"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Thursday, August 8, 2013

HAWAN SALLAR AZUMI NA 8/8/2013 ALHAMIS.

Hadejia A yau. Daga Muhd Yawale Hadejia >


kamar yadda Aka sani Hawan sallar Azumi yana da tarihi mai tsawo a cikin Garin Hadejia, wannan sallar ma A bisa al'adar masarautar hadejia ranar sallah maimartaba sarki zai fito daga gida da safe, akafa tareda sauran mutanan fada domin zuwa filin idi. Dukda cewa za'ayi sallar ne a Bubban Masallacin Juma'a na cikin gari. Sakamakon ruwan sama da akayi kuma yayi ta'adi, Mai martaba sarki ya dage Hawan sallah domin Jajantawa ga wadanda ruwa yayi musu ta'adi.


Ga bayanin yanda Hawan sallah yake kasancewa da kuma ta Gurarenda ake bi. Bayan an idar sallar idi liman ya kammala huduba,sai hakimai da sauran mahaya dawaki su hau, sannan maimartaba shima zai hau dokinsa tare da Dandalmu, zai bi ta kasuwar kuda zuwa Titin yahai zuwa makera, sannan zai bi ta makwallah zuwa kofar Liman.


Idan maimartaba sarki yazo daidai kofar liman yakan tsaya domin karfar Jafi daga Hakimai. Wanda hakan ta samo Asali ne Tun Lokacinda Sarkin Hadejia Muhammadu Mai shahada ya dawo daga Yakin Madarumfa, ya tsaya a wannan Gurbin Inda su Jarumansa suke zuwa suke masa Jinjina. Amma a lokacin yana Hakimi ne kafin ya zama sarki. Bayan ya zama sarkin Hadejia sai ya maidata Al'ada wato duk sallar Azumi da Layya zai tsaya Hakimai suzo suyi masa jafi.


Daga nan kuma sai maimartaba sarki ya karasa rumfar manyan baki domin gabatarda jawabin sallah, bayan nan kuma sai maimarta ya karasa gida ya sauka tareda sauran hakimai.


Wannan shine Bayanin Hawan sallar Azumin wannan shekara a takaice da fatan Allah yasa ayi hawa lafiya a sauko lafiya. Allah yaja zamanin maimartaba sarki.

Saturday, August 3, 2013

TAKAICACCEN TARIHIN SHEIKH ISAH WAZIRI (WAZIRIN KANO)

HADEJIA A YAU!
Shekh Isah Muhammad Gidado wanda akafi sani da Mallam Isah Waziri.. An haifeshi a cikin garin Kano a shekarar 1925, kuma Da ne ga Wazirin kano Muhammadu Gidado. Yayi karatunsa na Allo a ciki da wajen kasar kano, sannan ya halarci makarantar koyon Aikin Shari'ah a cikin garin kano, daga bisani ya tafi Jami'ar Al-Azhar dake Egypt Inda ya karasa karatunsa. Kuma ya samu ilmin shari'ah da Koyarda Ilmin Addinin Musulunci.




Bayan ya gama karatunsa Sheikh Isah Waziri ya dawo kano inda ya fara aiki a Ma'aikatar Shari'ah ta kano, a matsayin Clerk daga bisani ya zama Registrar. kuma ya fara Tafsirin Alqu'ani mai tsarki a Garin Zakirai ta karamar hukumar Gezawa a wancan lokacin.




Bayan ya bar Aikin Gwamnati Mai martaba Sarkin kano Alh. Ado Bayero ya nadashi Limamin Masallacin Murtala dake kano, kuma anan yaci gaba da Tafsirin Alqur'ani mai girma. Shekh isah Waziri ya bada gudunmawa da dama a cik da wajen kano wajen Daukaka Addinin Musulunci, kuma yayi kokari wajen ganin anyi aiki da Shari'ar Musulunci a kasar kano ganin cewa Mafiya yawansu musulmi ne!




