"" /> HADEJIA A YAU!: 2021

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Thursday, December 9, 2021

FURYAN HADEJIA...

HADEJIA A YAU!

TARIHIN FURYAWA


1.0 JADAWALIN WANDA SUKA RIKE SARAUTAR

 1. Furya Sakaina

(1760 – 1804)

2. Furya Muhammad Tsangwai
(1804 - 1810)

3. Furya Muhammad Ganuwa
 (1810 – 1856)

4. Furya Muhammad Babaru
 (1856 – 1860)

5. Furya Abubakar Sadik (1860 - 1906)

6. Furya Muhd Sani Babale (1906 - 1940)

7. Furya Muhd Tukur (1940 - 1946)

8. Furya Usman Kunkun (1946 - 1950)

9. Furya Muhd Mustapha (1950 - 1958)

10. Furya Abdullahi Tukur (1958 - 1997) 

11. Furya Muhd Danyaro (1997 - 2020). 

12. Furya Abdullahi Muhd (2020 to date).

2.0 TARIHI DA ASALIN FURYAWA

Asalin Furyawa fulani ne na kasar Borno wato Fulata Borno, ance mutanen kasar Machina ne wadda take Jihar Yobe a yanzu, mutane ne wanda suka kware a yaki sosai. Dalilin da yasa suka yiwo kaura daga inda suke shine, shugabansu wanda akafi sani da Sakaina dan Sarki ne bayan rasuwar mahaifinsa ya nemi sarauta a maimakon a bashi sai aka bawa kaninsa, a sakamakon haka ya debi magoya bayansa suka dawo wani gari da ake cewa Rinde. Furya tare da wani bufulatani ana ce masa Gurunde (shima da Jama’arsa) sune fulanin farko da suka fara zama a Rinde kuma Furya shine shugabansu wato ma’ana Furya Sakaina shine ya kafa garin Rinde shine kuma kamar Sarkin su a wannan lokacin.

Bayan rasuwar sarki Umaru Furyawa sun baro Rinde sun dawo Hadejia ta yau. A sakamakon gayyata da Sambo yayi musu bayan ya gaji dan uwansa Umaru a sarauta sun kafa gidansu ko unguwarsu dab da ganuwar Hadejia ta gabas kuma ana kiran wajen da unguwar Furya a yanzu kuma ‘Yan koli. 


Hakazalika, akwai ahali da ‘yayan ‘yanuwan Furya da suka rungumi sana’ar yaki bayan barinsu kasar Machina, shahararre a cikinsu shine Dan Furya wanda ya taya sarkin Gumel Habu Nakata yaki a garin kanyar maikaho ya kori shararren mayakin nan wato Danwaire. Daga baya sarkin Gumel ya bashi sarautar garin magajiya ta kasar Gumel a yanzu haka akwai hakimi da ake kira dan Furya a Gumel. Bayan nan Dan Furya ya koma Kano wajen sarkin Kano Alu yaci gaba da tayashi yaki, shima ya nadashi sarauta a garin Ringim bayan ya mutu dansa Musa ya gajeshi. A yanzu haka ana kiran dagacin Katutu ta garin Ringim da Dan-Furya, hakazalika akwai sunan unguwa Dan Furya House a Katutu Primary School Ringim.

         3.0 DANGANTAKAR FURYAWA           DA GIDAN SARAUTAR FULANIN HADEJIA

Lokacin da Umaru ya baro dan uwansa Sambo a Taurako (Digimsa) sai yayi yamma bai zame ko’ina ba sai Rinde. Furya da Gurunde sune shuwagabannin garin wato manyan Rinde sune suka bashi gida a tsakaninsu wato kowannesu ya matsa shi kuma yayi gida a tsakiyarsu. Daganan ya koma wurin Sambo ya dauko matarsa tare da shanunsa da sauran dabbobi.

Lokacin da Umaru ya kira sauran ‘yan uwansa Fulani yayi musu maganar kaiwa caffa ga Shehu Usman Danfodia sai suka nuna masa suna tsoron wulakancin sarkin Auyo Jibrin Uban Nalara, bugu da kari kuma sun shagalta da sha’anin kiwon shanunsu da sauran dabbobi. Asakamakon haka Umaru yace musu to ni zanyi aike wajen Shehu.

