"" /> HADEJIA A YAU!: 2019

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, September 17, 2019

DAMA CE KAWAI.... Dr. Nuruddeen Muhammad

HADEJIA A YAU!

Labarin Rayuwata

Dama ce kawai...! Dr. Nuruddeen Muhammad. 

Ma'anar Dama itace "wani lokaci ko wasu jerin al’amura da kan yi dalilin faruwar wani abu."

Rayuwata gaba d'ayanta labari ne na damarmaki wanda ke sanya fata da karfafa zuciya. Wadannan damarmaki sun kasance da iznin Allah mad'aukaki tamkar wata fitila ce da ta haskaka mini tafarkin rayuwa na zama duk abunda na zama.

Dacewa da samun wad'annan damarmaki, da kuma amfani da su a lokutan da su ka bijiro, shine dalili da kuma matakin dagowata daga tsukun yankin mahaifata a Hadeja, Jihar Jigawa, arewa maso yammacin Najeriya, inda ya kaini zuwa madaukakan wurare kamar ofisoshi da d'akunan taron Majalisar ‘Dinkin Duniya da ke birnin New York na k'asar Amurka da kuma dukkan nahiyoyin da ke fadin wannan duniya.

Babbar dama ta farko a gareni ita ce ta samun mahaifi irin wanda Allah ya azurta ni da shi (Mallam Muhammad Adamu UNIK), jajirtaccen malamin makaranta kuma Hedimasta da ya shahara kan gaskiya da rikon amana da kuma aiki tukuru. Malam ne ya fara cusa min ak'idar sanin darajar ilmi da maida hankali a kan aiki, tare da nusar da ni kyawawan dabi’u na rayuwa irin su: gaskiya da rik'on amana, hak'uri da juriya, karfin hali, sanin darajar d'an adam, fin k'arfin zuciya, tausayi, da kuma uwa uba, ya dasa min ginshik'in tsoron Allah a zuciyata. 

Wannan Damar dai ita ce ta ingantaccen ilimin da na samu  k'yauta a makarantun gwamnati (tun daga makarantar firamare ta unguwa zuwa sakandaren yanki, jami'a da kuma k'ololuwar mataki na karatun aikin likita. Karatu, tarbiyya da kuma jajircewa su ne dai ta hanyar da Ubangiji ya d'aukaka Nura ya koma Dakta Nura a yau.

Dama ce bud'e ido da na yi da wuri akan harkokin siyasa na gane yadda ake gudanar da ita, a inda na fahimci tasiri ko k'arfi na tarayyar jama'a a karkashin wata manufa guda idan aka yi amfani da shi wajen yad'a ak'idar da za ta amafanar da daukacin al'umma, musamman bangaren talakawa.

Babbar Dama ita ce da Allah (SWT) ya had'ani da Dr Sule Lamido, wanda ya gano wad'ancan halaye nawa, da tarbiyya, da karatu, da kuma bibiyar siyasa, ya gamsu da su, sannan kuma ya ci alwashin sarrafa su. Shine dai sanadiyyar da ta kai ni can k'ololuwar  gwamnati ina matashi d'an shekara 34 kacal, inda a gefe daya na san maza kuma maza su ka san ni, amma kuma a wani gefen na gane cewa duniyar nan fa ba komai ba ce face wani yanayi na k'ank'anin lokaci.

Ba komai ba ne face Dama ta jawo min yabo da girmamawa daga shugabannin k'asashe, manyan jami'an difilomasiyya da siyasa, fitattun shugabannin al'umma,  hamshak'an ‘yan kasuwa da kuma y'an uwana likitocin da na samu dacewar yin gogayya da su, kuma Allah ya ba ni damar nuna musu kokari da jajircewata ta ganin na kai gaci a duk wani al’amari da na sa a gaba ko kuma duk wani aiki da aka sanya ni.

Babbar tambaya a nan ita ce, ta ya ya wani matashi marar gata a sama, wanda ya fito daga arewacin Nijeriya, yankin da miliyoyin ‘ya’yan talakawa irinsa su ke rasa makomar rayuwa tun suna ‘yan kasa da shekaru 10, ya zama Ministan Najeriya ma fi k'arancin shekaru tun bayan dawowar mulkin damokirad'iyya a kasar a 1999, k'wararre a aikin likitanci, gogagge a harkar diflomasiyya, kuma har ya taka rawa a harkokin siyasar al'ummarsa, a k'asar da samun irin wannan tagomashi sai ‘yan tsiraru, masu uwa a gindin murhu??!
..... Amsar dai mai SAUK'I ce!!...

