"" /> HADEJIA A YAU!: Feb 18, 2013

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Monday, February 18, 2013

KASAR HADEJIA DA KEWAYENTA.

Hadejia A yau Muna farawa da sunan Allah Mai kyauta
Magamiya a Duniya, ya baiwa musulmai da
kafirai baki daya! Mai jin kai Kebe Gobe
kiyama. Ni'imarsa ga wanda yayi Imani take
Ranar Alkiyoma. Tsira da Aminci su Tabbata
Ga shugabanmu Annabi Muhammadu (s.a.w.)
wanda Allah ya aikoshi da shiriya ga
Mummunai.

Kasar Hadejia kasa ce wadda Allah Ya
Albarkaceta da Ni'imomi daban daban kamar
Kasar Noman Rani da Damina, Kiywo, da
sauran Albarkatun cikin Ruwa da na Kan
Tudu. Kuma kasar ta kafu tun a Karni na 17
wasu kuma sunce Karni na 15. Daga Gabas
tayi Iyaka da Daular Kanem Borno daga
yamma tayi Iyaka da Masarautar Kano. Haka
kuma daga Kudu tayi Iyaka Da Wuddiri wato
kasar Katagum. Sannan daga Arewa tayi Iyaka
da Masarautar Gumel da Daular Damagaram.

Kuma Hadejia tana daya daga cikin Hausa
Bakwai dukda cewa Fulani ne Suke Mulkinta.
Hadejia A yau.
Abinda nakeso na fada shine... Cikin Hikimar
Ubangiji da Ikonsa ya bamu Manyan mutane
Masu Kaunar Ci gaban Wannan yanki.


Wadansu 'yan Kasuwa ne wasu kuma
Ma'aikatan Gwamnati, wasu kuma 'yan Siyasa.
Kullum kokarinsu da Tunaninsu shine yaya
zasu samawa Kasar Hadejia Mafita? Yaya zasu
kawowa yankinsu ci Gaba? Yaya zasu rage
zaman banza ga Matasa? Yaya zasu Hada kan
Al'ummar Kasar Hadejia su kalli Alkibla Guda?

Allah ya saka musu da Alkairi.
Saboda haka ne wasu daga Cikinsu suka fara
Gina Masana'antu da kamfanoni domin
samarwa da Matasa aikin yi. Zamu fara da
Kamfanin shinkafa wanda ana nan Ana aiki
ba dare ba Rana. Sannan kamfanin Suga
wanda shima ana kan Aikinsa.
Haka nan Masana'antu Gasunan wasu ana
aikinsu wasu kuma tuni suna aiki kamar
Sambajo Gen. Enterprises da sauransu.
Sannan Idan kazo titin Maje Road zakaga
wasu Gine gine masu Hawa biyu (2) suma
anayinsu don kyautata Rayuwar Al'ummarmu.

Muna Addu'ah Ga 'yan kasuwarmu da
Ma'aikatan Gwamnatinmu da 'yan siyasarmu
Allah ya saka musu da Alkairi. Allah ya karfafi
zuciyarsu. Amin.

(1) A.V.M. Hamza Abdullahi
(2) Alh. Salisu Sambajo
(3) Alh. Hashim Ubali Yusuf
(4) Alh. Lawal A.A.
(5) Alh. Muhd. Daguro Adamu
(6) Comrade Umar Danjani
(7) Danmasanin Hadejia Alh. Dr. Muhd. Lawwal
(8) Magayakin Hadejia Alh. Muhd. Umar
(9) Professor Haruna Wakili
(10) Alh. Sarki Kafinta Mallam Madori.
Hadejia A yau.