Umaru ya tura mutum shida Sokoto wajen Shehu Usman Danfodio, mutanen sun hada da: (1) Furya (Shugaban tawaga) (2) Gurunde  (3) Zatanku (Bawansa ne) sai kuma sauran Rindawa mutum uku wanda ba’a fadi sunansu ba.

Bayan sunje sun isar da sakon Umaru wajen Shehu sai Shehu yace na karbi caffarsa saboda haka ga tuta kukai masa. Ya kuma ce su fada masa idan yaje kowane gari ya daga tutar da ikon Allah zasu yarda dashi su kuma bishi. Da suka dawo daga Sokoto suka zo da sakonnan na Shehu ga Umaru. Sai Umaru ya sake tara Fulani yace dasu “Ga Furya da Gurunde da zatanku da mutum uku mutanen gari dana aikesu wurin Shehu sun dawo amma sunzo mini da tutar Musulunci” Bayan ya fada musu sakon Shehu daganan suka fara fita Jihadi zuwa makwabtan garuruwa kamarsu Akurya, Asuwari, Abartayin, Tashena da dai sauransu duka tare da Furya, Rindawa da sauran Fulani ‘yan uwansa.

Bayan rasuwar sarkin Fulani Umaru sai aka aikawa Shehu labarin rasuwar. Shehu Usman ya turo wazirin Sokoto domin yazo yayi ta’aziyya ya kuma nada sabon sarki. Lokacin da yazo ya sauka ne a Rinde garin da sarki Fulani Umaru yake zaune. Fulani suka taru waziri yayi musu ta’aziyya amma a lokacin Sambo bai samu labarin zuwan waziri ba yanacan Mairakumi inda gonarsa take.

Da waziri ya kwana bakwai sai yace wa su Furya (Rindawa) a aikawa Fulani suzo don muyi shawara dasu akan wanda za’a zaba ya zama shugaba (wato sarki). Bayan duka sun hallara sai furya da jama’arsa suka lura Sambo kanin Umaru baya cikin wadannan manyan fulanin, kuma ba’a kula a kirashi bama, saboda haka cikin dare sai Furya, Gurunde da mutum biyu suka tafi wurin Sambo a sirrance suka ce masa yazo su tafi Rinde saboda anyi baki daga Sokoto, sai Sambo yace musu “mezanyi idan naje?” suka dai matsa masa suka kuma nuna masa rashin jin dadinsu kasancewarsa baya wajen, ganin ransu ya sosu shine ya amince ya biyosu Rinde, da isowarsu garin suka shiga gidajensu ta kusfa (A boye) saboda basa son agane sune suka kirashi, shi kuma ya biyo ta kofar gari ya iske su waziri da sauran manyan Fulani a rumfar kofar masallaci.

Da zuwansa sai Jimagara (Kawun Sambo) yace da waziri, “To ga wanda muke jira yazo, amma fa bamu aika masa yazo ba amma gashi Allah ya kawoshi” (saboda basu san su Furyane suka kirashi ba). Da jin haka sai waziri ya fidda takardu na kuri’a guda goma wanda Shehu ya bashi saboda gudun rigima. A takaice dai Allah ya taimaki Sambo yaci kuri’ar zama sarki, waziri kuma ya koma Sokoto yayiwa Shehu Usman bayani.

3.1 DANGANTAKAR AURATAYYA

Haka zalika, tarihi ya nuna akwai dangantakar auratayya tsakanin Umaru da Furyawa. Furya Tsangwai ya aurawa sarkin Fulani Umaru ‘Yarsa kuma sun haifi diya mace tare wadda aka sa mata suna Gabdo. Ita kuma Gabdo ta auri sarki Garko dan Sambo sun haifi ‘ya wadda ake kira da Maryam (Furatu).