Alhamdulillah... DAMA CE KAWAI!!!

Sanin da na yi cewa, ba dan wad'annan damarmaki da na samu a rayuwata ba, da kuwa ni ma zan iya shiga kowane irin hali, shine babban k'aimin da ya sanya na yi tunanin kafa wannan Gidauniya ta Unik Impact (www.unikimpact.foundation). Ita dai wannan Gidauniya tamkar wani dandamali ne na yi wa al'umma, musamman 'yan uwa matasa, kokarin samun dama a rayuwa ta hanyar bayar da tallafi ga harkokin ilminsu, tattalin arziki da kiwon lafiya, har ma da inganta muhallinsu. Sannan da yi musu jagoranci bisa sanin muhimmancin ilimi da kuma rungumar dabi’un kirki irin su: jajircewa a kan aiki, gaskiya da rik'on amana, fin k'arfin zuciya da kuma nuna tausayi ta hanyar yi wa al’umma hidima da taimakon na kasa.

Babban burin wanna Gidauniya shine tarairayar zukatan matasanmu da d'ora su a kan tafarkin samun d'aukaka da cin nasara a rayuwarsu. Idan har ni zan sami irin wannan d'aukaka, to a cikin ikon Allah kowa ma zai iya samun irin ta, ko sama da hakan  ma idan ya sami dama.

Hakika tarbiyya ce, da kuma karatun da duniya ta koya min, su ka ganar da ni cewa, d'aya daga cikin hanyoyin da mutum zai nuna godiya a bisa ni'imomin da Allah ya yi ma sa, shine, shi ma ya yi sanadiyyar samun dama ga wasu. Ta haka ne kawai zamu yi tunanin gyara al'ummar nan; ko da kuwa a sannu sannu ne.

Wani k'wararre da na yi aiki tare da shi, ya ta6a yi min tambaya cewa ya ya na ke hangen wannan Gidauniya ta Unik Impact a cikin zuciyata?... sai na amsa masa da cewa:

"Kamar gungu ne na wasu mutane da  Allah ya bai wa Dama a rayuwa  inda su ma su ke k'ok'arin ganin wasu da yawa sun sami irin wannan damar."

Hausawa dai su kan ce: ‘Yi wa wani, yi wa kai....’

Wednesday, September 11, 2019

KANO IN 1851.. PROGRESS OF THE AFRICAN MISSION.

HADEJIA A YAU!

Royal Geographical Society of London on
the 11th of January, the 24th of March, and the
10th of November, 1851.

Second Letter from Dr. Barth to Dr. Beke.

Kano February 23,1851. Without stopping to give any personal news, which you will doubtless hear from another quarter, I proceed at once to acquaint you with the result of my researches at this place, which would indeed have been much more extensive, if my material circumstances, in conjunction with a little sickness, had not taken up a good deal of my time. 

The present Sultan of the Fulani empire, or the Emir el Muminun Ali ben Bello, is represented as a man whose whole endeavour is only to a mass riches an example which is strictly followed by his officers. But as he never visits his provinces, and as the communication with them is very precarious, the governors are very independent, the office of some of them having even become hereditary. The Sultan himself is said to be able to collect a force of ten thousand horse. The name of the present Gedado is Abdu. Among the governors, who equally adopt the title of Sultan. 

1. The Governor of Kano has the greatest power, on account of the market, which enables him to send ten thousand cowries daily to Sokoto for the household of the Sultan. The name of the present Sultan of Kano is Othman ben Ibrahim Dabo, but his brother, the Galadima, has in fact greater influence and power, so that in reality there are at present two Governors, each of whom requires a considerable present. The Governor, who is said to have formerly had a force of 10,000 horse, is now not able to collect more than 7000. 

2. The second, as regards real power, after the Governor of Kano, is, as I am informed, Ibrahim ben Yakuba, the Governor of Bauchi, or Bautshi, who has his residence at Yakoba; for although he has a force of only 2000 horse, his troops of archers, the best known in Sudan, are numberless. 

3. The third rank belongs to the Governor of Zegzeg, Mohammed Sani, who resides at Zaria. He has about 3000 horse, and numbers of archers. Zegzeg is a province of great extent. 

4. Loul, the Governor of the extensive province of Adamawa comes next, who has his residence at Yola. Besides a large army of archers, he has a force of 2000 horse. 

5. The next in power is Ahmmedu, the Governor of Hadejha, who has a force of ahout 2000 horse. 

6. Next to him is Mohammed Bello ben Mallem Oumaro, the Governor of Katshina, with a force of not much more than 1000 horse. Katshina, on account of its vicinity to the hostile countries of Maradih and Gober, has greatly declined.

