"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, August 11, 2013

JAWABIN ALH. BAIDI GAJO YELLEMAN A BUBBAN TARO DA AKAYI DON HADIN KAN Al'UMMAR MASARAUTAR HADEJIA. (KASHI NA DAYA 1)

Free Web Proxy
Jamaa Salamu Alaikum. Na tsaya gabanku ne a game da izinin da aka mani akan in yi bayani gameda “Cusawa matasa kishin masarautar Hadejia”. Shi dai kishi wani kauna ne da mutun yake dashi na wani abu, ko Kasa, Addini, Mutum da sauransu. Misali Kishin da mutum yakewa kasarsa, Mace da take game da mijinta, mutum yake game da addinsa. Wannan tsanannin kishin zai iya sa mutum yayi dukkan abinda zai iya domin yaga cewa ya amfani abinda yake kishin kuma yakare
martabarsa. Kakan yi amfani da kishi don ka cimma kyakkyawar manufa mai amfani.


Wani babban alamarine da zai sa kayi duk abinda zaka iyayi iyakar karfinka domin shi wanda kake kishin ko abinda kake kishin.


Kasar Hadejia al’ummace da Allah Yayiwa dimbin albarka ta fannoni daban daban na rayuwa Kamar dimbin masu Ilimin addini dana zamani, Manyan Sarakuna, Attajirai, Manyan yan siyasa, Manyan Maaikata tun shekaru aru aru. Idan nace kasar Hadejia ina nufin Hadejia, Auyo, Birniwa, Guri, Kafin Hausa, Kaugama, Kiri kasamma da Malam Madori.


Bari muga yanda maganar kishi ta shigo a harkar jamaar Hadejia. Sanin kowane cewa yakamata ace Hadejia ta wuce inda take dinnan kasancewarta Mai sarautar daraja ta daya tun shekaru aru aru, kuma mutanenta ne suke mamaye aikin Gwamnati tun Kano State har yanzu a Jigawa State sannan kuma a gwamnatin tarayya. To amma har yanzu mun san akwai sauran abubuwa da yawa da muke bukata don mu cimma burinmu na samarda abubuwan more rayuwa ga jamaarmu. Su
wadannan abubuwan more rayuwa kuma suna samuwane ta hanyoyi daban daban. Jamaa zasu taru su hada karfe da karfi don su
samarda wadannan abubuwa.


Amma almuhimmi shine abinda zaa samowa jammaa daga hukuma, wato Gwamnati.
Hanyoyin samu wadannan abubuwa shine zai nuna tsananin kishin da zakayi na samosu daga hukumar da abin ya shafa. Babban
maaikacin Gwamnati zai iya samawa matasa aiki a gwamnati, zai iya kawo Maaikata (Project), ko Makaranta, Titi, Asibiti. Ko ruwansha a bangarensa. Dan Siyasa zai iya amfani da mukaminsa yakawo duk abubuwan da na lissafa a sama. Attajirai zasu iya kawo kamfanoni. To idan wadannan suka hada karfe da karfi, nan da nan zaka ga
abubuwa sun bunkasa ta kowane fanni kuma jammaa sun sami biyan bukata. Ina tunanin ko muna da irin wannan tsananin kishi da nake nufi anan. Idan kuma muna dashi, to ina tunani ko muna amfani dashi yanda yakamata don ciyarda alummarmu gaba.


In Ciyaman Local Government bashi da kishi, ina zaiyi aiki?


Idan Dan Majalisa bashi da kishi, ina zai yiwa jamaa kyakkyawan wakilci?


Idan babban maaikacin gwamnati bashi da kishi, ina zai kawo ayyuka (Projects) garinsu?
Da sauransu.


Anan ina so inyi wasu yan tambayoyi: MU HADU A KASHI NA BIYU (2) DON JIN TAMBAYOYIN.

JAWABIN ALH. BAIDI GAJO YELLEMAN A BUBBAN TARON HADIN KAN AL'UMMAR MASARAUTAR HADEJIA. (KASHI NA BIYU 2)

Free Web Proxy Hadejia A yau.


Anan ina so inyi wasu yan tambayoyi:


1. Kana da kishi ne sai ka jira Mai Martaba Sarki ya tura ma tawaga a gaya maka jamaar Hadejia suna bukatar abu?


2. Kana da kishi ne sai ka jira har jamaa sunyi zanga zanga kafin ka biya musu bukata?


3. Kana da kishi ne baka son zuwa garinku ko cikin jamarka?


4. Kana da kishi ne kake yiwa garinka shigar dare kuma a mota mai tinted glass don kada a ganka?


5. Kana da kishi ne zaka rike mukamin gwamnati har kayi ritaya baka kari jamaarka da komai ba? Da sauransu.


Shi kishi ne zai sa kayi abu ba sai an sa ka ba, kuma in kayi ba sai an gode makaba. Rashin wakilci mai kyau duk rashin kishi ne yake kawo shi. Saboda haka idan dai muka dore akan wadannan abubuwa biyar da na lissafa a sama, to gaskiya babu inda zamu.


A duniyarmu ta yau, da wuya wani ya dafa maka abinci ya sa ma a bakinka. Kai ne zaka yunkura ka nemowa kanka yancinka ko kuma abinda zai amfaneka. Sabida haka dole musa kishi a zukatanmu don mu samowa lardinmu abinda yakamata daga gwamnatin Jiha har gwamnatin tarayya.
Babban burinmu shine mu sami Jiha (Hadejia State). Domin idan ka sami jiha, to duk wasu abubuwa na ci gaba zasu zo da sauki.


To amma kafin mu sami jihar, yakamata muci gaba da amfani da dimbin arzikin da Allah Ya bamu na masu ilimi, Sarakuna, maaikata,
manyan yan siyasa da yan kasuwa domin cimma duk wani cigaba da muke bukata.


Alhamdulillahi muna da Manyan maikata kamar Directors Permanent Secretaries, Ministoci, Soja, Yan Sanda da sauransu. Idan muka hada karfe da karfi muka sa kishi a alaamuranmu babu inda bazamu kaiba. Tarihi ya nuna akwai inda mutum daya mai kishi ya kawowa jamaarsa cigaba.
Saboda haka kara jaddadawa iyayenmu da yayyenmu da kuma musamman matasa manyan gobe gameda duk abinda zasuyi su sa kishi da hadin kai a gaba. Mu zama tsintsiya madaurinki daya muna haduwa da juna muna tattaunawa muna tsaida shawarwari kuma muna daukan dukkan matakin da yakamata don muga cewa mun cimma burinmu.
Matasa kune kunnenmu, kuma kune idanunmu. Saboda haka duk abinda yakamata Jamaa su sani, ku yakamata ku jaddadashi domin a dauki mataki. Har abada yin shiru baya warware matsala sai dai ya kawo rashin jituwa marar amfani Allah Yasa wannan taro ya zama dalilin samarda hadin kai da cigaba ga alummar Hadejia da Jigawa baki daya.

Thursday, August 8, 2013

HAWAN SALLAR AZUMI NA 8/8/2013 ALHAMIS.

Hadejia A yau. Daga Muhd Yawale Hadejia >


kamar yadda Aka sani Hawan sallar Azumi yana da tarihi mai tsawo a cikin Garin Hadejia, wannan sallar ma A bisa al'adar masarautar hadejia ranar sallah maimartaba sarki zai fito daga gida da safe, akafa tareda sauran mutanan fada domin zuwa filin idi. Dukda cewa za'ayi sallar ne a Bubban Masallacin Juma'a na cikin gari. Sakamakon ruwan sama da akayi kuma yayi ta'adi, Mai martaba sarki ya dage Hawan sallah domin Jajantawa ga wadanda ruwa yayi musu ta'adi.


Ga bayanin yanda Hawan sallah yake kasancewa da kuma ta Gurarenda ake bi. Bayan an idar sallar idi liman ya kammala huduba,sai hakimai da sauran mahaya dawaki su hau, sannan maimartaba shima zai hau dokinsa tare da Dandalmu, zai bi ta kasuwar kuda zuwa Titin yahai zuwa makera, sannan zai bi ta makwallah zuwa kofar Liman.


Idan maimartaba sarki yazo daidai kofar liman yakan tsaya domin karfar Jafi daga Hakimai. Wanda hakan ta samo Asali ne Tun Lokacinda Sarkin Hadejia Muhammadu Mai shahada ya dawo daga Yakin Madarumfa, ya tsaya a wannan Gurbin Inda su Jarumansa suke zuwa suke masa Jinjina. Amma a lokacin yana Hakimi ne kafin ya zama sarki. Bayan ya zama sarkin Hadejia sai ya maidata Al'ada wato duk sallar Azumi da Layya zai tsaya Hakimai suzo suyi masa jafi.