4.0 ASALIN SARAUTAR FURYA DA AIKIN SU A MASARAUTAR HADEJIA

Kalmar Furya sunane na wasu Ahali ko haula a kasar Machina (kamar yadda bayani ya gabata). Sunan Furya ya zama sarauta a kasar Hadejia tun lokacin da Furya Tsangwai kanin Sakaina ya nada sarkin Fulani Umaru sarki bayan Shehu Usman Danfodio ya basu tutar musulunci da Jahadi. An zabi Furya ya nada sarki Umaru sakamkon shine shugaba a Rinde bugu da kari shine ya jagoranci tafiya Sokoto karbo tuta wajen Shehu Usman Danfodio. Tun daga wannan lokaci zuri’ar gidan Furya suke nada sarki a Hadejia harya zuwa yau. A sakamakon haka ake kiran duk wani mai nada sarki a Hadejia Furya. Haka zalika bayan sarki Sambo ya hau gadon sarauta ya sake tabbatar da sarautar furya ma’ana furya tana daya daga cikin manya-manyan sarautu tara da ya fara yi, sarautun kuwa sune:

1.     Sarkin Auyo (Yusufu, Kaninsa)

2.     Garko (Ciroma, Babban Dansa)

3.     Furya (Rindawa)

4.     Galadima (Mangawa)

5.     Madaki (Fulanin Sambo)

6.     Ma’aji (Fulanin Damagaran)

7.     Maidala (Auyokawa)

8.     Sarkin Yara (Fulanin Sambo)

9.     Sarkin Wanzamai (Auyokawa)

A takaice aikin Furyawa a masarautar Hadejia shine nada sabon sarki da hakimansa idan bukatar hakan ta taso, a sabili da haka ake yiwa Furya kirari da “Duk Mainan (Dan sarki) daka dafa kansa ya taka gacci”. Yana da kyau a sani, a tarihin Hadejia Furya shine kadai wanda sarki yake nadawa da hannunsa.

Bayan haka, yaki yana daga cikin aikin Furyawa a kasar Hadejia, sune akan gaba idan yaki ya tashi sabili da kasancewarsu jarumai kuma yakin sana’arsu ce, a sakamakon haka ake musu kirari da “Bahago tausa dama, jinni tsar Bahago”.

5.0 JADAWALIN MUTANEN DA SUKA RIKE SARAUTAR FURYA DA SHEKARUN DA SUKA YI

Furya Sakaina shine ya fara yin sarki ko shugaba a garin Rinde, a kiyasi ya kafa garin Rinde wajajen shekarar 1740 wanda sun zauna ne a karkashin mulkin sarkin Auyo. Bayan rasuwarsa sai Furya Muhammadu Tsangwai ya karba, shine Furya na farko daya fara nada sarki Umaru a matsayin sarkin Fulani bayan sun karbo tutar musulunci daga wajen Shehu Usman Danfodio, ya fara sarauta daga (1804 – 1810).

Bayan rasuwarsa sai Dansa Muhammadu Ganuwa ya gajeshi a shekarar (1810 – 1856) Furya Muhammadu ya samu lakabin Ganuwa ne a sakamakon jagorantar ginin ganuwar Hadejia da yayi. Sarki Sambo ya dora masa alhakin kula da aikin ginin, ance shine mai alhakin yankawa kowane gida iya ginin da zasu yi sannan ya kula da aikin. Haka zalika tarihi ya nuna furya Ganuwa yayi fice a fagen jarumta da sanin dabarar yaki kasancewarsa barde, ya halarci yaki da dama tare da sarki Sambo. Hakazalika ya nuna bajinta da kwarewa a lokacin da akayi yaki da Katagum a zamanin sarkin Hadejia Buhari, sabili da irin bajintar daya nuna sarki Buhari yayi masa kyautar Gandun noma a gabas da Hadejia wanda ya fara tun daga kofar gari ta gabas har zuwa tandanu, ana kiran gandun Gudarin Furya.

Bayan rasuwar furya Ganuwa sai dansa Muhammadu Babaru (Furya Babaru) ya gajeshi daga shekarar (1856 – 1860). Bayan rasuwarsa ne ‘ya’yansa Guda Biyar suka gajeshi daya-bayan-daya, kuma ya rasune kafin zuwan turawa.

Babban dansa Abubakar Sadiq (Furya Sadi) ya gajeshi a shekarar (1860 – 1906) ya kwashe shekara arba’in da shida yana sarautar Furya yayi mutuwar shahada tare da sarki Muhammadu Maishahada a yakin turawa da akayi a 1906. An kawo sunansa a wakar da akayi ta shahadar Hadejiawa wadda Alhaji Ibrahim Katala ya rubuta a baiti na 32 inda yake cewa “Furyan Hadejia shi da Bori na Salihu kofar gabas suka fadi nan aka cim musu”.