Sheikh Isah Waziri ya samu wannan sunan ne a lokacin yana Makarantar koyon aikin Shari'a Inda wani Malaminsu mai suna Sheikhul-Bashir yake fada masa ganin cewa Da ne ga Wazirin Kano Gidado. A maimakon yace masa Isah Muhammad Gidado, sai ya takaita sunan yake kiransa Isah Waziri.




Bayan da Limamin kano Kuliya ya tafi Aikin Ambasada a shekarar 1998, Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero ya nada Shekh Isah Waziri a Matsayin Bubban Limamin Kano. Sannan daga bisani An nadashi Wazirin Kano bayan da Dan-uwansa Wazirin Kano ya rasu.




A yau Juma'a 2/8/2013 azumi yana 24 Allah yayiwa Sheikh Isah Waziri rasuwa. Muna rokon Allah ya Gafarta masa ya kyauta Makwancinsa. Muma in tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani.

Tuesday, May 28, 2013

SARKIN DOGARAI DUMAMUSAU...

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU! Buya Mai Komo yana cewa.... Buzuzu baka dadin tauna Dorawa kashe mai zari, yai baki kirin da idanu yai jan idon Barkono, Jakarsa bata rama in ba damo da Macizai. Ya zama Gwanki matattarar 'yan kwari tsumma Madaukar cuta! Shine yakan zama gwanki matattarar Iblisai. Na kumbita kazamin gwarzo, Dan makama ka wuce kushe koda a dajin Gaba. Bawa tsare Sarkinka koda a Dajin Gaba. Baleru baban yaya, Sarkin Dogaran Hadejia, Shine yakan zama Gwanki Matattarar iblisai. Mata kubar kallonsa kayansa babu na zabe. Auya batai laya ba sai malami ya yarda! In malami ya yarda kudi biyan laya ne! Allah ya kyauta Kwanciya...

Saturday, April 27, 2013

TAURARINMU HADEJIAWA (4)

Image Hosted by ImageTitan.comHadejia A yau! Allahu Akbar!

ALH. ABDUL'AZIZ DANMASAGA :- Hakika Tarihin Hadejia bazai manta da wannan bawan Allah ba, yayi iya kokarinsa wajen taimakon rayuwar mutanen kasar Hadejia, musamman Talakawa Masu karamin karfi da Miskinai.

Yayi Amfani da Arzikin da Allah ya bashi ya kyautatawa Jama-ar kasar Hadejia. Allah ya gafarta masa.

Alh. Abdu Danmasaga Mutum ne mai fara'a da son ci gaban Al'umma, baya so yaga mutane suna zaman banza. Hakan tasa yake daukan mutane ya sanyasu Inda zasu koyi sana'a domin su dogara da kansu. Shine mutuminda duk ranar Juma'a ko Lahdi yake raba kudi ga 'yan makarantar Boarding, saboda yasan basa kusa da Iyayensu.

Ga kadan daga Ayyukansa da yayi na Alheri.

(1) yana sayen itace mota mota ana faskarawa a tarashi kuma a saidashi lokacin da yayi wahala akan kudi kadan.

(2) Ba'a fara sayan Itace ba a Makabarta sai bayan mutuwarsa, saboda ya bada fisabilillah. Allah yasa yana Aljannah.

(3) yana saida kalanzir a kankanin farashi musamman lokacinda watan Azumi ya karato ko kuma lokacin Damina.

(4) yana saida fetur a farashi mai sauki yayinda ake wahalar sa. Ko ya zama babu a gari.

(5) shi yake sakawa ayiwa Mahaukata Aski, ya basu Abinci kuma ya dinka musu sabbin Riguna.

Dama ace masu kudi ko 'yan siyasa zasu koyi hali Irin nasa, da kasa ta kwana lafiya!

Allah ya Gafarta masa, Allah yasa mu koyi Hali Irin nasa. Alh. Abdul'aziz Danmasaga. Hadejia A yau.

Sunday, April 21, 2013

TARIHIN SARKIN HADEJIA UMARU DAN BUHARI DA ZUWAN SARKIN DAMAGARAM HADEJIA..

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU!



