"" /> HADEJIA A YAU!: A FADAWA HADEJIYAWA KASUWA. TARIHIN KAFUWAR GANDUN BUNDUGOMA

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, June 4, 2025

A FADAWA HADEJIYAWA KASUWA. TARIHIN KAFUWAR GANDUN BUNDUGOMA

HADEJIA A YAU!
TARIHIN KAFUWAR GANDUN BUNDUGOMA. 

Daga Umar Yusuf Da'awa 

A Zamanin Mulkin Sarkin Haɗejiya Haru Bubba wadda ya yi mulki a shekarar 1865-1885 ne, kasuwa ta mamaye Kudancin Haɗejiya, Ma'ana ɓagaren Kudu da garin Haɗejiya. Kasuwa ta kafu jama'a sun shigo garin Haɗejiya, kama daga Turawa (Turkiyya) Larabawa dama Hausawammu na gida da na wajen kasar nan. 

Saboda shahara da Haɗejiya tayi na noman Gyaɗa da Auduga da Dawa da Gero dadai sauran su, wannan tasa jama'a suka shigo Haɗejiya daban daban. Haka aka yi ta kasuwanci a wannan yanki, har akwai lokacin da Jirgi yakan sauka a Haɗejiya mai sauƙar Ungulu na larabawa da Turawa a basu Auduga da gyaɗa, su kuma su kawo mana tufafin irin su Abaya da kayan mulki irin na gabas. Kasuwa tayi ƙarfi jama'a sun cika, sai ɓarayi suka fara ziyartar wannan kasuwa suna yin wasoso, har labari ya iskewa Sarki, nan take sarki ya tashi ɗaya daga cikin Fadawansa a bangaren 'Yan Baka wadda ake ƙira da Bundugoma, yace yaje ya sa ido ga yan kasuwa ya tabbatar sun yi saye da sayarwa lafiya babu tsoro. 

Bundugoma ya amsa umarnin sarki, in ya tafi tun Safe har yamma shi da yaran sa suna kula da 'yan kasuwa. Da yaga haka kawai sai ya tare wannan wuri gaba ɗaya da zama, ya share fili ya gina bukkar sa tare da yaran sa. Wannan tasa har yau ake ƙiran wannan wuri da Gandun Bundugoma. Bundugoma kuwa ana nufin mai Bindiga a yaren Manganci, domin shi Bamange ne. Kuma sune suke Sarautar Galadiman Bindiga a Hadejia. Kasuwa ta ci gaba da ci, kuma tafi cika ranar Lahadi saboda Baki suna zuwa ne ranar Asabat su kwana lahdi su ci kasuwa su wuce. 

A zamanin sarkin Hadejia Abdulkadir Turawa suka umarci a dawo da kasuwa yamma da gari don dacewa da zamani, sai kasuwa ta dawo duriyar yamma da gari wato Unguwar Rinde inda kasuwa take yanzu.

No comments:

Post a Comment

RUBUTA RA'AYINKA!