 7. Rather more powerful is Abder Rahman, the Sultan of Katagum, who is said to bring 1500 horses into the field. 

8. Next to him in power may be considered Yerima Ahmedu, the Governor of Messau, who is said to have 1000 horse at his command. 

9. Then follows Harder Lareima, the blind old Governor of Marma, who resides at Naenawa; his former residence, Birnin-Gorno, having been destroyed by the Bornuese. He is said to have about 700 horses. 

10. The tenth rank seems to be occupied by Ismaela, the Governor of Shera, brother of Abder Rahman 'of Katagum, with not more than 500 horse. 

11. Then follows Koiranga, the Governor of Boberu, having his residence at the place of the same name, with about 100 horse. 

The 12th, and last of all, is the free booting Governor of the ruined province of Daura, a man bearing the same name as the Governor of Katshina, Mohammed Bello, who, though he has but 400 horse, is feared by all his neighbours.

 Besides these twelve Governors, who receive their orders directly from Sokoto, there is the Governor of Zamfara, named Ahmedu, who, as the cousin of the Sultan, enjoys almost the same rights as the above-mentioned persons. He resides at Bakura, and is in command of a force of 300 to 4000 horse. 

In addition to the foregoing, there are still two important provinces belonging to the Fullanis, Nuffe and Alyori, as Yauri is commonly called; but they do not, like the others, pay tribute to the Sultan of Sokoto, but to Khalil, the Sultan of Gondu, and grandson of the conqueror Othman dan Fodi by his son Abdallahi. 

The present Governor of Alyori is named Thita. He resides at Afasa, and is able to bring into the field 5000 horse. The name of the present Sultan of Nuffe is Masaba, who resides at Ladi, the present capital; Raba having been destroyed by the Fullanis about five years ago, when it rebelled against them. The Governor of Nuffe has about 2000 horse.

The court at Sokoto consists of nine persons. The next person after the Sultan, or Governor serki, is the Galadima, his first minister, and the natural Vice- Governor, a person sometimes of greater authority than the Governor himself. Next follow the Serkin dawokki, who has the command of all the horse in Kano; the Barden-Kano, the chief or general who leads the army ; the Al-Kalli or principal judge; the Chiroman Kano, who exercises the power in the southern part of the province; the Serkin-baye, who has the northern part of the province under his authority; the Gado or minister of the treasurer; and finally, the Serkin-Shano, literally the master of the oxen; the oxen as the principal carriers of luggage in Sudan being an important part of a court or army in this country. When the Sultan leaves the place for any length of time, accompanied by his first minister and his captains, the Gado and the serkin-Shano have the authority. 

I now proceed to give a short account. of the quarters and the gates of' the town of Kano, which Clapperton, though he made such a long stay here, has not, as far as I am aware, made known. In enumerating the different quarters of the town, I shall begin from the mountain named Dala the most characteristic feature of the town. At the southern foot of which the houses commence, stretching down towards the S. with very irregular outskirts. From this point I shall proceed eastwards, returning afterwards to the W., and so on. In this order the names of the quarters are as follows:
Dalla, Kutumbawa, Gerke, Madabo, Yantandu, Adakawa, Koki Seta, Limanchi. Then turning S. to W., Yandoyea, Jibjin, Yellabu, another Limanchi with a large mosque, Masukiani, Tuddum-Makera, Yamrotshe, Mararaba bokoi, Bakin-rua, Runfawa, Yellua. Next, turning again towards the E., Rimingirajire, Maggoga, Maggogi, Unguankare Dendalin-Ware, another Limanchi, Dukkarana, Riiffogi, Derma. 

All these quarters are principally, if not exclusively, inhabited by the Habe, and they all lie to the N. of the Jakara, the ill-famed waterpool which separates the southern half of the town from the northern; while the following quarters are almost exclusively inhabited by Fullanis- Yaaleria, Mariri, Agadesawa, Yola (the madakin Kano), El Kantara, Uaitaka, Sheriffe-Dodo, Tokobei, Dukkawa, Saghidarnse, Shafushi; then, returning from E. to W., Sherbale, Madabo, Kurna, Sheshe, Dirimin Kai-kai Rejiyan-lemu, Kualli, Al Fendeki, Sorandinki, Rimi-n- Kira, Toji (where the palace of the Governor is), Yakasai, Mandauari, another Marmara with the surname of Danturku, Sabansara, Kudedefawa, Jingo, Disoe, Warure, Gwale, Kurmawa, Hawsawa, Ungua Makama, Galadancshi, Shahuchi (where the elder son of the Governor, or the Chiroma, lives), Yerserki. Kurmawa, Kusserua, Udelawa (lying S. of the palace), Rimin kira, Karaka, Dugarawa, Yeakase, Nasserawa, Abdelawa.