SARKIN HADEJIA UMARU: A SHEKARAR 1863 allah ya yiwa Sarkin Hadejia Buhari rasuwa a Yakinsu da sukayi da Gogaram (bade). Ko da aka dawo Hadejia aka binne shi sai Manyan fadawan Hadejia wadanda akwai Amana tsakaninsu dashi Buhari. Kamar SARKIN AREWA TATA GANA DA SARKIN YAKI JAJI suka jajirce Sai an Nada UMARU DAN BUHARI SARKIN HADEJIA. kuma hakan Akayi!


SARKIN HADEJIA UMARU NA BIYU an nadashi yana da shekara Goma sha Takwas (18). Kuma manyan fadawan Mahaifinsa sune suke gudanar da Sarautar tunda shi yaro ne. Kuma a zamaninsa Sarkin Damagaram Tanimu ya kawo yaki Hadejia. Kuma yayi sansani a Arewa da Hadejia daga nan har Jigawar Kasim mutanensa ne. saida yayi kwana Arba'in ana yaki amma Hadejiawa basu fasa wasanninsu na dandali ba. Sannan kuma basu fasa duk harkokinsu na kasuwa ba, su kuma mutanen Sarkin Damagaram suna kaiwa farmaki kauyuka suna kwace musu kaya! Sannan sun hana mutanen kauyuka shigowa Hadejia domin saye da sayarwa. A nan kuma sun hana Makiyaya kiwon Dabbobinsu, Sai sarkin Arewa yasa akayi sanarwa a Hadejia cewa: duk mai dabbobi gobe ya sako su za'a kaisu kiwo, kuma hakan sukayi suka saki dabbobinsu Sarkin Arewa da Mutanensa sukaje sukayi kiwon suka dawo. Ta wajen Dan-Rago kusa da Maficin Sarki.

Da Abin ya ishi Mutanen Hadejia sai suka Sanar da Sarkin yakin Hadejia Jaji, sai ya tara Fadawan Hadejia yace Naji ance Sarkin Damagaram yazo, Yau wajen kwana 40, sukace hakane! Sai sarkin Yaki yace so kuke yazo ya koremu daga Garin?

Da safiya tayi sai sarkin yaki Jaji ya hau dokinsa ya dauki Takobinsa ya fita yacewa sarkin Kofa in ya fita ya rufe Kofar Gari, kuma ko an koroshi karya sake ya bude, idan ya bude masa to zai kashe shi. Sarkin yaki Jaji yaje ya fara baza Mayakan sarkin Damagaram yana korasu, saida ya korasu har Rumfar Sarkin Damagaram ya dawo da niyyar Washegari aci gaba da yaki.

Da sarkin Damagaram yaga anyi haka sai ya tara Hakimansa da fadawa yace gobe zamuci Hadejia da yaki. Suka amsa suna Alwashi, bayan an baje sai Chiroman Damagaram ya samu sarki yace masa Shawara nazo in bayar, sarki ya yarda. Chiroma yacewa Sarkin Damagaram duk garin da mukaje musu yaki basu da sukuni saboda suna tsoronmu, Amma yau kwananmu Arba'in (40) Hadejiawa basu fasa duk abinda sukeyi ba! Kuma mun samu Labarin Sarkin Hadejia bai san munzo ba, yacewa sarki Ina ganin ya kamata ko mu shiga mu yakesu ko kuma mu koma Gida!

Wata rana ana yaki Sai aka harbi dokin Sarkin Arewa! Koda ya mutu sai akaje gida aka dauko wani Dokin aka cire kayan wancan Dokin aka sakawa wanda aka kawo. Tata gana ya koma kan doki, kashe gari ana cikin yaki sai Tata gana ya sauko daga Dokinsa yayi alwala ya koma kan Dokin, to ashe Sarkin Damagaram yana kallon su sai yace Lalle Sarkin Hadejia ya Isa ana yaki ka sauko kayi alwala? Jiya ma an kashe masa Doki amma saida akaje aka dauko wani a gari? Sai Zagin Sarkin Damagaram yace ai ba Sarkin Hadejia bane Yaronsa ne! Sai Sarkin Damagaram Tanimu yace to Ina Sarkin Hadejian? Sai zaginsa yace ai ance yana gida tunda aka fara yakin nan bai taba zuwa ba. Sai sarkin Damagarm yace wa fadawansa Gobe zamu bar Hadejia kar mu tsaya ayi ta kashemu. Saboda Sarkin Hadejia ya raina mu kwananmu Arba'in amma bai taba zuwa anyi yaki dashi ba? Wa yasan me zai mana in ya zo? Amma basu san Sarkin Yaro bane. Washe gari suka juya suka koma Damagaram. Kuma lokacinda sukazo Hadejia Da kaka ne! Anyi girbi Manoma basu gama Tare Amfaninsu ba. Shi yasa suka dade a Hadejia saboda akwai abinci da ruwa a kusa dasu.