Bayan shahadarsa sai kaninsa Furya Muhd Sani Babale ya gajeshi daga shekarar (1906 – 1940). Bayan rasuwar furya Babale sai Dan’uwansa Furya Muhd Tukur (Furya Tukur) ya gajeshi daga shekarar (1940 – 1949).

Bayan rasuwar furya Tukur sai kaninsa Usman Kunkun ya gajeshi ya fara daga shekara ta (1949 – 1950). Bayan rasuwar Furya Kunkun sai aka bawa kaninsa Muhd Mustafa sarauta, ya fara daga shekara ta (1950 – 1958).

Bayan rasuwar Furya Muntsafa sai aka nada dan dan uwansa Furya Abdullahi Tukur sarauta (Furya Tumalle). Ya fara sarauta daga shekara ta (1958 – 1997). Bayan rasuwar Furya Abdullahi sai dansa Furya Muhammadu Abdullahi Danyaro ya gajeshi a shekara ta 1997 wanda shine akan gadon sarauta a yanzu.

A takaice aikin Furya a masarautar Hadejia shine nada sabon sarki da kuma hakimansa. Kuma yanada kyau a sani, a tarihin Hadejia Furya shi kadaine wanda sarki yake nadawa da hannunsa idan sarautar ta fado. 

Ismaila Muhammad Danyaro. 

References

1.     Tarihin (Fulanin) Hadejia by Ma’aji Amar for Hadejia N.A (1956).

2.     Kasar Hadejia by Muhammad Ilallah for Hadejia N.A (1956)

3.     Three Nigerian Emirates: A study of oral history. (Victor N. Low, 1965 P. 134).

4.     Verbal interview with Furya Abdu, Baba Ubali, Baban Juji and many more among elders of the family.

5.     Kano daga Garko “Tarihin sarautar Kano” by Muhd Uba Adamu, Najib Hussain Adamu, Prof. Muhd Sa’idu Gusau.

6.     Kano history and culture bureau Archive.

 


Saturday, October 9, 2021

ARAB'S ORIGINS AT GARUN-GABAS. BY F. W. H. MIGEOD.

HADEJIA A YAU!

Arab Origins at Garun Gabbas.

By F. W. H. MIGEOD... 1911..




A noticeable feature among the peoples west of Lake Chad is that many claim an origin from Arabia and chiefly Yemen.This means little more than that a leader arose who migrate a number of followers by slave raiding and the prospect of loot, in the same way as Rabeh did at the end of the 19th century. The legends of this stream of migration are so persistent that an authentic genealogy proving it in at least one instance is of value in support of the general claim; and this is supplied by the town of Garun Gabbas. Many of the migrations appear to have had their origin in the refusal of certain persons and families to accept Mohammedanism, but whether the Arab tribes on the eastern side of Lake Chad owed their presence there to the same cause is another matter. In any case, Arab infiltration across Africa from the Red Sea and the Nile to Lake Chad did not begin in recent centuries.


 The small town of Garun Gabbas is about 12 miles north of Hadejia. The present Bulama or Headman (Bulama is a compound Bornu word, meaning Town Headman) named Musa claims to be of Arab descent and of a long line of kings. In appearance he is jet black, but with white whiskers, and I found nothing to distinguish him from a pure negro, except, perhaps, some slight difference of manner. One felt there was a distinction. He said he was not a Shuwa Arab, the Arab tribe living to the south of Lake Chad, but an Arab from Sham, ie., Syria, and the line of migration of his ancestors was Sham, Kanem, Bornu, Kulumpardu or (Kulunfardu), and thence to Garun Gabbas. His wife was Fula and his children by her spoke the language of their mother. His mother and grandmother were both Bornuese. He went the pilgrimage to Mecca before Rabeh's time, and was 5 years away, he reckoned his present age of 55.