 The importance of these ditferent quarters of Kano is the greater as in some cases they are entirely separated from one another by the spacious places or the numerous quarries which interrupt the groups of houses. Of the whole character of the town, which is indeed quite picturesque and interesting on account of the number of palm and other trees waving over its surface, I will not say a word, but will merely mention the gates in the extensive town-wall, which, like that of Katshina and Zaria, leaves a very wide open space, in some directions two miles in extent, round the town. The names of the gates, going from N. to W. and round from S. to E., are as follows : —Kofa Mazugerl, Kofan-rua, leading to Zinder, Kofan adama, Kofan gudan leading to Katshina, Kofan Kansakkeli on the direct road to Sokoto, Kofan Kaboga, Kofan-dukawia on the road to Zaria, Kofan gadan Kaiya, Kofan Kura leading to Katah, Kofa dan agundi, Kofan nassarawa, Kofa Wanbai on the direct road to Borno, and Kofa mata. These gates are shut every night and opened every morning; while the gate called Tawaieu Kofa (the gate of the enemies) is walled up, because, as they say, a prince, who left the town by that gate, died, but, as the name seems to indicate, because the enemy the Fullanis—made their entrance by it.

Tuesday, August 20, 2019

MUHIMMANCIN AIKIN SA KAI A TSAKANIN AL’UMMA DOMIN INGANTA MUHALLI...

HADEJIA A YAU!

Daga Dr. Nuraddeen Muhammad

Gangamin Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Da Inganta Muhalli a Garin Hadeja
Lahadi 18 ga Agusta, 2019. 

A'uzubillahi Minash shaid'anir rajim. Bismillahir rahmanir raheem.
Maimartaba Sarkin Hadeja, kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Jigawa; Alhaji (Dr) Adamu Abubakar Maje Haruna (CON), Maigirma Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa; Alhaji Umar Namadi, ‘Dan Majalisar Dattawa mai wakiltar yankin Arewa maso gabas na Jihar Jigawa; Sanata Ibrahim Hassan Hadeja (Shattiman Hadeja II), Bubban Sakatare a Ma'aikatar kula da Muhalli ta Jihar Jigawa; Dr Abdullahi Muhammad Kainuwa, Shugaban Hukumar Talabijin ta Jihar Jigawa; Alhaji Ishaq Hadeja, Shugaban K'ungiyar Gangamin Tsabtace Garin Hadeja da Shuka Bishiyoyi (HGPE); Mallam Ahmad Ilallah, Wakilan Kungiyar Inganta Muhalli da Shuka Bishiyoyi ta garin Gumel (GCIGCE)
Shugabannin Kungiyoyin sa kai na al'ummar Hadeja, Sauran manyan bak'i da aka gayyata' Yan Jarida na rediyo, da talabijin, da jaridu, da kuma kafafen sada zumunta na zamani, Y'anuwana maza da mataA ssalamu alaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu....

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Mad'aukakin Sarki, mai kowa mai komai, da ya bamu ikon taruwa a yau domin gudanar da wannan gagarumin aiki na alheri. Tsira da amincin Allah su tabbata ga manzon tsira Annabi Muhammad (SAW), fiyayyen halitta kuma mafificin masu tsabta da inganta muhalli.

Daga farko, zan fara da godiya maras adadi ga shugabannin wannan gamayya ta matasa domin tsabtacewa da kuma inganta garin Hadeja da suka bani wannan muhimmiyar dama har kashi biyu.

Ta farko ita ce kasancewa babban mai gabatar da jawabi a matsayina na d'an uwansu matashi - Dr Nura. Domin a ba mutum damar yin magana gaban irin wannan gangami, musamman idan a ka yi la'akari da irin mutanen da aka tara a wannan wuri, to ba k'aramar dama ba ce da kuma girmamawa.

Maudu'in da a ka ce na yi magana a kansa shine 'Muhimmancin Aikin Sa kai a Tsakanin Al'umma Domin Inganta Muhalli'.
Dama ta biyu kuwa ita ce, ta alfarmar da aka yi wa Gidauniyar da na k'irk'ra, wato Gidauniyar Unik Impact (ko Unik Impact Foundation a turance) ta yin tarayya a wannan aikin alheri da suka assasa ta hanyar ba da gudunmuwar d'aruruwan irin mad'aci da kuma mangwaro na zamani. Babban abin godiya ne a ba ka damar shiga cikin wani aikin alheri na al'umma.

