingdoms of seems to be obscure except perhaps for the Kingdoms of Hadejia,Auyo and Garin Gabas.

At the time of the foundation of Hadejia,a number of small settlements were said to have existed in the territory that came to be known as Hadejia emirate. For example,on the North-eastern side of Hadejia town, there was Madagwaigwai, whose present site is near Rubban Dakata a village about 10kilometres east of Hadejia Kiri kasamma road. While on the eastern side of the town was Maskangayu (kulunfardu), a village said to have been established by Damagarawa immigrants whose ancestors now live in Hadejia (ILALLAH).

The old site of Kulunfardu was located near Tandanu, just by the valley of River Hadejia, about 15kilometres from TURABU.

There was a tradition in Turabu which said that, at the side of kulunfardu, there was a large Tamarind (Tsamiyar linzamai) whose branches were said to have bent due to the weight of the Luggage of soldiers of Mai Ali of Borno when they camped there on their way to attack Kano during the reign of Sarkin Kano Muhammadu Kambari Dan shariff(1731-1734) By the western side of Hade's camp was KADIME (still located to the site) which was about 9kilometre from Hadejia. By the Northern side of Hadejia was Majeri a few kilometre from Mallam madori, and by the southern side were Auyakayi(Tunawa), Unik(Arki), Majawa and Auyo.

These settlement were clearly established in the surrounding areas much earlier than Hadejia town.
End of page One.

A short History of Hadejia 1800-1906. By Musa Usman Mustapha.
Ana saida shi a k.liman.

Thursday, July 5, 2012

SARKIN HADEJIA BUHARI DA WAZIRIN SOKOTO A KATAGUM KASHI NA (2)

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU!

A kashi na farko kunji yanda Buhari suka kare da Wazirin sokoto da Mutanen Katagum: da kuma komawar sarki Buhari shabawa wato iyakar Hadejia da Gumel da kuma Damagaram.

YAKIN TAKOKO:- Bayan an Nada Ahmadu a matsayin Sarkin Hadejia, sauran Magoya bayan Buhari sai suma suka bar Hadejia suka koma Shafowa inda Buhari yake suka zauna tare. Sarkin Hadejia Buhari anan ya zauna tsakanin Takoko da Shafowa a Arewacin Hadejia da mutanensa kuma yake tafiyar da wannan yankin. Kuma iyakar Hadejia ce da Damagaram da Machina ta Arewa maso Gabas wato yankin Niger da kuma Borno. Kuma Buhari ya bada Gudun mawa sosai a wannan Yankin wajen Maidasu Musulmi. Inda yayi ta jihadinsa a yankin, kuma a wannan zama da yayi a Shafowa Buhari ya samu kyakkyawar dangantaka da Sarkin Machina da kuma Shehun Borno Umar wanda ya mulki Borno a wannan shekara (1835-1880) wannan dangantaka ta kara baiwa Buhari karfin gwiwa.


A shekarar 1851, Sarkin Musulmi Alu Bubba ya yanke shawarar daukan matakin Karshe akan Buhari, saboda yana tunanin Shehun Borno zaiyi amfani da Buhari ya rusa Daular Sokoto saboda ya zame musu Barazana a Arewa Maso Gabas. A wannan lokacin kuma DanGaladiman Sokoto ya hada Mayaka daga Hadejia,Kano,Katagum,Misau da Jama'are zuwa shafowa.

A wannan lokacin kuma Buhari ya fita kudu da shafowa shi da Sarkin Machina yana garin Takoko shida Jarumansa. A lokacinda Dangaladiman sokoto suka fito su yaki Buhari sai ya zabi Sarkin Jama'are Samboli ya jagoranci yakin, saboda shi ya fisu sanin Yankin. A ranar da zasu yaki buhari kuma a ranar Buhari ya shirya mamaye Garuruwanda suke kudu da Hadejia, sai aka hadu a Garin Takoko. Yayin da aka hadu aka gwabza fada Buhari yaci Galaba a kansu duk suka gudu, Sarkin Hadejia Ahmadu yayi kokarin ya Gudu Kasar Kano amma sai Barde Risku ya bishi ya Kashe shi.