The founder of Garun Gabbas was one Ibrahim, and members of the same family went and founded the now more important city of Daura. Inhabitants of Garun Gabbas wore possibly largely Arab, the leader of the colonists was a Beriberi (i.e. Bornuese), known to them by the name of Zanoa, but his real name was not known. Zanoa's family no longer exists. The reason of the migration out of Bornu was that Ibrahim had a dispute with Mallam Mukhtar, his elder Although the early brother. He came along peacefully and there was no fighting. Although a Beriberi was the leader of the colonists, Garun Gabbas was never under the rule of Bornu. Nevertheless the inhabitants are said to have used the Kanuri language (the language of Bornu) in the days before the founding of Daura, the date of which I have not been able to ascertain with any degree of acouracy. 



The reason probably was that owing to the preponderating influence of the Bornu empire as far back as the thirteenth century, and possibly earlier, the Kanuri language became and still is very widely used. In any case the Bornu influence is reputed to have been very strong in Garun Gabbas. An unexplained detail is why Zanoa does not appear in the list of kings. There are twenty of the ancient families said to be still represented in the country. Some of the inhabitants had in recent years married Beriberi women, but Beriberi men had not settled there in great numbers. The Town is now very small compared with what it was formerly. The present population is Fula, it had spread even to within a few miles of Kano.


Garun-gabas is a small town compared with what it was formerly. The present population is Fula, Awuyokawa (related to the Bedde), and some Beriberi, the Fula being in the largest numbers. The old record of the kings was burnt accidentally six years ago (say 1916). I was told, but a new one had been written out containing all they could remember.


In the original list was the number of years each king had reigned, but they could not be reproduced. The first on the list is Ibrahim who came out of Bornu, it is said they were Mohammedans then and brought horses and asses, but not cattle. 


 As to the town, the old mud wall is now scarcely discernible. The Headman's house is surrounded by a high mud wall, but all the other houses are of grass and circular in shape. There are some baobab trees about that at the rest house being 35 feet in circumference. The soil between Hadejia and Garun Gabbas is dark grey clay, except where crossed by the numerous east to west sand ridges. On the low ridge on which stands the rest house lies a little quartz gravel of very small size, which was the first i had seen on my westward journey from Lake Chad. A depth of twenty-two fathoms.



LIST OF KINGS OF GARUN GABBAS FROM A MANUSCRIPT. 


ARABS…. 

1. Ibrahim
  1. 2. Maji

  2. 3. Kulada

  3. 4. Yerima

  4. 5. Kimeri

  5. 6. Donkofo

  6. 7. Jatou

  7. 8. Amale

  8. 9. Mammadu

  9. 10. Donko

  10. 11. Yahaya 

  11. 12. Dan Asawa

  12. 13. Aburi

  13. 14. Sakaina

  14. 15. Musa

  15. 16. Kujeilu

  16. 17. Adam

  17. 18. Aliyu

  18. 19. Tagwoi

  19. 20. Jimami

  20. 21. Balikurugu

  21. 22. Issaku


FULANI...

 23. Baruwei 

24. Gauyama 

25. Bouri 

26. Ousmanu 

27. Abdu 

28. Abdu 


SLAVE OF KING OF HADEJIA. A pagan.. 


29. Baluwa


ARABS grandfather of present man. 


30. Muhamman Bako


FULANI… 


31. Tukur 

32. 

Buba 

33. Kawu 

34. Alhaji Abubakar. father of the present man 

34. Musa. Present man 1922.



Reference....... MAN A MONTHLY RECORD OF ANTHROPOLOGICAL SCIENCE.

PUBLISHED UNDER THE DIRECTION OF THE ROYAL ANTHROPOLOGICAL INSTITUTE OF GREAT BRITAIN AND IRELAND.

PUBLISHED BY THE ROYAL ANTHROPOLOGICAL INSTITUTE 50, GREAT RUSSELL STREET, LONDON, W.C.I. General Agent: FRANCIS EDWARDS, 83, High Street, Marylebone, W.l,New York Agents: Messrs, G. E. STECHERT & Co.










Tuesday, June 15, 2021

GANUWAR HADEJIA DA KOFOFIN TA...

HADEJIA A YAU!










Garin Hadejia gari ne wadda ganuwa ta kewaye shi, sannan yana da kofofin shiga guda biyar. 