SARKIN HADEJIA UMARU Mutum ne mai son Nishadi kowane Lokaci yakan fita Bakin kogi ko Gona Domin Debe kewa. Kuma anyi amfani da wannan Damar inda wata rana ya fita sai aka Rufe Masa Kofa. Koda yazo yaga kofa A rufe sai ya juya ya tafi Chamo ya zauna. Aka nada Kanin Mahaifinsa Sarkin Hadejia Wato HARU BUBBA. 1865-1885. Shi kuwa UMARU DAN BUHARI yayi zamansa a Chamo kuma Ya rasu a shekarar 1920. Allah yaji Kansu Ameen.

HADEJIA A YAU.

Friday, April 5, 2013

KHUDUBA DAGA MASALLACIN FANTAI HADEJIA...

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU! Daga Yaya Ilallah.


~~~ZUWA WAJEN BOKA~~~


Alhamdulillahi Rabbil Alamin. Muna farawa da sunan Allah wanda da Ikonsa komai ya kasance, da kuma Abinda zai kasance! Tsira da Aminci su tabbata ga Manzonsa Muhammadu s.a.w. Wanda ya aikoshi da zance mafi dadi wato Alqur-ani.


Alhamdulillahi Yau khuduba daga Masallacin Usman Bn Fodio dake cikin makarantar Fantai daga bakin Mal. Bashir Muhd Baima, ta yi magana ne ga hani zuwa wajen:- BOKA ko YAN TSUBBU. Wadda a lokacin yanzu shedan ya kada gangarsa wajen haska zukatan ashararu daga cikin mutane kamar 'yan siyasa, masu mulkin gargajiya da na gwabnati da kuma masu rike da wasu mukamai.


Manzon Allah s.a.w yace: Duk wadda ya je wajen Boka, ba za a amsa masa Sallarsa ta kwana 40 ba. In kuma ya yi imani da abun da ya fada, to ya kafurta da abun da Annabin ya zo da shi. Wani abu mafi muni da takaici, za ka ga matasa maza da mata na neman taimakon Bokaye wai da sunan Farin jini, neman mulki, mallakar miji da kokarin mallakewa zuciyar abokin soyayya ga samari da 'yan mata.


Haka dabi'ar ta kara watsuwa cikin zukatan wasu jahilai ta yadda in wani abu na musiba ya samesu , sai su tafi ga Boka don gano yadda wannan abu ya faru a gareshi. Ya manta da Allah ne ya Qaddara masa. Toh Allah kyauta.


Masu irin wanga dabi'a Allah shiryesu, mu kuma Allah ya karemu. Amen.

Monday, March 25, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) PART THREE (3)

HADEJIA A YAU.


DAGA M. MUHAMMAD IDRIS HADEJIA.


SHEIKH USMAN KADUNA *************** ­ Sheikh Usman Kaduna,daya daga cikin manyan malaman Jihar Jigawa,kololuwa­r malunta a masarautar Hadejia, daya daga cikin jigogin "council of ulama" na jihar jigawa, shehi kuma madugun tafiyar Darikar Tijjaniya a masarautar nan. Gaba daya rayuwar malam akan yada ilmin addini ta kare.

Malam ya yi aiki a L.E.A a matsayin babban inspector na Arabiya.Ya sha yin Board Member a Hukumar Alhazai ta jiha.

Gidan malam jami'a ce ta masarautar Hadejia. Malam malamin malamai ne domin duk wani malami mai shekaru saba'in zuwa kasa in malam bai karantar da shi ba to ya karantar da malaminsa. Malam ­ ya yi nisa a fagen bayarda ilmi domin har daga kasashen ketare ana zuwa wannan jami'a tasa.


Almajiran malam ne suka fara kafa Islamiya ta dare domin magance hira marar amfani da matasa kan yi a cikin wannan gari.

Malamyana gabatar da tafsiri a kowane watan azumi a dukshekara wanda ke samun halartar jama'a masu yawa. Bayan karantarwa ta yau da kullum malam yana karantar da hadisi a ranar kowace juma'a tsakanin magariba da isha'i. Allah ya karawa malamlafiya ya kuma ba shi ladan Ayyukanda yake na Alkairi.