Shuka bishiya abu ne mai matuk'ar muhimmanci a garemu ba wai kawai ta fuskar kariya da inganta muhalli ba, a'a, har ma ta fuskar addininmu, tattalin arzik'inmu, da kuma walwalarmu.

Tun farko, shi dai addinin musulunci, a matsayinsa na tsarin wayewa na gabadayan rayuwa, ya yi tanadin tsare-tsare da ka iya magance matsaloli na muhalli da ke yi wa d'an adam barazana a wannan lokaci. A bisa tarbiyya irin ta addinin musulunci, wasu magabatan na kallon cewa hatta shi kansa muhallin wani nau'ine na amana da Allah (SWT) ya mallaka a hannun bayinSa. Akwai ayoyi da dama na Alkura'ani mai tsarki da su ke tsawatarwa ga mumunai akan almubazzaranci, yad'a 6arna da kuma fasadi a bayan k'asa. Lalatawa da kuma wofintar da muhalli, tamkar wani nau'ine na almabozaranci da kuma 6arna a bayan k'asa.

Saboda matukar muhimmancin da addinin musulunci ya dora kan amfanin itatuwa a muhallin dan Adam shi ya sa ma ya yi hani da sare bishiyoyi da sauran nau'in shuke- shuke ba tare da wani kwakkwaran daliliba.

Manzon Allah Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, ya kwadaitar a cikin ingattattun hadisansa akan falala da kuma fa'idar inganta muhalli, da daraja shi, da kare shi ta hanyar shuka bishiyoyi. D'aya daga cikin hadisan shine wanda mazon ya ke cewa; "ita duniyar nan koriya ce shar k'yak'yk'yawa, kuma Allah (SWT) ya dank'a muku ita a matsayin amana".

Ko da a yanayi irin na yak'i, Manzon tsira ya kan gargadi kwamandojin rundunonin musulmi da su guji sare bishiyoyi da kuma amfanin gona na abokan gaba. Ma'aikin dai ya kasance a lokacin rayuwarsa yana bada muhimmanci da karfafa guiwa kan amafani da k'asa mai d'orewa. 

Tuesday, August 6, 2019

THE SEDIMENTS OF COLONIAL MASTERS SYMBOLS IN HADEJIA. By Ahmed Aliyu Ilallah

HADEJIA A YAU!


 


A rejoinder to Babangida Usman Hadejia
………………………
Com. Ahmed Ilallah 

It will be difficult to describe the moods of concerned people on this issue. we should note that, the disturbed feelings is beyond the people of Hadejia but a global issue. But what always muddled my mind and some people alike, this kind of issues is just like a children nights tells by elders, it will just pass-bye, no action will be taken to address it. 

Mal. Babangid Usman has given the prerequisite information on this historic matter. My quest on the issue and other related issues concerning the historic symbol of Hadejia, that may come later in trigger by me or other people, showed that the site of these buildings is not in possession of any public organization (LG, SG, EC..). The sites including the structures are sold by either the State Government or Local Government to private individuals for residential purposes. 

This action is direct insult to the legacy and history of Hadejia and purely demonstration of either obliviousness of the antiquity or unpatriotic custom to the legacy of colonial history in Hadejia.

Many states in the country haven’t destroyed their history, in abridged quest for Arewa House in Kaduna.

With due respect, I wish to refresh the memory of all the stakeholders on this issue. I am also drawing the attention of: the Jigawa State Government, HE Abdulkadir Namadi, Senator Ibrahim Hadejia, Hon. Ibrahim Kamfani  Auyo, Hon. Mallam AbubakarJallo, Hon. Maikanti to please retract these site back to the public authority and intimate the relevant authorities to develop it for  future economic and social development of the region.

I am appealing to the current possessors of the lands to please, stop developing and destroying the site for general public interest.

To the people of Hadejia to please, get ready for all of us to buy-back the lands and take it back to the relevant public authority, by donating at least N5 for an approximate over 1.8m Hadejiawa  to save the image of our region, if the above failed to consider
 (a suggestion).

alhajilallah@gmail.com

Thursday, August 1, 2019

THE NINGI MOUNTAINS OF NORTHERN NIGERIA 1846-1902

HADEJIA A YAU!