Daga nan kuma sai maimartaba sarki ya karasa rumfar manyan baki domin gabatarda jawabin sallah, bayan nan kuma sai maimarta ya karasa gida ya sauka tareda sauran hakimai.


Wannan shine Bayanin Hawan sallar Azumin wannan shekara a takaice da fatan Allah yasa ayi hawa lafiya a sauko lafiya. Allah yaja zamanin maimartaba sarki.

Saturday, August 3, 2013

TAKAICACCEN TARIHIN SHEIKH ISAH WAZIRI (WAZIRIN KANO)

HADEJIA A YAU!
Shekh Isah Muhammad Gidado wanda akafi sani da Mallam Isah Waziri.. An haifeshi a cikin garin Kano a shekarar 1925, kuma Da ne ga Wazirin kano Muhammadu Gidado. Yayi karatunsa na Allo a ciki da wajen kasar kano, sannan ya halarci makarantar koyon Aikin Shari'ah a cikin garin kano, daga bisani ya tafi Jami'ar Al-Azhar dake Egypt Inda ya karasa karatunsa. Kuma ya samu ilmin shari'ah da Koyarda Ilmin Addinin Musulunci.




Bayan ya gama karatunsa Sheikh Isah Waziri ya dawo kano inda ya fara aiki a Ma'aikatar Shari'ah ta kano, a matsayin Clerk daga bisani ya zama Registrar. kuma ya fara Tafsirin Alqu'ani mai tsarki a Garin Zakirai ta karamar hukumar Gezawa a wancan lokacin.




Bayan ya bar Aikin Gwamnati Mai martaba Sarkin kano Alh. Ado Bayero ya nadashi Limamin Masallacin Murtala dake kano, kuma anan yaci gaba da Tafsirin Alqur'ani mai girma. Shekh isah Waziri ya bada gudunmawa da dama a cik da wajen kano wajen Daukaka Addinin Musulunci, kuma yayi kokari wajen ganin anyi aiki da Shari'ar Musulunci a kasar kano ganin cewa Mafiya yawansu musulmi ne!




Sheikh Isah Waziri ya samu wannan sunan ne a lokacin yana Makarantar koyon aikin Shari'a Inda wani Malaminsu mai suna Sheikhul-Bashir yake fada masa ganin cewa Da ne ga Wazirin Kano Gidado. A maimakon yace masa Isah Muhammad Gidado, sai ya takaita sunan yake kiransa Isah Waziri.




Bayan da Limamin kano Kuliya ya tafi Aikin Ambasada a shekarar 1998, Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero ya nada Shekh Isah Waziri a Matsayin Bubban Limamin Kano. Sannan daga bisani An nadashi Wazirin Kano bayan da Dan-uwansa Wazirin Kano ya rasu.




A yau Juma'a 2/8/2013 azumi yana 24 Allah yayiwa Sheikh Isah Waziri rasuwa. Muna rokon Allah ya Gafarta masa ya kyauta Makwancinsa. Muma in tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani.

Tuesday, May 28, 2013

SARKIN DOGARAI DUMAMUSAU...

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU! Buya Mai Komo yana cewa.... Buzuzu baka dadin tauna Dorawa kashe mai zari, yai baki kirin da idanu yai jan idon Barkono, Jakarsa bata rama in ba damo da Macizai. Ya zama Gwanki matattarar 'yan kwari tsumma Madaukar cuta! Shine yakan zama gwanki matattarar Iblisai. Na kumbita kazamin gwarzo, Dan makama ka wuce kushe koda a dajin Gaba. Bawa tsare Sarkinka koda a Dajin Gaba. Baleru baban yaya, Sarkin Dogaran Hadejia, Shine yakan zama Gwanki Matattarar iblisai. Mata kubar kallonsa kayansa babu na zabe. Auya batai laya ba sai malami ya yarda! In malami ya yarda kudi biyan laya ne! Allah ya kyauta Kwanciya...

Saturday, April 27, 2013

TAURARINMU HADEJIAWA (4)

Image Hosted by ImageTitan.comHadejia A yau! Allahu Akbar!

ALH. ABDUL'AZIZ DANMASAGA :- Hakika Tarihin Hadejia bazai manta da wannan bawan Allah ba, yayi iya kokarinsa wajen taimakon rayuwar mutanen kasar Hadejia, musamman Talakawa Masu karamin karfi da Miskinai.

Yayi Amfani da Arzikin da Allah ya bashi ya kyautatawa Jama-ar kasar Hadejia. Allah ya gafarta masa.

Alh. Abdu Danmasaga Mutum ne mai fara'a da son ci gaban Al'umma, baya so yaga mutane suna zaman banza. Hakan tasa yake daukan mutane ya sanyasu Inda zasu koyi sana'a domin su dogara da kansu. Shine mutuminda duk ranar Juma'a ko Lahdi yake raba kudi ga 'yan makarantar Boarding, saboda yasan basa kusa da Iyayensu.

Ga kadan daga Ayyukansa da yayi na Alheri.

(1) yana sayen itace mota mota ana faskarawa a tarashi kuma a saidashi lokacin da yayi wahala akan kudi kadan.

(2) Ba'a fara sayan Itace ba a Makabarta sai bayan mutuwarsa, saboda ya bada fisabilillah. Allah yasa yana Aljannah.

(3) yana saida kalanzir a kankanin farashi musamman lokacinda watan Azumi ya karato ko kuma lokacin Damina.

(4) yana saida fetur a farashi mai sauki yayinda ake wahalar sa. Ko ya zama babu a gari.

(5) shi yake sakawa ayiwa Mahaukata Aski, ya basu Abinci kuma ya dinka musu sabbin Riguna.

Dama ace masu kudi ko 'yan siyasa zasu koyi hali Irin nasa, da kasa ta kwana lafiya!

Allah ya Gafarta masa, Allah yasa mu koyi Hali Irin nasa. Alh. Abdul'aziz Danmasaga. Hadejia A yau.

Sunday, April 21, 2013

TARIHIN SARKIN HADEJIA UMARU DAN BUHARI DA ZUWAN SARKIN DAMAGARAM HADEJIA..

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU!



SARKIN HADEJIA UMARU: A SHEKARAR 1863 allah ya yiwa Sarkin Hadejia Buhari rasuwa a Yakinsu da sukayi da Gogaram (bade). Ko da aka dawo Hadejia aka binne shi sai Manyan fadawan Hadejia wadanda akwai Amana tsakaninsu dashi Buhari. Kamar SARKIN AREWA TATA GANA DA SARKIN YAKI JAJI suka jajirce Sai an Nada UMARU DAN BUHARI SARKIN HADEJIA. kuma hakan Akayi!


SARKIN HADEJIA UMARU NA BIYU an nadashi yana da shekara Goma sha Takwas (18). Kuma manyan fadawan Mahaifinsa sune suke gudanar da Sarautar tunda shi yaro ne. Kuma a zamaninsa Sarkin Damagaram Tanimu ya kawo yaki Hadejia. Kuma yayi sansani a Arewa da Hadejia daga nan har Jigawar Kasim mutanensa ne. saida yayi kwana Arba'in ana yaki amma Hadejiawa basu fasa wasanninsu na dandali ba. Sannan kuma basu fasa duk harkokinsu na kasuwa ba, su kuma mutanen Sarkin Damagaram suna kaiwa farmaki kauyuka suna kwace musu kaya! Sannan sun hana mutanen kauyuka shigowa Hadejia domin saye da sayarwa. A nan kuma sun hana Makiyaya kiwon Dabbobinsu, Sai sarkin Arewa yasa akayi sanarwa a Hadejia cewa: duk mai dabbobi gobe ya sako su za'a kaisu kiwo, kuma hakan sukayi suka saki dabbobinsu Sarkin Arewa da Mutanensa sukaje sukayi kiwon suka dawo. Ta wajen Dan-Rago kusa da Maficin Sarki.

Da Abin ya ishi Mutanen Hadejia sai suka Sanar da Sarkin yakin Hadejia Jaji, sai ya tara Fadawan Hadejia yace Naji ance Sarkin Damagaram yazo, Yau wajen kwana 40, sukace hakane! Sai sarkin Yaki yace so kuke yazo ya koremu daga Garin?

