"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, October 6, 2015

TAKAITACCEN TARIHIN RAYUWAR CHIROMAN HADEJIA. ALH. AMINU HARUNA

Daga Muhammad Yawale....
.

text-align: center;">

Bismillahirrahmanir-rahim.
An haifi Alh Muhammadu Aminu Haruna a garin Guri a shekara ta 1943, A lokacin mahaifinsa Alhaji Haruna Abdulkadir yana Chiroman Hadejia Hakimin Gundumar Guri. Ya halarci makarantar kur'ani wato allo a garin Guri makarantar sule Gangaran a 1952-1956, ya halarci makarantar Elementary primary Dallah a cikin garin Hadejia a 1953-1956, ya halarci makarantar middle school ta fantai hadejia a 1957-1960, sannan ya halarci makarantar horarda malamai ta Bichi a shekara ta 1960-1962.
Marigayi ciroman Hadejia yayi karatu a potiskum (s.t.c sage 1) a 1970 yayi karatu a kaduna polytechnic (stage2-3) a 1971-1974 yayi karatun higher diploma a zaria Insitute of Administration (A.B.U) a 1979-1980. Ya halarci tarurruka na karawa juna sani a wurare daban daban na kasarnan.

AYYUKAN DA YAYI:
Yayi malamin makaranta a lokacin (N.A) ta Hadejia na tsawon shekaru 2, a karkashin tsohon Head master marigayi Alh Abdu maigari Tafidan Hadejia, yayi malamin makaranta a primary ta dubantu a 1965, yayi sakataren karamin minista na MADAKIN Hadejia Muhammadu Gauyama, a ma'aikatar tsaro ta kasa a lagos bangaren jiragen sama (Air-force) a shekarar 1965-1966,
Yayi malami a kotun babban alkali lokacin alkali Dahiru. A shekarar 1966-1968, yayi malamin Turakin Hadejia lokacin Turaki Adamu, yayi Akawu a ma'aikatar mulki ta (N.A), yayi sakataren karamar hukuma a wadannan wurare Bichi, ringim, gumel, wudil, babura, gezawa, kafin hausa, dawakin tofa yayi sakatare na musamman a karamar hukumar birni da kewaye (kano municipal council).

Ya rike mukamin DPM a kananan hukumomin garki, malam madori, Taura a inda yayi ritaya. Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya nadashi Tafidan Hadejia Dan majalisar sarki a shekara ta 1994, cikin yardar Allah kuma Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar ya nadashi Chiroman hadejia a ranar asabar 13 ga watam march 2004 a inda ya gaji yayansa chiroman Hadejia Alh. muhammad Abbas.

Marigayi chiroman Hadejia mutum ne mai jajircewa kan gaskiya da rikon amana akan harkar da aka dorashi kuma ya nemawa mutane da dama aiki a lokacin gwamnati kuma duk abinda ya gani ba daidai ba baya yin shiru sai yayi magana hakazalika bai yarda kayimasa zancen waniba. Marigayi chiroman Hadejia ya rasu ranar juma'a da daddare 03/10/2015 bayan ya sha fama da jinya muna rokon Allah ya jikansa ya kuma kyautata bayansa.

Thursday, May 14, 2015

YAN GUDUN HIJIRA...



YAN GUDUN HIJIRA!
Tun a lokacin da rikicin Boko Haram ya Addabi jihohin Borno da Yobe aka samu watsuwar 'yan gudun hijira a wasu sassa na Nigeria, ciki harda jihar Jigawa, kuma akasarin wadannan 'yan gudun hijira zakaga Mata ne da kankanan yara wadanda mafiya yawa suna a kasar Hadejia da kasar Gumel. A lokacin da suka fara zuwa wadannan yankuna saboda basu da abinda zasuyi dole wasu daga cikinsu suke bin masallatai da majlissai domin neman abinda zasuci abinci da yaransu. Abin tausayi zakaga yara da basu fi shekara 7 zuwa 10 ba suna bi kantuna da wurin zaman jama'a suna neman taimako, a kwanakin baya basuyi yawan da ya wuce kaga biyu ko uku ba a kullum amma yanzu abin sai karuwa yake wanda a kalla sai kaga goma zuwa sama a rana daya da mata da kananan yara abin tausayi. zaka gansu a kofar masallatai da kasuwa har da Bankuna wurin layin Atm. Dole mumini mai Imani ya tausayawa rayuwar wadannan bayin Allah domin ba a son ransu suka bar gidajensu da 'yan uwansu suka zo suke yin Bara ba! Saboda yawan kwararowarsu yasa jama'a sun fara kosawa ganin abin ya zama ba na kare ba, yanzu kullum a baka gansu a gidanka ba kaga biyar ko shida.

MASU HANNU DA SHUNI....

Hakika Masu hali sai sunyi amfani da damar da Allah ya basu wajen taimakon wadannnan bayin Allah da muhalli da Sutura da Abinci, da kuma kula da rayuwarsu musamman kananan yaran. yana da kyau masu hali su ware wani abu daga cikin Dukiyarsu don taimakon wadannan bayin Allah a matsayin Sadakatul-jariya.

GWAMNATI MAI JIRAN GADO...

Koda yake bani da masaniya game da yunkurin da Gwamnatin Jigawa tayi game da wadannan bayin Allah, kuma ban taba ganin wani wuri da aka ware don 'yan gudun hijira ba zanso in bada shawara ga Gwamnati mai jiran Gado, A karkashin mulkin ko jagorancin Jam'iyyar Apc, dasu fara duba wannan Matsalar ta 'yan Gudun Hijira kafin su fara Aiwatar da kowane Aiki domin ceto rayuwar wadannan Mata da kananan yara daga yin Bara, wanda hakan ya fara jefa wasu daga cikinsu zuwa ga halaka. An fara samun rade radin wadannan mata 'yan gudun hijira sun fara yin Arangama da wasu gurbatattun mutane suna yin lalata dasu suna basu kudi, har ma ance wasu da yawa sunyi cikin shege Allah ya kiyaye! Abin takaici sai kaga idan 'yan Hisbah suka kama mace tana lalata in suka bincika sai kaga 'yar gudun hijira ce. Kasan Dalilin da yasata cikin wannan hali?

SHAWARA GA GWAMNATI....

Ina bada shawara ga Gwamnati mai jiran gado da suyi la'akari da wannan matsalar domin su san ta yadda zasu bullowa wannan Al'amari, ya kamata Gwamnati ta samar musu mahalli na wucin gadi sannan ta sanya yaransu a Makaranta don ceto rayuwarsu. kuma Ina baiwa Gwamnati Shawara da ta sama musu sana'oi domin su dogara da kansu. misali Gwamnati zata iya amfani da makarantar koyon sana'a don koyawa Matan yanda ake yin SABULU, SAKA, DINKI,Da sauransu. Daga karshe ina Rokon Allah da kar ya nuna mana makamanciyar wannan Bala'i da zai sa mutum ya bar gidansa da iyalinsa ya tafi wani wuri yana yin abinda ko a Addini yana daga cikin Abu mai Kaskanci. Allah ka zaunar da kasarmu da Jiharmu lafiya.

Ismaila A Sabo Hadejia.
13/may/2015.

posted from Bloggeroid