                   An Islamic Frontier Polity:

Frontier areas often provide refuge for those in rebellion against the metropolitan society. But once on the frontier, they face certain organizational problems. If there is a local population, they may meld into it, or keep apart from it, or try to use it for their own purposes. And the immigrants are often forced, sooner or later, lnw some kind of relationship with the metropolitan centers. This paper examines the case of a group of Hausa mallams (learned men) who fled their own society and established a polity on the fringe of the Sokoto Empire, in the Ningi mountains of the Jos Plateau of northern Nigeria. They came to live in an area occupied from time immemorial by vigorous but small-scale "pagan" societies, with rudimentary forms of organized political authority. At the same time, the immigrant mallams had not withdrawn entirely from the reach of the organized states-emirates led by the Sokoto Caliphate. Thus, paradoxically, this Muslim reformist polity came to depend on an alliance with its new non-Muslim neighbors in order to survive pressure from the Muslim states with which it had immensely greater cultural affinities. The contradictions that this entailed are at the heart of our story.

THE MALLAM REVOLT IN KANO
Kano Emirate was perhaps the most important of all the emirates in the Fulani-dominated Sokoto Empire that emerged after the successful Fulani jihad of 1804-1808. By the mid-nineteenth century, Kano had become not only an outstanding metropolitan center of Islamic learning but also the financial entrepot for the Caliphate. But like many empires, Sokoto began to suffer from the Costs of expansion and its citizenry responded in various
ways to the increasing burdens of rents and taxes. Most, to be sure remained loyal; others joined dissident brotherhoods; and some fled to the fringes of the empire (Last 1970;345-357). 

At the end of 1846, some sixteen Hausa learned men (mallams) and their families, led by Mallam Hamza, left the Islamic center of Tsakuwa in Kano Emirate, pursued by Kano forces for their refusal to pay the land tax (kurdin kasa) a tax from which they had been exempted before the Fulani Hamza never developed into a cohesive brotherhood (tariq). Instead, its retreat into a non-Muslim area on the frontier of Islam made it the founder of a predatory polity.

THE NINGI FRONTIER ZONE
The area into which Hamza's mallam community moved was peripheral to the Islamicized metropolitan centers of northern Nigeria sociologically, culturally, ethnically, politically, and geographically. In this sense, it may be regarded as a frontier zone. The Ningi area is the northern most extention of the Jos Plateau massif. It is mountainous, incised with valleys suitable for plain and terraced agriculture. Most of it is some 2,000 feet above sea level, the central area rising to 3,000 feet and peaks reaching 6,000. The Ningi area of our story nearly coincides with present Ningi Division, which is just under 2,000 square miles. The area expences a completely rainless season and it genetally shares in the hardships of the "famine zone" of the Western Sudan (Renner 1926:583- 596).

Even in the remote past, Ningi appears to have been an isolated fringe area from the perspective of the flatlands on which arose the old Hausa city-scates. It shows a great deal of cultural and linguistic diversity and it had never developed, within historic times at least important integrative networks among its communities. It is impossible CO know what the 
population of Ningi was when the mallams arrived. The first assessment in colonial times, done in 1908 (Groom 1910), gave a total population of some 21,500, some 17,000 of these being of "original" stock. Among these, the largest groups were the Warji (ca. 7,000), the Pa'a (ca. 5,000), and the Buta (over 3,000); the other groups were each in the range of a thousand or less. These figures suggest that the non-Muslim population that the mallams found and thac came to represent their "reservoir" of economic and military strength was in the range of a score of thousands. 

Sunday, June 2, 2019

SABBIN MASARAUTUN KANO.... Daga Fatuhu Mustapha..

HADEJIA A YAU!

Sabbin Masarautun: Rano Gaya, Karaye da Tatsuniyar Bayajidda... 



Daga Fatuhu Mustapha.

Dama dai mun san meye asalin garin Bichi, domin bawani jimawa yayi ba. Amma meye asalin kafuwar wadannan garuruwa da na lissafa a sama? 

Akwai hanyoyi kusan hudu da zamu fahimci kafuwar wadannan garuruwa, sun hada da...... Tarikh Arbab Wato Kano Chronicle, Hausa Girgam, Wakar Bagauda da kuma kundin WaraÆ™a Maktuba fiha-asl al Wangariyun. Wadannan sune manyen kundayen da ake dogaro dasu akan tarihin kasar Kano.  