Da safiya tayi sai sarkin yaki Jaji ya hau dokinsa ya dauki Takobinsa ya fita yacewa sarkin Kofa in ya fita ya rufe Kofar Gari, kuma ko an koroshi karya sake ya bude, idan ya bude masa to zai kashe shi. Sarkin yaki Jaji yaje ya fara baza Mayakan sarkin Damagaram yana korasu, saida ya korasu har Rumfar Sarkin Damagaram ya dawo da niyyar Washegari aci gaba da yaki.

Da sarkin Damagaram yaga anyi haka sai ya tara Hakimansa da fadawa yace gobe zamuci Hadejia da yaki. Suka amsa suna Alwashi, bayan an baje sai Chiroman Damagaram ya samu sarki yace masa Shawara nazo in bayar, sarki ya yarda. Chiroma yacewa Sarkin Damagaram duk garin da mukaje musu yaki basu da sukuni saboda suna tsoronmu, Amma yau kwananmu Arba'in (40) Hadejiawa basu fasa duk abinda sukeyi ba! Kuma mun samu Labarin Sarkin Hadejia bai san munzo ba, yacewa sarki Ina ganin ya kamata ko mu shiga mu yakesu ko kuma mu koma Gida!

Wata rana ana yaki Sai aka harbi dokin Sarkin Arewa! Koda ya mutu sai akaje gida aka dauko wani Dokin aka cire kayan wancan Dokin aka sakawa wanda aka kawo. Tata gana ya koma kan doki, kashe gari ana cikin yaki sai Tata gana ya sauko daga Dokinsa yayi alwala ya koma kan Dokin, to ashe Sarkin Damagaram yana kallon su sai yace Lalle Sarkin Hadejia ya Isa ana yaki ka sauko kayi alwala? Jiya ma an kashe masa Doki amma saida akaje aka dauko wani a gari? Sai Zagin Sarkin Damagaram yace ai ba Sarkin Hadejia bane Yaronsa ne! Sai Sarkin Damagaram Tanimu yace to Ina Sarkin Hadejian? Sai zaginsa yace ai ance yana gida tunda aka fara yakin nan bai taba zuwa ba. Sai sarkin Damagarm yace wa fadawansa Gobe zamu bar Hadejia kar mu tsaya ayi ta kashemu. Saboda Sarkin Hadejia ya raina mu kwananmu Arba'in amma bai taba zuwa anyi yaki dashi ba? Wa yasan me zai mana in ya zo? Amma basu san Sarkin Yaro bane. Washe gari suka juya suka koma Damagaram. Kuma lokacinda sukazo Hadejia Da kaka ne! Anyi girbi Manoma basu gama Tare Amfaninsu ba. Shi yasa suka dade a Hadejia saboda akwai abinci da ruwa a kusa dasu.

SARKIN HADEJIA UMARU Mutum ne mai son Nishadi kowane Lokaci yakan fita Bakin kogi ko Gona Domin Debe kewa. Kuma anyi amfani da wannan Damar inda wata rana ya fita sai aka Rufe Masa Kofa. Koda yazo yaga kofa A rufe sai ya juya ya tafi Chamo ya zauna. Aka nada Kanin Mahaifinsa Sarkin Hadejia Wato HARU BUBBA. 1865-1885. Shi kuwa UMARU DAN BUHARI yayi zamansa a Chamo kuma Ya rasu a shekarar 1920. Allah yaji Kansu Ameen.

HADEJIA A YAU.

Friday, April 5, 2013

KHUDUBA DAGA MASALLACIN FANTAI HADEJIA...

