![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEgE34U1axZcvLPtkZcJkzqygNrEGTiSef8bQRVJE6e7XKPb-sS5TICd3IoLEwmucFDsgxx805_tPSg7FgcjNNHN6arzZyF1MnE13lFfO9rODpfYeMwXFBakzt1nMwhIM94xbCMeVGXoPDhm/s320/581163_402902489755713_1979872597_n.jpg)
HADEJIA A YAU! Rahotanni daga jihar Kaduna ya nuna cewa Har yau rikici bai lafa ba dukda Dokar hana zirga zirga da aka sanya a Jihar. Ko a yammacin yau anji Karar harbe harbe da kone kone a yankin Badarawa,Unguwar yero da kuma wasu sassa a Unguwar Dosa. Wani ma'aikacin Gidan Redio ya ruwaito cewa An harbi wani yaro a Gabansa, Bayan an kaishi asibiti daga bisani ya cika. Allah ya mana maganin wannan masifa! Kwanaki hudu dai kelau ana zaman Dar dar a Jihar Kaduna Rikicinda ya rikide ya zama na kabilanci da Addini.
No comments:
Post a Comment
RUBUTA RA'AYINKA!