Amma kafin nan, bari mu koma baya mu fahimci me ake nufi da kasa, mai kuma ake nufi da gari. Kasa dai kamar yadda zamu ce kasar Kano, kasar Katsina, Kasar Zazzau, Kasar Zamfara, na nufin wata nahiya dake zaman kanta, Wadda a turance ma iya cewa tana da Sovereign power ko kuma authority, da take gudanar da alamuranta ba tare da wani katsalandan na wata kasa ba. Acikin littafin Raudatul Afkar, na Malam Gidado Bin Mustapha (Malam Dantafa), ya bayyana wannan yanki namu da sunan Sudan ta Tsakiya, wanda ya banbanta su da Sudan Madaukakiya da kuma Sudan Makaskanciya. Kasashen Sudan a cewar malamin sun hada da: Borno, A'ir, daulolin dake sahara, Kano, Katsina, Gobir da Zazzau. Wadannan a cewarsa sune kasashen dake Sudan ta Tsakiya. Ba shi kadai ne ya ambata haka ba, shehin Malamin nan na Timbuktu wato Ahmad Babq al Timbukti a wata amsa da ya aikewa wani almajirinsa dake zaune a kasar Masar wato Ibrahim al Isi, wacce ya kira da Al Kashf wal Bayn fi hukm mujallab al Suud, ya bayyana cewa " amma kasashen Hausa sune: Kano, Katsina, Zazzau, Gobir da kuma Borno " in banda Borno da ya sanya aciki, dukkan wadannan kasashe, an tabbatar da Dauloli ne masu zaman kansu a kasar Hausa. Duk wata Daula da kaji to daga baya ne. 


  1. Kafuwar Daulolin Tsakiyar Sudan 


Mafi dadewa a iya saninmu sune Daular Tumbi da Washa, wanda a yanzu Tumbi wani kauye ne a kasar Gumel, yayin da Washa ke kasar Damagaram. Wadannan dauloli sunyi karfi kwarai a wasu lokuta masu tsaho, sai dai bawani cikakken nazari a kansu, dalilin kafuwarsu, karfinsu da kuma dalilin rushewarsu. Amma dai mun san tun shekara sama da dubu, dakarunsu kan kai hari zuwa Kano da Katsina da Zaria. 

Kasar Kano da Asalin Mulkinta 

Shaidu na tarihi sun tabbatar da cewar kasar Kano ta samo asali ne, tun kusan fiye da shekaru 3000 da suka gabata, bayan da wasu kabilu da ake kira maguzawa (Majusawa: kamar yadda Murray Last ya bayyana asalin sunan), Wanda ake zaton sun taso ne daga tsibirin Dahlak na kasar Ethiopia wato Habasha. Wannan kabila sun zo nan kasar Kano karkashin jagorancin wani babban limamin addininsu maisuna Dala, da kuma wasu yanuwansa guda uku: Kanau, Ranau da kuma Gayya.

Wadannan mutane ba yan siyasa bane tun farko, hankalinsu yafi tafiya wurin yada addininsu na Maguzanci, daga sune aka samu firqoqi ko dariqu irinsu Gwandarawa dake jihar Nasarawa a yau, Arna da a yanzu kusan duk sun koma Kirista, da Domawa dake kasar Kazaure da Kismawa dake Dambatta da sauransu. 

Sun kafa wurin bautarsu a kan dutsen Dala dake cikin garin Kano Wanda suka kira Kakuwa, inda Suke bautar wani aljani da suke kira da Tsumburbura, Danko, ko Shamus, Wanda Malam Adamu Na Maaji yace shine Yaquqa da ake bautawa tun zamanin Annabi Nuhu acikin littafinsa: Iilan bi Tarikh Kano. Wasu kuma yanki suka kafa nasu bautar a Bakin Ruwa, inda suke bautar Ruwan Jakara (sai dai wadannan ana ganin ba Maguzawa bane, asalinsu Abagayawa ne). Akwai kuma wasu masu bautar bishiya wata Tsamiya da ake kiransu da Gazargawa, wadanda ke zaune a Madatai. Da Gwandarawa dake bautar farji a dutsen Bompai da sauransu. 

A wannan lokacin garin Kano ba komai acikinsa in banda wuraren bauta, a saboda haka baa noma kasar, ko ayi farauta, ko yaki ko a haki maadananta. Wannan babban laifi ne ga addinansu. A wannan hali bukatar siyasa da ta tattalin arziki ta taso, Wanda ya sanya, bayan rasuwar Dala, wasu daga cikin kannensa suka ga bukatar lallai su nemawa kansu da mutanensu mafita. A saboda haka suka fara tarwatsewa daga Kano. Ranau da yake zaune a Kusurwa (nan inda gidan Galadiman Kano yake a yanzu wato gidan Wambai) ya tashi ya koma wani wuri da ake kira Zamna Gaba (wato Rano a yau) ya kafa gari. Gayya ma ya tashi ya koma ya kafa garin Gaya. A ka bar Kanau a matsayin babban limamin addininsu a Kano. Amma duk da wannan suna tare da cibiyarsu ta addini dake Dala. Babu wata shaida da ta nuna, wadannan garuruwa sun kafa wata kasa tasu mai zaman kanta. 

