"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, March 17, 2012

A ranar 14 ga watan september 2012; Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar zai cika shekara goma yana jagorancin kasar Hadejia! A karkashin mulkin Daular Usmaniyya. Zamu rinka kawo muku irin ci gaban da masarautar Hadejia ta samu a lokacin Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar.

Wednesday, February 29, 2012

Wakar Malam Amadu Dan matawalle Hadejia

1, Harama fasihi ka kara shiri, sarkin samari da 'yan mata.


2, Bismilla nayi nufin waka allah ta-ala kaban hikima, in shirya waka da hausa ta.


3, Nine nasan duk abinda nake nufi a wakar Hadejiawa.


4, sarki yana da mabudinsa nima ina da mabudi Malam idi kaine mabudina.


5, D.O yana da akawunsa nima ina da akawuna Abdu yaro kaine akawu na.


6, Ga mai fasaha kanin sidi, na abdu yaro na maitaushi.


7, Dan maraya na cikin daji, mugun dawa na cikin bene.


8, Su gajango an samu gun Ala, hannun ruwa zaya sha kashi.


9, A gidan biki damisa tilas aka sata sai da ta dau tandu.


10, Giwa tana yin bikin 'yarta, zaki ka bai alwalin ango namun dawa za'a sha hidima.


Sauran baiti goma a baya!