In muka duba Report din Lugard akan Africa wanda yace "Duk kasar Hausa babu gari kamar hadejia wajen jarunta da rundunar mayaka majiya karfi, akwai ganuwa a zagaye da garin masu kofofi guda biyar masu karfin gaske wanda harsashin bindiga bazai iya fasa kyauran kofar ba." Lugard Ya rubuta wannan magana acikin (kundin Najeriya ta Africa shafi na 247). Wanda yake ajiye a dakin da ake ajiye kayan tarihi na Najeriya ta Africa a Arewa House Kaduna.

A wata wasika da Captain Philips H. C. B. ya rubutawa Colonel Larymore ranar 17 December, 1903. Inda yace. 
 "HADEJIYA BUBBAN GARI NE SOSAI KUMA TANA DA GAWURCACCIYAR GANUWA MANYA-MANYA MASU KYAU SOSAI A  ZAGAYE DA GARIN MAI TSAWO KIMANIN KAFA TALATIN GABA DA BAYANTA, TA KO INA A ZAGAYE DA ITA AKWAI KOFOFI GUDA BIYAR KADAI, ITA KANTA GANUWAR KAURINTA YA KAI KAFA TALATIN DAGA KASA. KYAMAREN KOFOFIN MASU KARFI NE SOSAI YADDA HARSASHIN BINDIGA BAZAI IYA FASA SHI BA CIKIN SAUKI, YAWAN JAMA'AR DA KE CIKIN GARIN SUN KAI KIMANIN DUBU TAKWAS ZUWA DUBU GOMA. FADIN GANUWAR GARIN YA KAI KIMANIN MAYIL HUDU DA RABI. GARIN ZAI YI KWATANCI DA KAMAR RUNDUNA, AMMA TA KAI KIMANIN DARI UKU DA HAMSIN (350)."

A Zamanin Sarakunan Habe garin Hadejia bashi da ganuwa sai dai wani abu da ake kira "KAFI", wato wani Asiri ne na kafewa gari wadda abokan gaba bazasu samu nasarar yakar garin ba. Shi kafi ana sanya Layu ne a cikin Tukunya ko a kahon rago da sauran su, sannan a binne a farkon gari da karshen gari ta kowane bangare. A lokacin da Sarkin Hadejia Sambo ya samu nasarar korar Sarkin Hadejia na Habe, bayan ya zauna a gidan sarautar su sai ya sake tsara taswirar fadar sa, inda ya sake gine-gine da soraye da masaukin baki da sauran su. Dalilin da yasa aka samu Kududdufin Atafi kenan, domin anan aka rinka debo ƙasar da aka gina sorayen fada.

Sarkin Hadejia Sambo shine ya gina ganuwa a Hadejia, inda kuma yayi kofofin shiga garin guda hudu. Wannan Ganuwar daga yamma iyakar ta Kofar Jarma, daga kudu kuma Bakin Ramin Atafi kusa da gidan Sarkin Busa. Daga gabas kuma iyakar ta ramin Tankari kusa da Unguwar Hudu, daga gabas kuma iyakar ta Unguwar Dallah. A zamaninsa kuma Fulani suka bar mazaunin su da yake Rinde, can kusa da Gandun Kabo suka dawo cikin garin Hadejia, inda da yawan su sai suka zauna a yamma da gari inda yanzu Unguwar Rinde take. Bayan Sarkin Hadejia Sambo shima Sarkin Hadejia Buhari ya fadada ganuwa ta bangaren Kudu har sai da ta kai kusa da Kogin Hadejia, shima Sarki Haru ya ci gaba da fadada ganuwa har sai da ta kai inda take a yanzu, sannan ta ci gaba da zama kofofin ta guda hudu. 

Kofar Gwani itace Kofar gabas
Kofar Matsaro itace kofar yamma
Kofar Kogi itace kofar kudu
Kofar Barno itace kofar Arewa.

Ganuwa kuma ta zagaye garin domin babu ta inda zaka shiga cikin gari sai ka bi ta kofofin nan. A zamanin Sarkin Hadejia Muhammadu wadda ya gaji Sarkin Hadejia Haru ya sake ginin kofofin nan, inda aka sake musu gini mai kyau a shekarar 1871. Dalilin wannan gini ne ma yasa ake kiran kofar Gabas da suna Kofar Gwani, domin wani magini ne mai suna Gwani ya gina su har ma da Soron fada da ake kira Soron Bubban Gwani.