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU! Daga Yaya Ilallah.


~~~ZUWA WAJEN BOKA~~~


Alhamdulillahi Rabbil Alamin. Muna farawa da sunan Allah wanda da Ikonsa komai ya kasance, da kuma Abinda zai kasance! Tsira da Aminci su tabbata ga Manzonsa Muhammadu s.a.w. Wanda ya aikoshi da zance mafi dadi wato Alqur-ani.


Alhamdulillahi Yau khuduba daga Masallacin Usman Bn Fodio dake cikin makarantar Fantai daga bakin Mal. Bashir Muhd Baima, ta yi magana ne ga hani zuwa wajen:- BOKA ko YAN TSUBBU. Wadda a lokacin yanzu shedan ya kada gangarsa wajen haska zukatan ashararu daga cikin mutane kamar 'yan siyasa, masu mulkin gargajiya da na gwabnati da kuma masu rike da wasu mukamai.


Manzon Allah s.a.w yace: Duk wadda ya je wajen Boka, ba za a amsa masa Sallarsa ta kwana 40 ba. In kuma ya yi imani da abun da ya fada, to ya kafurta da abun da Annabin ya zo da shi. Wani abu mafi muni da takaici, za ka ga matasa maza da mata na neman taimakon Bokaye wai da sunan Farin jini, neman mulki, mallakar miji da kokarin mallakewa zuciyar abokin soyayya ga samari da 'yan mata.


Haka dabi'ar ta kara watsuwa cikin zukatan wasu jahilai ta yadda in wani abu na musiba ya samesu , sai su tafi ga Boka don gano yadda wannan abu ya faru a gareshi. Ya manta da Allah ne ya Qaddara masa. Toh Allah kyauta.


Masu irin wanga dabi'a Allah shiryesu, mu kuma Allah ya karemu. Amen.

Monday, March 25, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) PART THREE (3)

HADEJIA A YAU.


DAGA M. MUHAMMAD IDRIS HADEJIA.


SHEIKH USMAN KADUNA *************** ­ Sheikh Usman Kaduna,daya daga cikin manyan malaman Jihar Jigawa,kololuwa­r malunta a masarautar Hadejia, daya daga cikin jigogin "council of ulama" na jihar jigawa, shehi kuma madugun tafiyar Darikar Tijjaniya a masarautar nan. Gaba daya rayuwar malam akan yada ilmin addini ta kare.

Malam ya yi aiki a L.E.A a matsayin babban inspector na Arabiya.Ya sha yin Board Member a Hukumar Alhazai ta jiha.

Gidan malam jami'a ce ta masarautar Hadejia. Malam malamin malamai ne domin duk wani malami mai shekaru saba'in zuwa kasa in malam bai karantar da shi ba to ya karantar da malaminsa. Malam ­ ya yi nisa a fagen bayarda ilmi domin har daga kasashen ketare ana zuwa wannan jami'a tasa.


Almajiran malam ne suka fara kafa Islamiya ta dare domin magance hira marar amfani da matasa kan yi a cikin wannan gari.

Malamyana gabatar da tafsiri a kowane watan azumi a dukshekara wanda ke samun halartar jama'a masu yawa. Bayan karantarwa ta yau da kullum malam yana karantar da hadisi a ranar kowace juma'a tsakanin magariba da isha'i. Allah ya karawa malamlafiya ya kuma ba shi ladan Ayyukanda yake na Alkairi.


ALHAJI HASHIMU AMAR(WAZIRIN HADEJI)*************** ­* Alhaji Hashimu Amar yana daya daga cikin tsofin 'yan bokon wannan masarauta, ajins­u daya da marigayi sarkin Hadejia Alh. Abubakar maje tun daga firamare har midil (Middle).


Alhaji Hashimu Amar a"internal revenue" ya yi aikinsa har ya kai kolokuwawato babban Darakta kuma anan ya yi ritaya. AlhajiHashimu ya dauki ma'aikata matuka a wannan masarauta har ma da wajenta.

Alhaji Hashimu dattijo ne mai gaskiya da rikon amana ya kare mutuncinsa da na masarautarsa matuka don haka wajen daukan aikinsa bai nuna kabilanci ba, babu ruwansa da kusa ko nesa, ko na gari ko kauye.

Wannan ya kara masa mutunci matuka a wannan masarauta. Alhaj­i Hashimu ya zama wazirin Hadejia a lokacin Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje kuma kullum yana hanya domin samo ci gaban wannan masarauta.

Hadejiawa suna masa addu'a Allah ya albarkanci zuriyarsa.

Saturday, March 23, 2013

HADEJIA EMIRATE

HADEIJA A YAU.

Authority : Mr. A. Campbell-Irons.

The Emirate of Hadejia contains an area of 2,768 square miles, and is divided into six Districts. It is situated to the north-east of Katagum, in the Northern Division. It is a disputed point whether in the tenth century.

Hadeija or Gobir formed one of the seven Haussa States. In the Kano Chronicle there is a mention that the son of the Sarkin Machina came to Kano in the reign of Yakubu (1452-63) and was made Chief over Hadeija, with the title of Sarkin Gabbas.

It became a Fulani Emirate at the time of the Jihad, Sambo receiving a flag from Othman Dan Fodio. His elder son Buhari made himself King in defiance of the Sarkin Musulmi's edict in favour of his younger brother ; and, obtaining the support of the Shehun Bornu, defeated all opponents. His reign was one long succession of wars and he was finally killed in battle at Gorgaram about 1863.

Hadeija sent in submission to the British in 1903. In 1904 the British occupied the country, but the fifth Chief opposed their advent and was overthrown and killed in 1906, and Haruna appointed in his place. He died in 1909, and was succeeded by the Chiroma Abdulkadir.

In that same year the Beiyut-el-Mal (Baitilmalu) was started.

The population number some 115,448, and consists of Kanuri, Fulani, Auyokawa, Maguzawa from Kano, Koyamawa, Beddawa, Ngizimawa, Mangawa.

There is a town of historic interest in Hadeija named Garungabas, but which in old times bore the name of Biram, which was originally of great influence. It was founded by Arabs from Bagdaza or Baghdad. One Muktari, or Bayajibda, with his younger brother Biram, Migrated west until they reached Birnin Bornu (Kukawa), where the Shehu gave Muktari a town and his daughter in marriage. Muktari was presently compelled to flee, but left his wife on the road, where she gave birth to Biram, who founded Garin Gabbas, Muktari continuing his journey as far as Daura, where he slew the celebrated serpent and married the Queen.

Another version of the legend is that it was Buram, the younger brother, who founded Garingabas.

A descendant of this Arab family still reigns as Chief. Hadejia A yau.

Tuesday, March 19, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) Part two (2)

Image Hosted by ImageTitan.com Hadejia A yau! Daga M.MUHAMMAD IDRIS.. A cigaba da kawo muku Takaicaccen tarihin wadanda suka bada Gudunmawa a kasar Hadejia, yau mun tabo Mutum Uku wadanda tarihin Hadejia bazai manta dasu ba!


AIR VICE MARSHAL HAMZA ABDULLAHI(RTD) *************** AVM Hamza Abdullahi. Daya daga manyan hafsoshin soja na kasa, daya daga cikin manyan arewa, tsohon Gwamnan Jihar kano, tsohon ministan Abuja, tsohon ministan aiyuka na musamman. Avm Hamza yayi mulki na wata 18 amma ya yi aiki na mamaki a fadin jihar kano.


Aiyukan da suka shafi masarautar Hadejia sun hada da: ginin hanyar Bulangu da Guri, ginin Asibitin Birniwa, K/Hausa da Bulangu, ginin makarantun mata na kaugama da Birniwa, ginin kwaltocin cikin garin Hadejia da gina fadar Hadejia ta zo daidai da zamani. karin streets light. .


Lokacin yana ministan Abuja ko 'yan kwangila da dama sun samu aiki, manyan mutane da yawa sun samu fulotai, ya samarwa matasa karatu a institute of management ta Abujan.


Avm Hamza bayan ya bar Gwamnati ya ci gaba da bayar da gudunmawa domin ci gaban al'ummarsa ya gina katafaren gida domin saukar bakin kunya, ya gina masallaci na juma'a mahadi ka ture ya kuma tanaji makeken fili a yamma da masallacin domin gina makaranta, yana kawo masu Likitocin ido domin masu larurin ido.


