"" /> HADEJIA A YAU!: 09/01/2025 - 10/01/2025

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, September 20, 2025

SARAUTAR BARDE A HADEJIA.

HADEJIA A YAU!


Sarautar Barde, sarautar ce ta Habe wacce Fulani suka gada bayan Jihadin Shehu Usmanu Danfodiyo, kuma sarauta ce ta Mayaka ko Jarumai. Ma'anar sarautar Barde ita ce, duk lokacin da sarki zai yi wata tafiya mai nisa, Barde zai kasance a gaba har sai ya tabbatar da masaukin Sarki akwai kyakkyawan tsaro a wurin kafin Sarki ya iso ya sauka. Kuma yana binciken inda abokan gaba suke lokacin yaki sannan yana binciken inda abokan yaki suka buya don kawo harin samame. 

UNGUWAR TUDUN BARDE HADEJIA 1808 Ca

Wannan unguwa mai suna a sama, (Unguwar Tudun Barde) ta samo sunan ta ne daga Barde  Risku shugabanr rundunar yakin Hadejia, shi ne  ya fara sarautar Barde a Haɗejiya.

Barde Risku mutumin Takoko ne ta karamar hukumar Mallam Madori shi ne wanda mahaifin sa ya hada shi da Sarki Sambo lokacin jihadi bisa dalilin gayyatar mahaifin da Sarki Sambo yayi, yana da yar'uwa wanda Sarki Sambo ya aura wato DIBI mahaifiyar Sarki Buhari.


Barde Risku shi ne wanda da Sultan ya mikawa Sarki Sambo tuta shi kuma ya mikawa Risku, wannan tasa a lokacin sa  Tuta da shemar da ake kafawa  lokacin yaki suke karkashin kulawar sa.

Unguwar Tudun Barde tana Kudu masu yamma da fadar Haɗejia daga cikin ta aka samuTudun Mabudi koda yake babu unguwa Tudun Mabudi a hukumance.

Barde Risku yana  da da guda  daya da ya tabbata a tarihi wato Barde Fannami.
Kamar yadda tarihi na kunne ya girmi kaka ya nuna, bayan Sarkin Hadejia Sambo ya shiga garin Hadejia duka qasa ta zama tasa sai ya tasamma gyare gyare tare da nada hakimai da zasu taya shi jagoranci kasar Hadejia. Sambo ya nada hakimai daga kowanne bangare na kabilun da suke kasar Hadejia, wannan tasa ya nada Risku daga bangaren Kanuri. Daga wannan lokacin zuwa yau ga jerin mutanen da suka yi Sarautar Barde....
   1. Barde Risku 
   2. Barde Fannami 
   3. Barde Dandaku 
   4. Barde Zangoli
   5. Barde Ibrahim Hassan

Babangida Mukhtar Hadejia. 

Friday, September 19, 2025

COALITION OF APC SUPPORT GROUPS CELEBRATES BOT CHAIRMAN, ALHAJI SALIHU MUHAMMAD (COMMANDER), ON BIRTHDAY.

HADEJIA A YAU!



Dutse, Jigawa State – The Coalition of APC Support Groups, Jigawa State, has extended warm birthday felicitations to its esteemed Chairman of the Board of Trustees, Alhaji Salihu Muhammad, popularly known as Commander, in celebration of his birthday anniversary.

In a statement signed by the Coalition’s Publicity Secretary, Comrade Muhammad Babangida Muhammad, the leadership and entire membership of the coalition expressed their heartfelt appreciation for the Chairman’s unwavering dedication to the growth and unity of the APC family in Jigawa State.

From Muhammad Babangida Muhammad 

The statement described Commander as “a visionary leader, a pillar of strength, and a true patriot who has consistently demonstrated maturity, loyalty, and commitment to party ideals.” According to the coalition, his strategic wisdom and selfless service have continued to inspire many both within and outside the party.

“As you mark another year of a purposeful life,” the message read, “we pray that Almighty Allah (SWT) continues to bless you with sound health, divine wisdom, and increased grace to continue serving humanity and our great party.”

The coalition concluded by congratulating the celebrant and reaffirming their confidence in his leadership.