Bagaudawa da Sabon Canji 

Asalin Bagaudawa dai Hausawa ne dake zaune a yankunan kasar Bauchi. Akwai masu raayin kalmar Bauchi na nufin Bahaushe. A wani kaulin kuma ana zaton tana nufin 'Bawa'. A wani rangadi da Firauna Hausal ya fito, a jirgin ruwa, an bayyana cewa ya fado ta tafkin Chadi, ya biyo ta kogin Jakara, ta Hadeja Jamaare, ya shiga kasar Bauchi (Baushe)inda ya iske mutane, daga nan ya bi ta kogin Binuwai ya je har Bargu (Barku), ya bi ta kogin Kwara ya fada zuwa Tekun Atlanta ya koma gida.....

(Zamu cigaba inda zamu ji alakar Bagauda da Daura, da karairayin tatsuniyar Bayajidda) insha Allah..... 

Tuesday, March 5, 2019

JIGAWA THE SECOND HIGHEST POVERTY STATE IN NIGERIA MY ARGUMENT AND THE CHALLENGES IN THE NEXT LEVEL... By Comrade Ahmed Ilallah

HADEJIA A YAU!



My mind vibrates, when I read the report that put Jigawa as the second poverty state in Nigeria, just after Zamfara, many can easily admit the position of Zamfara, due to the current insurgency, which is taking years now.

But my concern, dismay and arguments is the position of Jigawa. Jigawa cannot be in the highest poverty level in this country, I am questioning the methodology used for obtaining the result. What are the variables and modules used in the statistics that produced the said result? If employment generations, women & youth empowerment and increased in per capita incomes are instruments against poverty, Jigawa is among the realistic state in these capacity.

Jigawa a rural state, means the majority of the population are rural residents.  The present administration policy of empowering rural women with the programme titled “Goat Multiplication Programme” has not only enriched our local women, but has also increased the populations of small ruminants in the state. The programme is just an addition to the cluster farming programme and many empowerment programmes that are professorial of Jigawa State. In fact, the government policy has attracted private investors, like Dangote Rice, Gwiwa Independent Power Project and many others, that are all on stream.

Jigawa state as agricultural state, the state, the government of federation and the private investors in the last four years have hugely invested in agriculture, specifically in rice, sesame and wheat production, which yields a significant result especially in the Northeast of Jigawa and Southwest. Jigawa State is at the top in rice production in the country. I am assured of great economy and investments development and transformation in the state in the last years, through Jigawa Invest, we have factories that are now fully working. All these are visible.

The report can be a starting challenge to the incoming administration in the state, both the executive and legislative, if the report is against our expectation and has the facts that we are at that level. The challenges would be for the leaders to have a fresh strategy of alleviating poverty in the state with good understanding of the generality of Jigawa.

Though, I am googling to have the full report, I personally question the accuracy of this investigation. 

I boldly call the state government and all the CSOs that, we are working independently for good governance to perusal the report, and enlighten the public to disregard it.

This report is faulty, Jigawa is beyond many of the overrated states.

Friday, January 4, 2019

AVM. HAMZA ABDULLAHI..

HADEJIA A YAU!

Air Vice Marshal (retired) Hamza Abdullahi (2 March 1945-3 January 2019.
Hamza Abdullahi was born in Hadejia in Jigawa State, on 2 March 1945. He attended the Nigeria Air Force Tactical Training Wing, Kaduna in 1964. He completed the Aircraft Technical Officer’s Course in West Germany (1964–1966), and studied at the Royal Military Training Centre in Chichester, England in 1974. In July 1975, Lt. Colonel Abdullahi was air provost marshal and assisted in the coup that removed General Yakubu Gowon from power, replacing him with General Murtala Mohammed.

Hamza Abdullahi was appointed the Governor of Kano State in January 1984, he announced in January 1985 that his government was revitalizing the Expanded Program on Immunization, targeting children and pregnant women at risk from preventable diseases. As Minister of Federal Capital Territory from 1986 to 1989, Abdullahi oversaw the construction of Phase 1 of Abuja. His goal was to have 75% of the ministries in Abuja by 1990, the target date for the official transfer of the capital from Lagos. He described the new city as "a symbol of our unity". Abdullahi was promoted air vice-marshal in October 1988 and retired from the Nigerian Air Force two months later. He dead 3/1/2019. May his gentle soul rest in Jannatul firdaus.