Avm yana daukan yara masu karamin karfi ya kaisu Turkish School in sun gama ya nema musu admission a kasa ko a waje,yanzu haka akwai yara biyu a kasar Turkey wanda shi yake daukan nauyinsu. Tsakanin Avm. da masarautarsa akwai kauna domin ba sallar da za ta zo bai yi ta a Hadejia ba sai in ba ya kasa. Muna masa fatan alheri da karuwar arziki mai amfani.



ALHAJI BELLO IBRAHIM AUYO **************** Marigayi Alhaji Bello Ibrahim Auyo. "Agogo sarkin aiki" tsohon malamin makaranta, gogaggen dan siyasa. Ya fara aiki tun daga malamin makaranta har ya kai mukamin sakataren ilmi.


Ya rike mukamin kwamishinan zabe tun muna jihar kano. Ya yi shugabancin karamar hukumar Hadejia har sau biyu. Shi ne shugaban ALGON na kasa.


Alhaji Bello Ibrahim ya fi kowane shugaban karamar hukuma da aka yi a Hadejia aiyuka na raya gari. Alhaji Bello Ibrahim ne ya gina sakatariyar karamar hukumar Hadejia da ake cikinta, shi ne ya gina Asibitin Kofar Arewa da shagunan bayanta, shi ne ya gina kasuwar jan bulo. Bello ya dauki ma'aikata da malaman makaranta masu yawa a zamaninsa. A zamaninsa matasa masu yawa sun samu muhalli domin ya raba filaye da dama a wurare masu yawa.

Misali shi ya raba filin idi kuma ya sanyawa wurin suna Unguwar Mu'azu Hadejia,


ya bayar a fanisau kuma shi ya sayarwa mutane gidajen fanisau, ya raba a gabari, ya raba a Gandun Sarki.

Bello ya yi ginan magudanan ruwa ba adadi a Hadejia. Yayi aiyuka a Auyo lokacin muna hade da ita.

"Turmin tsakar gida sha gwagwarmaya"
Bello mutum ne mai riko da addini, jam'i ba ya wuce shi, ya rike dangi musamman marayu, da azumi a bakinsa Allah ya karbi ransa. Allah ya sa ya sha ruwa a Aljanna, ya yafe masa kura-kuransa.......



ALHAJI ADAMU KWANO *************** Alhaji Adamu kwano tsohon ma'aikacin lafiya ne wanda ya bayar da gudun mawa matuka a wannan fage. Allah ya yi masa fikira kwarai domin shi ba likita ba ne amma yakan yi aikin da ya gagari likitoci.


Adamu kwano ya shahara akan kaciya domin galibin matasan Hadejia da kewaye daga 'yan shekara 30 zuwa 50 duk yawanci shi ya musu shayi.

Alhaji Adamu kwano attajiri ne mai son ci gaban addini, shi ne ya gina makarantun islamiya ta Hudu da Garko da makarantar sakandire ta Aminu Yusuf.

Adamu kwano shi ne mutum na farko da ya yi kokarin gina Asibiti mai zaman kanta sai dai ba ta fara aiki ba Allah (SWT) ya yi masa rasuwa.

Muna rokon Allah(SWT) ya ji kansa yaarzurta mu da masu hali irin nasa. AMEEN.

Monday, March 18, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) Part One (1)

Image Hosted by ImageTitan.comHadejia A yau! DAGA MUHAMMAD IDRIS HADEJIA


Shirin Taurarinmu zai Rinka tabo takaicaccen Tarihin Mutanen Kasar Hadejia da Irin ci gaban da suka bata, Domin kaima ka bada taka Gudunmawa. Kuma zamu fara da takaicaccan Tarihin.......


ALHAJI HAMZA TURABU *************** Alhaji Hamza Turabu. Bahadeje mazaunin kano. Alhaji Hamza tsohon ma'aikaci ne a Hukumar Aikin Gona ta Jiha. Yana rike da mukamin Director Forestry tun muna kano har muka zo jigawa kuma akansa ya bar aiki.

Dattijo ya yi wa mutane da yawa hanyar samun aiki musamman a Ma'aikatar Aikin Gona kuma shi ne ya assasa filantaishin masu yawa da muke gani a yau fadin kano da jigawa.

Alhaji Hamza mutum ne mai son ya ga matasa sun yi karatu shi ya sa gidansa ya zama mazaunin Dalibai 'yan wannan masarauta har a yau. Hadejawa suna ma addu'a Allah ya albarkanci zuriyarka. Amin.


SHEIKH MUHAMMAD LAMIN KHAN (MALAM MODIBO YALLEMAN) **************** Marigayi Sheikh Muhammad Lamin Khan yana daya daga cikin dattijon 'Yalleman, daya daga cikin malaman addini na wannan masarauta, shine bubban Limamin 'Yalleman.


Malam Modibo ya zaga kasashen Afirka da dama akan neman ilmin addini kuma ya same shi domin ya karantu a bangarori na addini dabam-dabam. Ana zuwa har daga garuruwan makwabta a dauki karatu a wurinsa.


Bayan kasancewar gidansa makaranta ce shi ne ya assasa Makarantar firamare ta Madani da kuma Sakandiren Madani. Matasa da yawa cikin garuruwan 'Yalleman, Dakayyawa, Hadiyin, Ubba, da kewaye a wannan makaranta suke karatu. Malam Modibo ya hada duk wani hali na dattako da ake so,don haka yake da girma a idon jama'a a ciki da wajen wannan masarauta.


Muna addu'a Allah ya sa kur'ani ya cece shi. Amin.


HAJIYA LAMI AMINU KANI *************** Hajiya Lami Aminu Kani 'ya ce a wurin Sarkin Fulanin Hadejia Alhaji Daudu Saleh. kuma matar na hannun daman AVM Hamza Abdullahi, wato Alhaji Aminu Kani. Hajiya Lami tana daya daga cikin tsofin 'yan boko mata na wannan masarauta.


Hajiya Lami babbar ma'aikaciya ce a hukumar bayar da wuta "PHCN" Kuma zamanta a wannan wuri ya amfanar da wannan masarauta matuka domin idan ka kasa masu aiki a PHCN na wannan masarauta kashi dari Hajiya Lami ce ta kai kashi saba'in daga cikinsu PHCN. Mace mai kamar maza.


Hadejawa sun baki Sarkin Fulanin Mata. Muna addu'a Allah ya kara daukaka. Amin.

Saturday, March 16, 2013

SAKO ZUWA GA MASU AMFANI DA FACEBOOK.



Hadejia A yau!Shafukan INTERNET da Wayar Hannu ta GSM....Bincike ya nuna cewa shafin internet na FACEBOOK da wayar hannu ta GSM suna daga cikin ababen dake kara rura wutar fadan addini a Nigeria.

Hakan yana faruwa sakamakon irin yadda mutane ke amfani da su wajen isar da sako atsakaninsu. Mutanen mu suna da son bayar da labari,Inma ingantacce ko mara inganci don neman addu'ar 'yan uwansu ko don nuna bajintar su ko kuma don wata manufa ta su ta daban.

Wannan yasa dayawa sukan fadi abinda basu da tabbas akansa, ko kuma suyi kari cikin labarin na su.

Ya kai dan'uwana mai son bayarda labari! Kaji tsoron Allah, kada kafadi, ko kada karubuta sai abin da kaji ko kagani kokuma kake da tabbas akansa. kasani za ka amsa tamyar Allah akan abinda kake fadi kokuma kake rubutawa a duniya (facebook), wacce amsa ka tanada?

Ba wani abin birgewa bane afara jin labarin dake tayar da hankali agurinka. Addinin muslunci ya hore mu da yin magana ba tare da ILIMI ba. Mu kiyaye ko Allah (S.W.A) ya kiyaye mu.

Ya Allah! Kakiyaye mu, kabamu zaman lafiya, Amin.

Haka kuma a Facebook zakaga GROUP ko PAGE wadanda basu da Aiki sai watsa Labarin karya. Misali sai a saka Hoton Yarinyar da bata jiba bata Gani ba wai Ace tace tana neman Miji. Wanda kuma Addinin Musulunci bai yarda da hakan ba.

Kuma 'yan mata kuji tsoron Allah duk abinda ya sameku kuke Janyowa kanku. Domin kune kuke yawan sauya Hoto dan ku Birge mutane!

A garin hakan kuma sai a samu wasu bata gari suyi downloading din hoton su dinga Talla daku.

Ko kuma Namiji ya Bude 2go da sunan mace yasa hoton wadda bata jiba bata gani ba. Wai dan ya yaudari 'yan Iska 'yan'uwansa. Allah ya kiyaye mu.

To Jama'a sai mu kula da fadar jita jita, domin karya haramun ce. Allah ya kare mu amin....

Friday, March 15, 2013

KUDUBAR JUMA'A DAGA BUBBAN MASALLACIN HADEJIA.

HADEJIA A YAU. A yau malam Na'ibi yi mana kudubace mai taken :- JIN TSORO DAGA AZABAR ALLAH S.W.T. Fassara:- Ibrahim Umar. Yan uwana musulmai Malam ya ja hankalinmune game da jin tsoro daga azabar Allah Mai Girma da Daukaka domin kamun ubangiji ya kasance mai tsananine. Yan uwana kullun mu cigaba da kasancewa daga cikin bayin Allah Madaukaki masu da'a tare da jin tsoron azabarsa. Kada mu kasance daga bayi azzalumai masu zalintar kansu wajen keta Abubuwan da musulunci ya hana. Manzon Allah S.A.W yana cewa "kuji tsoran wuta ko da da tsagin dabino ne" Ma'ana koda abin da zakayi sadaka dashi kamar tsagin dabinone don ka bayar dashi ka kare kanka daga wuta to kayi kokari ka bayar. ALLAHUMMA INNA NARJU RAHMATIKA WA NAKHAFU AZABAK. ya Allah SWT ka karemu daga azabar wuta amin.