Bayan Yakin Takoko yazo karshe kuma an kashe Sarkin Hadejia Ahmadu Amma ba'a son ran Buhari ba kuma aka masa Sallah aka kaishi Hadejia aka binne shi, sannan sai Buhari ya koma Hadejia yaci gaba da Mulki. Sakamakon wannan yakin, dangantaka ta sake baci tsakanin Hadejia da Sokoto, kuma Sarkin Musulmi yaki yarda da ya nada Buhari Sarkin Hadejia. Sai ya nada Tukur Na yayari, kanin Sarki Ahmadu kuma yace ya zauna a Mashama a Kasar Katagum a Matsayin sarkin Hadejia ya Gaji wansa Ahmadu. Amma Tukur bai yarda ya zama Sarkin Hadejia ba saboda yana tsoron Buhari, sai yaga bazai iya yin haka ba. Kuma saboda Gudun kar Buhari ya kasheshi sai Tukur ya Gudu daga Mashema yayi kaura zuwa Kano Lokacin Sarkin Kano Usman Na1(1846-1855) Sai aka Turashi ya Mulki Yayari a Kasar Birnin Kudu. (Yayarin Tukur) Tukur ya zauna acan Har zuwa lokacinda ya Mutu 1909. Buhari kuma yaci gaba da mulkin Hadejia yana kai hare hare a matsayin Jihadi Har saida yakai Gabasawa,Sankara,Ringim da Kuka kwance A Arewa maso yamma. A Kudu saida ya mamaye Kununu,Takalafiya, Kafin baka, Doma, Ruba, Itas da Kwanda. A Gabas kuwa saida ya Mamaye Babuwari, Kazura, Dawah, Gatare da Margadu. Saida Sarki Buhari ya fadada kasar Hadejia tafi Ko ina fadin Kasa a karni na19.

GAMON KAFUR:-

Tuesday, July 3, 2012

DAJIN DUHUN KARO A HADEJIA.



HADEJIA A YAU! 

DUHUN KARO:-duhun karo wani Daji ne dake kasar Hadejia kuma yafi yawa a Gabashin Hadejia. Wannan Daji daji ne mai Dimbin tarihi wadda duk wadda yake kasar Hadejia zaice maka haka ya taso yaga wannan Dajin. Hasali ma wadda ya kafa Hadejia (HADE) ni'imar wannan Daji ce tasa ya zauna a wannan yanki. Dajin Duhun Karo yana tafe ne da Ruwa a Gefensa sannan ga Itatuwa masu bin Danshin ruwa a gefen ruwan, Kuma wannan dajin ya taso ne tun daga Falgore yamma da Kano har ya dangana da komadugu ta Jihar yobe, sannan ya nufi Jihar Borno har zuwa Tafkin Chadi.

Wannan Daji ya kasu da yawa a Kasar Hadejia inda ya bazu kuma yafi girma da Ni'ima a Yankin Baturiya da Gabta da yankin Kadira har ya shiga zuwa Kasar Gorgaram.   Duk wadda ya saba bin hanyar kano ta Ringim zai ga wannan dajin musamman kwanar Auyo zuwa Hadin mai dan karofi inda nan ne ya fito har bakin titi musamman ma Burtalin fulani na Wajedu, sannan shine ya shiga Muhimbira har fateka zuwa Bubbar Riga yayi Gabas har Sansanin Sarkin Damagaram Tanemu. 


