![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEhXY6NWrvaceLROJg6ERSYvYQbe3Lo1SzhOJezY9pEWkODkDr7BEf9usnf4005y5m2slnqvsRG6zSPTAH_f2tn7jGhM1siNpfRirEJdQOv7qSU6GyJu6JxriUYnjZgf9IqG9vlnbD5EDLeI/s400/581163_402902489755713_1979872597_n.jpg)
HADEJIA A YAU! An sake sanya dokar awa Ashirin da hudu a Jihar Kaduna Sakamakon Tashin hankalin da ya biyo bayan harin bom din da aka kai a Zariya da kaduna. An samu labarin Jiya da dadare matasa sunyi ta kai farmaki a junansu da niyyar daukan fansa. Haka kuma yau ma fada ya barke a Unguwanni daban daban a kaduna. Dukda dokar hana zirga zirga da Gwamnan jihar ya saka. A Damaturu ma ta jihar Yobe rikicin ya lafa kuma suma ansa dokar Hana zirga zirga. Mutanen garin dai sun bayyana wannan abin a matsayin Gazawar Gwamnatin tarayya na kasa magance matsalar tsaro.
No comments:
Post a Comment
RUBUTA RA'AYINKA!