Monday, March 11, 2013

FACEBOOK A KARKARA!

HADEJIA A YAU!Hadejia A yau! Assalamualaikum! 'Yan uwa barkanmu da yau, da fatan Alkairi. muna gaf da fara wani shiri a wannan shafi na facebook. shirin kuwa zai leka ne loko na kauyukan Arewacin Nigeria, domin jin halin da talakawa suke ciki a kauyuka da karkara. domin wasu kauyukanma ba'a kulasu sai an buga gan-gar siyasa. Sanin kowane Talakawa akar-kara suna cikin mawuyacin hali fiye da na biranen Arewacin Nigeriya. Ada sashin hausa na gidan redion b.b.c. yana gudanar da wannan shiri wanda kuma yin hakan na sanya gwamnati ta gyara kura-kuranta. To amma yanzu shiru muke ji ba labari. Hakan yasanya mu yin azama wajen gabatar da wannan shiri ta hanyar fcbk. kasancewar shugabanni na amfani da shafin na fcbk. Duk da ma dai sunsan halinda ake ciki to amma fadawa duniya zai kara sanyasu su gyara. Kaima kema zaku iya shiga wannan shiri ayi da ku domin yin hakan jihadi ne bubba wanda Allah ne kadai yasan ladan da zaka samu. Domin ka yi sanadiyyar fitar miliyoyin alumma daga cikin Kangin talauci. Duk mai bukatar ayi wannan aiki da shi ya Tuntubi Garba Tela Hadejia ta inbox. Ko ya kira lambarsa ko ya masa sakon Wasika (text). 07065540705. Allah ya bada Iko.

Thursday, March 7, 2013

HUKUNCIN GADO DA MASU CIN GADO. KASHI NA DAYA (1)

HADEJIA A YAU! Assalamu Alaikum! Wannan babi zai yi bayani a kan masu gado a cikin maza, da masu gado a cikin mata. Sannan babin zai yi bayani akan irin bambancin darajojin magada. (1) MASU GADO A CIKIN MAZA Masu gado daga cikin maza, su goma (10) ne! Ga jimlarsu, amma idan aka rarraba su, su goma sha biyar ne, (15) kamar haka:- 1. Da (Na tsatso) 2. Dan da, (Jika har zuwa tattaba kunnansa) 3. Uba (Na ciki) 4. Kaka namiji (Na wajan uba, har zuwa Sama) 5. Dan'uwa shakiki (Na uwa daya, uba daya) 6. Dan'uwa li'abi (Na uba daya, uwa daban) 7. Dan'uwa li'ummi (Na uwa daya, uba daban) 8. Dan dan'uwa shakiki (Na uwa daya, uba daya) 9. Dan dan'uwa li'abi (Na uba daya, uwa Daban) 10. Kanin uba, shakiki (Na uwa daya, uba daya) 11. Kanin uba li'abi (Na uba daya, uwa daban) 12. Dan dan kanin uba, shakiki (Na uwa daya uba daya) 13. Dan dan kanen uba, li'abi (Na uba daya uwa daban) 14. Miji. 15. Ubangijin bawa. Hadejia A yau! MASU GADO A CIKIN MATA Masu gado a cikin mata su bakwai ne (7) Ga jimlarsu, amma idan aka rarraba su, su goma ne, (10) kamar haka:- 1. 'Ya ko Diya (Ta tsatso) 2. 'Yar da, (Na tsatso duk yadda ya yi nisa) 3. Uwa 4. Kaka mace (Ta wajan uba) 5. Kaka mace (Ta wajan uwa) 6. 'Yar'uwa shakikiya (Ta uwa daya, uba daya) 7. 'Yar'uwa, li'abiya (Ta uba daya, uwa daban) 8. 'Yar'uwa, li'ummiya (Ta uwa daya, uba daban) 9. Matar Aure 10. Uwargijiyar bawa ko baiwa. Hadejia A yau! MASU GADO DARAJARSU TANA DA BAMBANCI DA JUNA Masu gado suna da bambanci da junansu. Ma'ana gado ba abu ba ne wanda za a ce a raba shi daidai, a tsakanin magada. Dole ne a raba shi yadda Allah Madaukakin Sarki Ya raba shi cikin hikimarSa. A rabon gado wani ya fi wani rabo. Wani kuma ba ya da rabo in ga wani. Wani kuwa zai tashi daga wani rabo ya koma ga wani rabo, saboda samun wani tare da shi. Wani kuma zai kada wani; wani sauran dukiya yake kwashewa. Saboda haka za mu bi su dalla-dalla, domin mu yi bayaninsu, in sha Allahu. MASU FARALI Za mu fa ra da bayanin abin da ake nufi da masu farali. Masu farali su ne wadanda Allah Madaukakin Sarki Ya ambaci rabonsu a cikin Alkur'ani Mai girma. wadannan su ne kamar haka: 1. 'Ya (Ta tsatso) 2. 'Yar da (Na tsatso) 3. Uwa 4. Uwar uwa 5. Uwar uba 6. Dan'uwa li'ummi (Na uwa daya) 7. 'Yar'uwa li'ummiya, (Ta uwa daya) 8. Miji. 9. Mata. MASU ASIBCI Za mu fara bayani a kan abin da ake nufi da asibi. Asibi shi ne wanda idan a ka zo wajan rabon gado, zai tsaya har a fitar wa masu farali, farilinsu, sannan abin da ya yi saura ya kwashe, za mu jera su kamar haka: 1. Da (Na tsatso) 2. Dan da (Na tsatso) 3. Dan'uwa shakiki, (Uwa daya uba daya) 4. Dan'uwa li'abi, (Na uba daya) 5. Dan dan dan'uwa shakiki (Uwa daya uba daya) 6. Dan dan dan'uwa li'abi, (Na wajan uba) 7. Kanin uba shakiki (Uwa daya uba daya) 8. Kanin uba li'abi, (Uba daya uwa daban) 9. Dan kanin uba shakiki, (Uwa daya uba daya) 10. Dan kanin uba li'abi, (Uba daya uwa daban) 11. Wanda ya 'yanta bawansa. 12. Wadda ta 'yanta bawanta. MASU ASIBCI WANI LOKACI WANI LOKACI SU KARBI FARALI Wadanda ke yin asibci wani lokaci, wani lokaci kuma su amshi farali, su ne kamar haka: 1. 'Yar'uwa shakikiya (Uwa daya uba daya) 2. 'Yar'uwa li'abiya (Uba daya uwa daban-daban) MASU ASIBCI WANI LOKACI WANI LOKACI SU KARBI FARALI WANI LOKACI SU HADA DUK Wadanda ke yin asibci wani lokaci, wani lokaci kuma su amshi farali, wani lokacin kuma duka gaba daya, da asibci da farali. Sune:- 1. Uba. 2. Kaka namiji. MASU GADON NISFI Kafin mu yi bayanin masu gadon nisfi, ya kamata mu san mene ne nisfi? Nisfi kalmace ta Larabci. Ma'anarta rabi (1/2). Idan an raba wani abu biyu, kowane daya daga cikinsu ya zama nisifi ke nan. Masu gadon nisfi (Rabi), su biyar ne kamar haka: 1. Miji. 2. 'Ya (Ta tsatso) 3. 'Yar da (Na tsatso) 4. 'Yar'uwa (Ta uwa daya, uba daya) 5. 'Yar'uwa (Ta uba daya, uwa daban) Wadannan su ne masu nisifi. Za mu bisu daya bayan daya; mu yi bayanin su dalla- dalla, ta hanyar da za a fahimta, in sha Allahu, domin ko wanensu yana da sharuda. Alhamdulillahi.

Tuesday, March 5, 2013

WA YA KAMATA YA TSAYA A BAYAN LIMAN?

Hadejia A yau! Assalamu Alaikum! Godiya ta tabbata Ga Allah wanda ya Halicci Mutum da Aljannu dan mu bauta masa.

Tsira da Aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu, wanda Allah ya Aikoshi da Alqur'ani da Salloli guda Biyar (5).

Bayan haka Al-ummar Musulmi Musulunci yana da tsare tsare wanda Idan ka bisu zaka rabauta! Hakika Tsayuwa a bayan Liman a yayinda ake sallah ba na kowa bane na Masana ne! Domin Idan Liman yayi kuskure a sallah sune suka san Irin abinda zasu fada masa dan ya gyara.

Idan wanda baida Ilmi ya tsaya bayan Liman kuma aka samu akasi Liman yayi Kuskure kana tunanin zai iya gyara masa? Bazai iya ba, saidai ya sake batawa.

Manzo (s.a.w.) yana cewa :- An sanya muku Liman dan kuyi koyi dashi, Idan yayi Ruku'i kuyi Ruku'i, Idan yayi Sujudi kuyi sujudi.

Danme zakayi abinda Liman baiyi ba?

ZAN BAKU LABARIN MUJRIMI... Mujrimi wani Balaraben Kauye ne! Yazo Birni kuma Sallah ta Magriba ta kamashi sai yazo yayi Alwala ya tsaya a bayan Liman. Sai akayi Sa'a Liman ya karanto Ayar nan da take cewa:-

Alam Nukhliqil Awwalyn? (Fassara) shin bakuga yadda muka Halakarda Mutanen farko ba? Sai Balaraben kauye ya fice daga sahun farko ya koma sahu na biyu.

Sai Liman ya sake karanta Summa Nutbi'uhumul-Akhiriyn. (fassara) sannan haka muka aikata ga mutanen baya. Sai Balaraben kauye ya koma sahun Karshe.

Sai Liman ya kara karanta Kazalika Naf'alu bil- Mujrimiyn. (fassara) sannan haka Muka aikata ga Mujrimai.

Sai Balaraben kauye ya fita a guje yace Ni ake Nema. Domin yaji an ambaci kamar sunansa. To dan Allah me ya janyo haka? Allah yasa mu Gane.

Monday, February 18, 2013

KASAR HADEJIA DA KEWAYENTA.

Hadejia A yau Muna farawa da sunan Allah Mai kyauta
Magamiya a Duniya, ya baiwa musulmai da
kafirai baki daya! Mai jin kai Kebe Gobe
kiyama. Ni'imarsa ga wanda yayi Imani take
Ranar Alkiyoma. Tsira da Aminci su Tabbata
Ga shugabanmu Annabi Muhammadu (s.a.w.)
wanda Allah ya aikoshi da shiriya ga
Mummunai.

Kasar Hadejia kasa ce wadda Allah Ya
Albarkaceta da Ni'imomi daban daban kamar