ALHAJI HASHIMU AMAR(WAZIRIN HADEJI)*************** ­* Alhaji Hashimu Amar yana daya daga cikin tsofin 'yan bokon wannan masarauta, ajins­u daya da marigayi sarkin Hadejia Alh. Abubakar maje tun daga firamare har midil (Middle).


Alhaji Hashimu Amar a"internal revenue" ya yi aikinsa har ya kai kolokuwawato babban Darakta kuma anan ya yi ritaya. AlhajiHashimu ya dauki ma'aikata matuka a wannan masarauta har ma da wajenta.

Alhaji Hashimu dattijo ne mai gaskiya da rikon amana ya kare mutuncinsa da na masarautarsa matuka don haka wajen daukan aikinsa bai nuna kabilanci ba, babu ruwansa da kusa ko nesa, ko na gari ko kauye.

Wannan ya kara masa mutunci matuka a wannan masarauta. Alhaj­i Hashimu ya zama wazirin Hadejia a lokacin Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje kuma kullum yana hanya domin samo ci gaban wannan masarauta.

Hadejiawa suna masa addu'a Allah ya albarkanci zuriyarsa.

Saturday, March 23, 2013

HADEJIA EMIRATE

HADEIJA A YAU.

Authority : Mr. A. Campbell-Irons.

The Emirate of Hadejia contains an area of 2,768 square miles, and is divided into six Districts. It is situated to the north-east of Katagum, in the Northern Division. It is a disputed point whether in the tenth century.

Hadeija or Gobir formed one of the seven Haussa States. In the Kano Chronicle there is a mention that the son of the Sarkin Machina came to Kano in the reign of Yakubu (1452-63) and was made Chief over Hadeija, with the title of Sarkin Gabbas.

It became a Fulani Emirate at the time of the Jihad, Sambo receiving a flag from Othman Dan Fodio. His elder son Buhari made himself King in defiance of the Sarkin Musulmi's edict in favour of his younger brother ; and, obtaining the support of the Shehun Bornu, defeated all opponents. His reign was one long succession of wars and he was finally killed in battle at Gorgaram about 1863.

Hadeija sent in submission to the British in 1903. In 1904 the British occupied the country, but the fifth Chief opposed their advent and was overthrown and killed in 1906, and Haruna appointed in his place. He died in 1909, and was succeeded by the Chiroma Abdulkadir.

In that same year the Beiyut-el-Mal (Baitilmalu) was started.

The population number some 115,448, and consists of Kanuri, Fulani, Auyokawa, Maguzawa from Kano, Koyamawa, Beddawa, Ngizimawa, Mangawa.

There is a town of historic interest in Hadeija named Garungabas, but which in old times bore the name of Biram, which was originally of great influence. It was founded by Arabs from Bagdaza or Baghdad. One Muktari, or Bayajibda, with his younger brother Biram, Migrated west until they reached Birnin Bornu (Kukawa), where the Shehu gave Muktari a town and his daughter in marriage. Muktari was presently compelled to flee, but left his wife on the road, where she gave birth to Biram, who founded Garin Gabbas, Muktari continuing his journey as far as Daura, where he slew the celebrated serpent and married the Queen.

Another version of the legend is that it was Buram, the younger brother, who founded Garingabas.

A descendant of this Arab family still reigns as Chief. Hadejia A yau.