![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEgAhm78uSydeW2X0xb2l15WTQrOZYH2xPyWHImqmJCwSedVZmFHGHXTYXp16hzgZ6mqPNG7o4mEddGrAjmhuoYUyBlJV9wLcrIcaGf1o2TPXxpE25lY3DWt-4PFht5GHDt5EJOm-vPQQ85Q/s320/Adamu.jpg)
A ranar Asabat 22/december/2012, Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje (c.o.n.) zaiyi bikin cika shekar Goma yana Mulkin kasar Hadejia, A karkashin Daular Usmaniyya.
A ci gaba da kawo Muku Tarihin wadanda suka baiwa Kasar Hadejia Gudunmawa wajen ci Gabanta, yau zamu kawo muku Takaitaccen Tarihin Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje. Hadejia A yau!
An haifi Mai Martaba Sarkin Hadejia a shekarar 15/october/1960, a cikin garin Hadejia. Ya fara Makarantar primary a Abdulkadir pri.school Hadejia a shekarar 1967-1972, sannan Ya shiga Makarantar Secondary a Garin Ikot Ekpene Cross-river a shekarar 1973-1976, sannan ya koma Govt.sec.school Danbatta a shekarar 1976-1979.
Mai Martaba Sarki ya samu Nasarar shiga Makarantar Gaba da Secondary ta school of Rural and social science dake Rano ta jihar kano a shekarar 1981-1982, da kuma 1983-1985.
By Ismaila A sabo
Mai Martaba Sarki ya fara Aikin Gwamnati a tsohuwar Jihar Kano a ministry of social wellfare a shekarar 1982-1988, sannan ya koma Kano state pilgrim wellfare board a shekarar 1988-1991.
Bayan da aka kirkiro Jihar Jigawa Mai Martaba Sarkin Hadejia ya koma Jigawa state pilgrim board a shekarar 1991-1998. Sannan ya koma Ma'aikatar Kananan Hukumomi ta jiha a shekarar 1998-1999 Inda ya rike mukamin senior personnel officer.
A wannan shekarar ne Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya nadashi sarautar IYAN HADEJIA dan majalissar Sarki. Hadejia A yau!
A shekarar 2000-2002, ya rike Mukamin Sakataren Alhazai a Jigawa state pilgrim board.
A ranar Laraba 11/september/2002 Allah yayiwa sarkin Hadejia rasuwa Alh. Abubakar Maje Haruna, sakamakon zaben 'yan majalissar Sarki suka zabi Alh. Adamu Abubakar a Matsayin Sarkin Hadejia Na Goma sha shida (16).
Kuma an Nadashi ranar Asabat 14/september/2002. A karkashin jagorancin Galadiman Hadejia Alh. Habibu Adamu.
A ranar Asabat 23/march/2003, An baiwa Mai martaba Sarki Sanda, a karkashin Jagorancin Gwamnan Jihar Jigawa na wancan Lokacin Alh. Ibrahim Saminu Turaki. Hadejia A yau!
Muna Taya Mai martaba Sarki Murnar cika shekara Goma yana Mulkin Masarautar Hadejia.