Kasar Noman Rani da Damina, Kiywo, da
sauran Albarkatun cikin Ruwa da na Kan
Tudu. Kuma kasar ta kafu tun a Karni na 17
wasu kuma sunce Karni na 15. Daga Gabas
tayi Iyaka da Daular Kanem Borno daga
yamma tayi Iyaka da Masarautar Kano. Haka
kuma daga Kudu tayi Iyaka Da Wuddiri wato
kasar Katagum. Sannan daga Arewa tayi Iyaka
da Masarautar Gumel da Daular Damagaram.

Kuma Hadejia tana daya daga cikin Hausa
Bakwai dukda cewa Fulani ne Suke Mulkinta.
Hadejia A yau.
Abinda nakeso na fada shine... Cikin Hikimar
Ubangiji da Ikonsa ya bamu Manyan mutane
Masu Kaunar Ci gaban Wannan yanki.


Wadansu 'yan Kasuwa ne wasu kuma
Ma'aikatan Gwamnati, wasu kuma 'yan Siyasa.
Kullum kokarinsu da Tunaninsu shine yaya
zasu samawa Kasar Hadejia Mafita? Yaya zasu
kawowa yankinsu ci Gaba? Yaya zasu rage
zaman banza ga Matasa? Yaya zasu Hada kan
Al'ummar Kasar Hadejia su kalli Alkibla Guda?

Allah ya saka musu da Alkairi.
Saboda haka ne wasu daga Cikinsu suka fara
Gina Masana'antu da kamfanoni domin
samarwa da Matasa aikin yi. Zamu fara da
Kamfanin shinkafa wanda ana nan Ana aiki
ba dare ba Rana. Sannan kamfanin Suga
wanda shima ana kan Aikinsa.
Haka nan Masana'antu Gasunan wasu ana
aikinsu wasu kuma tuni suna aiki kamar
Sambajo Gen. Enterprises da sauransu.
Sannan Idan kazo titin Maje Road zakaga
wasu Gine gine masu Hawa biyu (2) suma
anayinsu don kyautata Rayuwar Al'ummarmu.

Muna Addu'ah Ga 'yan kasuwarmu da
Ma'aikatan Gwamnatinmu da 'yan siyasarmu
Allah ya saka musu da Alkairi. Allah ya karfafi
zuciyarsu. Amin.

(1) A.V.M. Hamza Abdullahi
(2) Alh. Salisu Sambajo
(3) Alh. Hashim Ubali Yusuf
(4) Alh. Lawal A.A.
(5) Alh. Muhd. Daguro Adamu
(6) Comrade Umar Danjani
(7) Danmasanin Hadejia Alh. Dr. Muhd. Lawwal
(8) Magayakin Hadejia Alh. Muhd. Umar
(9) Professor Haruna Wakili
(10) Alh. Sarki Kafinta Mallam Madori.
Hadejia A yau.

Thursday, February 7, 2013

SANA'AR WASAN KURA DA BIRI

Easily Upload Your Images To Myspace
As.HADEJIA A YAU!
Sana'ar wasa da kura wata sana'a ce wadda ta samo asali tun lokacin Maguzawa, har ta kawo ga wannan karni da muke ciki. Inda zakaga mai wasa da kurar ya sanya mata camfu a bakinta kuma yana rike da ita da sasari.

Yakanyi ta mata kirari yana zungurarta ita kuma kurar tana kugi duk don a birge masu kallo. Sannan masu wannan sana'a suna tafiya da abu biyu, wato bayan wasa da kurar suna saida magani musamman wanda ya shafi yara.
Zakaga ana kaiwa yara ana dorasu a kan kurar wai don karsuyi tsoro. Wasu kuma ana dorasu ne domin maganin fitsarin kwance.

To kowane mai wasa da kura zai fada maka dadin sana'ar da kuma wahalarta, to ko menene wahalarta? Wani mai wannan sana'ar ya tabbatar min cewa wahalarta tana da yawa musamman ma wajen yanda zaka samo kurar tun tana karama, kayi kiwonta har ta girma. To ko menene Hatsarinta? Yace hatsarinta yana da yawa Amma Allah bai taba hadasu da hatsarin ba.

Sannan shima wasa da Biri yanzu zakaga masu wasa da kurar sune sukeyi, Kuma ya kara min da cewa suna hada wasan kura da na biri ne domin kawata masu kallo.
Allah ya kyauta.

Tuesday, February 5, 2013

ME YA HADA ALMAJIRCI DA BARA?

Image Hosted by ImageTitan.com
Hadejia A yau. Ko da kaga wadannan yara kasan su waye? Wadannan su ake cewa Almajirai, ko menene Ma'anar Kalmar Almajiri? Kokuma waye Almajiri?

Almajiri ana nufin Dalibi mai neman karatun Alqur'ani kokuma Ilmin Addinin Musulunci. Domin ya zama malami mai karantarwa! Malamai sune ake yiwa take da :- Masu tsantsanin Duniya saboda kiyamah,
Masu zuyyina Adon Qur'ani.


ALMAJIRI- Idan akace almajiri a kasar Hausa ana nufin mai Neman Ilmin addini.Wadanda idan sukaji Labarin malami a duk Inda yake zasu tashi suje domin neman Ilmi.
Haka kuma Iyaye suma sukan kai 'ya'yansu domin su samu Haddar Alqur'ani ko makamancin hakan.

To a yanzu labarin ya sanja domin Iyaye suna kaiwa 'ya'yansu Almajirci ne don bazasu iya ci dasu ba, zakaga yaro baifi shekara biyar ba (5) an kawoshi wai Almajirci. Anya yaron nan ba gamuwa yayi da ragon Uba ba? Babu ruwansu da'ya'yansu sai damina ta fadi zasu debosusu tayasu Noma.

Zakaga Almajiri ya sato karfunan bakanikai ya kaiwa Makera su saya, Almajiri ya sato gwangwanaye ya kai Jaribola, Almajiri yanzu har kasuwar tsaye! Sun gamu da ragagen Iyaye su dama baburinsu karatu ba, sudai suga babu waninauyi a gabansu.


Allah ya kyauta. Dukda wasu zasuce Ai da sokoto ma kiskadi ce Amma babu wanda ya baka tarihin In sun tashi daga karatu bara suke zuwa. Muma Nan Mai-rakumi ai kiskadi ce da sauran garuruwa.

Amma bamuji cewa suna zuwa bara ba.

Tuesday, January 15, 2013

TARIHIN RAYUWAR SIR. AHMADU BELLO (SARDAUNA) 15/01/2013.

Easily Upload Your Images To Myspace
An haifi Alhaji Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto, a ranar 12 ga watan yuni na 1910 a garin Rabbar na jihar Sokoto dake Arewacin Najeriya. Kakansa shi ne sarkin Musulmi Bello, wadda yana daya daga cikin wadanda suka kafa daular Sokoto, kuma dane ga marigayi Mujaddadi Shehu Usman Dan Fodiyo.


Ahmadu Bello ya fara makaranta a garin Sokoto, sannan ya wuce zuwa makarantar horas da malamai ta Katsina. Kafin daga bisani Sultan ya nada shi malami a makarantar Middle School ta Sokoto.

A shekarar 1938 aka nada shi Sardaunan Sokoto bayan da ya gaza a yunkurin da yayi na zamowa Sultan, wato Sarkin Musulmi. Ya kuma halarci kasar Ingila domin yin karantu kan harkokin mulki a shekarar 1948.

Ya kuma fara shiga harkokin siyasa gadan-gadan bayan dawowarsa daga karatu, inda har aka zabe shi ya zamo mamba a majalisar dokoki ta Arewacin Najeriya. Ya kuma zama ministan ayyuka da raya kasa.

Sir Ahmadu Bello ya kasance Firimiyan farko na yankin Arewa daga shekarar 1954 zuwa 1966. Sannan ya jagoranci jam'iyyar NPC ta lashe kujeru da dama a zaben da aka gudanar bayan samun 'yancin kai..

Bayan kammala zabe, ya zabi ya ci gaba da kasancewa Firimiya, inda ya nada Abubakar Tafawa Balewa ya zamo Fira Minista. Ya taka rawa sosai wajen hada kan yankin Arewacin kasar wanda keda kabilu mabiya addini daban-daban, da kuma aiwatar da ayyuka na ci gaban kasa.


An kashe Ahmadu Bello a ranar 15 ga watan Janairun shekara ta 1966, bayan wani juyin mulki da wasu sojoji 'yan kabilar Ibo suka jagoranta.

Thursday, December 27, 2012

SAKON GODIYA DAGA MAI MARTABA SARKIN HADEJIA.

HADEJIA A YAU! Assalamu alaikum! Bayan gaisuwa irin ta Addinin musulunci tare da fatan Alkairi. Ina meka godiya da ban gajiya zuwa ga Mai girma Gwamnan Jihar Jigawa da Sanatoti da 'yan -Majalissu da Sarakunan Jihar Jigawa da sauran sarakunan Jihohi makwabta, Game da taya murna da akayi ta cika shekaru Goma a Kan Gadon Sarautar Hadejia! Kuma muna meka sakon godiya ga Jami'an tsaro da Mutanen Gari da Al'ummar Masarautar Hadejia sakamakon Hadin kai da suka bada aka gabatarda taro Lafiya. Allah ya saka da Alkairi. Hadejia A yau.
Kuma Muna meka sakon Godiya da ban gajiya ga Hakimai da Dagattai da Masu Unguwanni na wannan Masarauta mai Albarka. Allah ya saka da alkairi.

Muna kara godiya ga 'yan kwamitin wannan taro wadanda suka bada gudunmawa aka Gudanarda wannan taro Lafiya.

Kuma muna kara Addu'ah Allah ya kawo ci Gaba mai Amfani a Masarautar Hadejia! Allah ya tsaremu daga Masifu da fitintinu a kasarmu baki daya. Ameen. Hadejia A yau!

Tuesday, December 18, 2012

THE ESTABLISHMENT OF FULANI JIHAD DYNASTY IN HADEJIA (Page one)

HADEJIA A YAU!
