
Reference--- Assessment reports by K. L. Hall, Assistant District officer Hadejia District Kano Province.14th/July/1915.
"" />
HADEJIA A YAU! Wannan Dandali Na kirkireshi don bada Tarihin Kasar Hadejia, da Tarihin Sarakunan ta, da wadanda suka bada Gudunmawa wajen Inganta Al'adun Gargajiya. Hadejia A yau. Ismailasabo@gmail.com




posted from Bloggeroid
Koda yake a lokacin wannsn garin da ake Kira Doran Baga mutanenmu ne suka je suka kafa Daba a kusa da gabar Kogi. Anan ne sukaci gaba da zamansu suna Kamun Kifi da sauran Albarkatun ruwa sannan su sarrafa su kawo Maiduguri da wasu sassa na jihar Yobe su sayar. Haka gari yaci gaba da girma sakamakon zuwan mutane Masunta domin su samu abinda zasuci da Iyalensu. Sakamakon gari ya zama gari har sai ake kiran Dabar tasu DORON BAGA.
Akasarin mutanen da suka tafi daga kasar Hadejia mutanen Kafinhausa ne da kuma yankunan Kirikasamma da Guri, idan ka lissafa wancan lokacin zuwa yau zai baka shekara 44. Wadannan mutanen wasunsu sun bar garuruwansu ba tare da suna dawowa suna gaida Iyayensu ba, wasunsu kuma har iyayen nasu suka bar Duniya basuzo sun gansu ba,wasu a cikinsu sun manta yanda yanayin garinsu ma yake saboda sun samu Duniya acan. Da yake ba duk aka taru aka zama daya ba wasu sukan zo su gaida 'yan-uwansu da abokan Arziki sannan su koma tunda Allah yayi zamansu acan.
RIKICIN BOKO HARAM....
A cikin Shekarar 2008/2009 Rikicin Boko Haram ya faru a Gabashin Nigeria, musamman yankunan Jihar Borno da Yobe da wasu sassa na Adamawa da Bauchi da Gombe, wanban rikici yayi Asarar Rayuka da Dukiyoyi masu dinbin yawa, inda akayi ta kone Gidaje da Kasuwanni da wuraren Sana'a. Wannan ne yasa wadancan mutane da na Ambata a sama wadanda Kwakuduba tasa suka bar garuruwansu sai suka fara tunanin su dawo gida, sakamakon fadin Hausawa " Giji Lahira ce" anan ne fa suka fara dawowa ba tare da abinda suka tara a can ba, wasu sun dawo gida sun tarar duk wadanda suka sani sun mutu wasu kuma tsufa ya kama su.
Daga Muhammad Yawale....
.
text-align: center;">AYYUKAN DA YAYI:
Yayi malamin makaranta a lokacin (N.A) ta Hadejia na tsawon shekaru 2, a karkashin tsohon Head master marigayi Alh Abdu maigari Tafidan Hadejia, yayi malamin makaranta a primary ta dubantu a 1965, yayi sakataren karamin minista na MADAKIN Hadejia Muhammadu Gauyama, a ma'aikatar tsaro ta kasa a lagos bangaren jiragen sama (Air-force) a shekarar 1965-1966,
Yayi malami a kotun babban alkali lokacin alkali Dahiru. A shekarar 1966-1968, yayi malamin Turakin Hadejia lokacin Turaki Adamu, yayi Akawu a ma'aikatar mulki ta (N.A), yayi sakataren karamar hukuma a wadannan wurare Bichi, ringim, gumel, wudil, babura, gezawa, kafin hausa, dawakin tofa yayi sakatare na musamman a karamar hukumar birni da kewaye (kano municipal council).
Ya rike mukamin DPM a kananan hukumomin garki, malam madori, Taura a inda yayi ritaya. Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya nadashi Tafidan Hadejia Dan majalisar sarki a shekara ta 1994, cikin yardar Allah kuma Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar ya nadashi Chiroman hadejia a ranar asabar 13 ga watam march 2004 a inda ya gaji yayansa chiroman Hadejia Alh. muhammad Abbas.
Marigayi chiroman Hadejia mutum ne mai jajircewa kan gaskiya da rikon amana akan harkar da aka dorashi kuma ya nemawa mutane da dama aiki a lokacin gwamnati kuma duk abinda ya gani ba daidai ba baya yin shiru sai yayi magana hakazalika bai yarda kayimasa zancen waniba. Marigayi chiroman Hadejia ya rasu ranar juma'a da daddare 03/10/2015 bayan ya sha fama da jinya muna rokon Allah ya jikansa ya kuma kyautata bayansa.

posted from Bloggeroid