Itama Kofar Kogi ta sauya suna a zamanin da aka rufewa Sarkin Hadejia Umaru Kofa, saboda ambaton kalmar kyale su da yayi shine yasa ake kiran ta Kofar Kyale su. 

Kofar Barno itama ta sauya suna yanzu an fi kiran ta da sunan Kofar Arewa, dalilin da yasa ake kiran ta da Kofar Barno kuwa shine, saboda Unguwannin da suke kusa da kofar duk mazaunin Barebari ne, irin su Gagurmari, Kilabakori, Kakaburi, Zonagalari da sauran su. 

Itama kofar yamma dalilin da yasa ake kiran ta da suna Kofar Matsaro shine saboda Sarkin Kofar ne ake kiran sa Mai Tsaro, shine ake cewa kofar Mai tsaro daga baya sunan ya sauya ya zama Matsaro. 

Zamanin Yakin Hadejia da Turawa a shekara ta 1906, Turawan sun rusa ganuwa ta Kudu da gari inda suka samu suka shigo Hadejia suka cita da yaki. Bayan an gama yaki ba'a gine wurin da Turawan suka shigo ba, sai aka gyara wurin aka saka masa kyauren kofa, sannan ake kiran kofar da suna Kofar Talata. An yiwa wannan Kofa lakabi da sunan ranar da Turawa suka fasa Ganuwar suka shigo Hadejia, wato ranar Talata.

Bayan shekaru da yawa kuma wannan kofa sai ake kiran ta da suna Kofar Mandara, domin akwai wata mata da ake kira Mandara kullum a wannan kofar take wuni domin tana tura dabbobin ta kiwo tun safe har zuwa yamma. Saboda karuwar Kofar Mandara sai kofofin Hadejia suka zama guda biyar.

Tun zamanin Sarkin Hadejia Haru wadannan Kofofi guda hudu suke da Sarakunan su, wato masu kula da su kenan. Wadda kuma sune suke sarautar Unguwannin da kofofin suke, misali... Mai Unguwar Matsaro shine sarkin Kofar Yamma, haka sauran kofofin duk masu unguwannin wurin sune sarakunan Kofofin.

Sunday, May 30, 2021

SARKIN YAKIN SARKIN MUSULMI NA GABAS...

HADEJIA A YAU!

A lokacin da Sarkin Marma Muhammadu ya dawo daga Sokoto wajen taya Sarkin Musulmi Yakin Madarumfa, jama'ar gari da mahaya Dawaki sun fita taryen sa domin kafin yazo labari ya iske Hadejiawa cewa Sarkin Musulmi ya nada shi Sarautar Sarkin Yakin Sarkin Musulmi na Gabas. Kafin Sarkin Marma ya iso kofar Fada Sarkin Hadejia Haru Bubba ya fito filin fada don jiran isowar Sarkin Marma, ko da ganin Sarki ya fito sai aka sanarwa Sarkin Marma cewa Sarki yana filin kofar fada.

Shi kuwa Sarkin Marma Muhammadu da ya iso kusa da Masallacin Juma'a sai ya tsaya anan, mahaya dawaki suka rinka zuwa suna yi masa Gaisuwa (Jafi). Anan Sarkin Jauje ya shirya masa wata waka da yake cewa...

Wai ina wani ba kai ba zaki wan dawa, 
Uwa hana kukan talaucin duniya,
Mu je mai randa mu debo tulina,
Ina ke gaba ina ke gaba,
Da ku fadawa ku daina haye masa.

Bayan an gama gaisuwa (Jafi) sai Sarkin Marma ya nufi Kofar fada yayi gaisuwa a wurin Sarkin Hadejia Haru Bubba, sannan ya wuce gidan sa ya sauka. Bayan ya zama Sarki a shekarar 1885, sai ya maida wannan Jafin Al'adar hawan sallah, duk sallar Azumi da Layya zai tsaya a kusa da Masallacin Juma'a Hakimai su zo su yi Jafi. Haka Al'adar ta ci gaba har zuwa yau.
Allah ya karawa Masarautar Hadejia daraja da daukaka.

Ismaila A Sabo.