Na shiga wannan Dajin kuma banda kukan tsuntsaye da Namun daji babu abinda kake ji. Nayi tafiyar kilo meter takai biyar a cikin dajin, har saida ya Kaini Askandun fulani da Akurya, na gamu da wani Bafulatani mai suna Musa kuma na tambayeshi shekarar sa nawa a wannan dajin? Sai yace shima anan aka haifeshi, kuma yanzu shima yana da 'ya'ya wadanda ya haifa a wannan Dajin. Na tambayeshi ko zai bani labarin wannan dajin? Sai yace ya tashi yaga Kuraye suna zuwa suna razana musu shanu, kuma yace akwai Namun daji kamar Gada, Barewa, Bauna da dai sauransu. Amma tunda aka fara sarewa dajin sai sukayi nisa kuma da 'yan farauta da suka damesu. Yace Amma har yanzu akwai kananan Namun daji kamar Zomo, Guza, kuma wani lokacin ana samun Gada. Tsuntsaye kuwa dukda harbi da ake Har yanzu akwaisu da dama.
Dajin in ka shiga cikinsa baza kasan ana rana ba saboda tsabar Inuwa da take ciki kuma ga Ruwa a gefensa. Akasarin bishiyoyin da ke dajin farar kaya ce da kuma Bishiyoyi kamar su Danya, Darbejiya, Gabaruwa, Kirya, Kanya, Magarya,  da sauran bishiyoyi masu Ni'ima.


Kalu balenda wannan Daji yake fuskanta shine Sare saren Bishiyoyi da ake yi a cikinsa da kuma fadada Gonakai da makwaftan dajin sukeyi. Ta wani fannin kuma akan samun wasu suna kunna masa wuta. Amma dukda haka in ka shiga zai baka sha'awa. Na tambayi wani dattijo mai suna Garba Tandanu mai shekara 60, yace wannan dajin yasan lokacin da kuraye suke Hanasu zuwa Hadejia ta Rugar Isa inda sai sun zagaya ta Tuwankalta sannan zasuzo Hadejia Amma yanzu sai dai tsuntsaye da kananan namun daji. HADEJIA A YAU.

Sunday, July 1, 2012

KASAR HADEJIA ZAMANIN SARKI ADAMU




HADEJIA A YAU! Hadejia tana daya daga cikin Garuruwan da ke Karkashin Tutar shehu Usman Danfodiyo! Jama'ar Hadejia Akasarinsu fulani ne da Hausawa da Mangawa. Kuma Suna bin Addinin Musulunci ne. Idan muka tabo Tarihin Hadejia tun lokacin mulkin Habe zamuga cewa dama ko a wancan lokacin Addinin Musulunci ne addinin mutanen Hadejia sai dai dan abinda ba'a rasa ba. Kafin a jaddada addinin Musulunci lokacin shehu dan fodiyo sarakunan Habe ne suke Sarautar Hadejia, kuma anyi sarakuna da dama kamar (1)Baude(2)Musa(3)Abubakar. Bayan Malam Sambo ya karbo tuta karkashin jagorancin Sarkin fulani Umaru sai Hadejia ta koma Karkashin mulkin Fulani.
HADEJIA A YAU! A yau Hadejia ta zama wata fuskar kasuwanci a jihar Jigawa, domin duk abinda ka sani na sayarwa zaka samu a wannan gari. A shekaru Hamsin baya In ba ranar Kasuwar Garin ba wani abin bazaka samu ba. Allah ya albarkaci Hadejia da kayan Lambu Irinsu Tumatir, Tattasai, Attaruhu, da sauransu. Wadannan ana yinsu ko wane lokaci a Hadejia ba sai da damana ba. Saboda Albarkar kogi da Allah ya bamu. Haka kuma fannin kayan Abinci kamar shinkafa,Alkama,Masara. Duk ba sai da damina akeyinsu ba a Hadejia. Saboda Albarkar da Allah ya bamu ta kasar Noma mai kyau. Idan muka koma batun Amfanin Abinda ke cikin Ruwa Hadejia A kullum Tana Fidda kifi kimanin Na Naira milyan Biyu a takaice! Wani abu da yake shine Kalu bale a garemu shine.........