In 1808, Sarkin Fulani Umaru, his son and successor Muhammadu Kankiya died. Muhammadu Sambo was appointed as the new Sarkin Fulani of Hadejia. The Fulani leader's In Rinde decide to send a delegation to Sokoto to inform the Shehu of the developments in Hadejia region. Shehu Usman Danfodiyo accept the appointment of Muhammad Sambo as the New Leader of The fulani in Hadejia, condole the people over the death of Umaru and Muhammadu Kankiya, and formally installed Sambo as their new Sarkin Fulani Hadejia. After his formal installation, Muhammadu Sambo decided in 1810 to shift his base from Rinde to Hadejia but before he carried out his plan Habe Ruler of Hadejia Abubakar got the security report of Sambo's intention. Hadejia A yau.

Conscious of the Fulani's military success in the area, Abubakar decided to withdraw from the town without resistence.
Therefore, on the date Sambo decided to occupy Hadejia, on reaching the town, he found the town deserted and so occupied it without any resistance. From that time onwards, Hadejia became the base of the Fulani and eventually the capital of the emirate. An important development that followed the shifting of the Fulani base was the Installation of Sambo as the first Fulani Jihadist Emir of Hadejia in 1810. Thus, Sambo established the first Jihadist dynasty in Hadejia from which sprang all subsquent emirs of Hadejia to date.http://bit.ly/K2WOg4

He also unified all the territories formerly under the Habe administration, under a single central administration to the Emirate of Hadejia. Hadejia A yau!

At the time Sambo moved the Jihadists base from Rinde to Hadejia and formally established the emirate, the structure of the emirate's administration was by far modest andd until mid-century, the capital appeared to have been lesss developed.

At the time of the establishment of the emirate, Muhammadu Sambo relied on a much less formally structured organization and therefore surrounded himself with a relatively small entourage of co-favourite most of whom lacked either titles or fiefs. Therefore, Sambo had to face the difficult task of establishing the apparatus of Centralized administration in his domain. As a firs step towards the establishment of an emirate government, he appointed Yusuf his younger brother as Sarkin Auyo, and his eldest son Muhammadu Garko as Chiroman Hadejia and Makama Lele as the Galadima.
Each of the new title holders was given a specific function to perform in the administration. For example Chiroma, was the crown prince while Galadima was the prime Minister. Sambo's other appointments were those of Madaki (war commander), Ma'aji (Treasurer), Sarkin yari (chief prison supretendant), and Sarkin Wanzamai (chief Barbear). All these state officials were chieftaincy status and performed a specific assignment in the administration. Hadejia A yau!

By Musa Usman Mustapha.

Sunday, December 16, 2012

SABON GWAMNAN KADUNA DA TARIHIN RAYUWAR SA.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music A yau Lahdi Za'a rantsar da Alh. Mukhtar Ramadan yero a matsayin Gwamnan Jihar Kaduna! An haifi Muktar Ramalan Yero a ranar 1 ga Mayun shekarar 1968 a birnin Zazzau. Ya halarci makarantar Firamare ta karamar hukumar wadda ke Unguwar Kaura daga shekarun 1974 zuwa 1980. Ya shiga ta Sakandire dake Ikara daga shekarun 1980 zuwa 1985, sannan ya wuce Cibiyar Koyon Mulki wadda ke karkashin Jami’ar Ahmadu Bello ta Zaria, inda ya samu takardar shaidar digiri na farko da na biyu, wato Masters, a fannin Akanta daga 1986 zuwa 1991. Ya wuce Kwalejin Koyon Aikin Akanta ta Jos. Muktar ya yi aikin NYSC a jihar Ogun, a hukumar saye-sayen Kayayyaki masu muhimmanci a shekarar 1991. Da ya karasa, sai ya fara aiki sashen Kudi na Jami’ar Ahmadu Bello, a matsayin mai kula da hada-hadar sashen da bankuna. Bayan shekaru biyu, sai ya koma bankin Universal a matsayin mai kula da asusun masu hudda da bankin daga shekarun 1993 zuwa 1997. A wannan bankin saida ya kai matsayin Babban Akantan bankin. A shekarar 1997 ne ya mayar da aikinsa zuwa Kamfanin Nalado Nigeria Limited, kamfanin Namadi Sambo a matsayin Babban Akanta, daga baya ya zama Shugaban Ma’aikata, Shugaban Sashen Kudade da Shugabancin Ma’aikata. Cikin hukuncin Ubangiji, da Namadi Sambo ya zama gwamnan jihar Kaduna a 2007, sai ya nada shi kwamishinan ma’aikatar kudi, mukamin da ya rika shekaru uku. Shi memba ne na kungiyoyi da dama, daga cikinsu akwai Kungiyar Akantoci ta Kasa da Cibiyar Shugabannin Kamfanoni da ta Akantocin Kididdiga da Riritawa Kudade da ta Masu ilmin fasaha da Injiniyoyi da sauransu. Yana da aure da ‘ya‘ya, kuma mutum ne mai sha’awar karance-karance da hawan dawaki da sauraren kade-kade da kuma yin mu’amala da mutane, shi ya sanya yake da tausayi. Wani abin lura shi ne, Muktar Yero ya baiwa marada kunya, inda ya gudanar da ayyukan Ma’aikatar Kudin jihar Kaduna cikin rikon amanar da aka san shi da shi, a duk wuraren da ya yi ayyuka a baya. Saboda haka ne, aka ba shi mukamin mataimakin gwamna a lokacin da Shugaba Namadi Sambo ya zama Mataimakin Shugaban Kasa a 2010. Bayan Mutuwar Gwamna patrick Yakowa Ranar Asabat 15/12/2012. sakamakon Hatsarin Jirgin sama a yau. Alh. Muktar Yero ya zama Gwamnan Jihar Kaduna. An rantsar dashi ranar Lahdi 16/12/2012. ALLAH YA TAYAKA RIKO.

Friday, December 14, 2012

ALHAJI TIJJANI DODO HADEJIA.

Image Hosted by ImageTitan.com 
Hadejia a yau!
A ci gaba da kawo muku tarihin wadanda suka bada Gudun mawa a Kasar Hadejia, yau Aji kima ya kawo mana Kadan daga Irin Gudunmawar da Alh. Tijjani Dodo yake bayarwa!

Dattijo Alhaji Tijjani Dodo Hadejia Dan Baiwa ne, Wanda ba kowa ya san hakan ba.Wannan mutumin baya kasa a gwiwa ganin al'uma sun ci gaba. Wannan yasa ya wajabtarwa kansa fafatawa a harkokin rayuwa daban-daban domin samarwa al'uma mafita. Duk wurin da ka leka zaka hango shi saboda Jajircewa da gina rayuwar sa da yayi akan Gwagwarmaya. 

1.Dan kasuwa ne,

2.Dan siyasa ne,

3.Ba sarake ne,

4.Dan kungiyar aikin gayya ne,

5.Dan kungiyar Achaba ne,

6.Dan kungiyar matasa ne,

7.Dan kungiyar yan kasuwa ne,

8.Dan kungiyar ma'aikatan gwamnanti ne

9.Dan kungiyar kwallon kasa ne,

10.Dan kwamatin hawan sallah ne,

11.Dan kwamatin gyaran makabirta ne.

12.Dan kwamatin jinga ne,

13.Dan kwatin gayaran masallaci

14.Dan kwamatin gyaran gari.

15.Dan kungiyar raya al'adun Gargajiya.


Yanzu haka shi ne shugaban aikin gayya na Hadejia,
shi ne kuma shugaban yan Achaba, haka kuma dogari ne a fadar Hadejia. Lalle Juyi Goma sai Wake Inji masu Iya magana.

A hannu daya kuma dan siyasa,dan kasuwa, Jama'a ya kamata mu jinjinawa wannan bawan Allah, Allah ya bamu dubu masu amfani irinsa.

Wannan hotonsa ne yana bada hannu. Bai yadda yaga abu bai yi iya bakin kokarinsa ba. Idan na magana ne zaiyi idan da karfinsa ne zaiyi idan da aljihunsa ne sai yayi.

Allah ya saka da alherinsa.

Monday, December 10, 2012

TARIHIN SHEIKH JA'AFAR MAHMOOD ADAM.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music MARIGAYI SHEIKH JA'AFAR MAHMUD ADAM. GIDANSU, HAIFUWARSA DA .TASHINSA. Babban Shehin Malami, Kwararren mai Tafsiri, Gawurtaccen mai Da’awah,Baban Salim Ja’afar dan Mahmoodu dan Adamu, An haifeshi a yankin Daura a jihar Katsina a Shekara ta 1961. Gidansu Malam Ja’afar, Gidane da su ke kulawa da Ilimin Addini da Haddar Alqu’ani, Kakansa ya kasance yana karantar da Littattafan Fiqhu da Yaren Larabci, Wasu cikin ‘Ya’yansa kuma har sun haddace Alqur’ani. Malamin farko da ya fara dorawa Malam Ja’afar karatun Alqur’ani, Wani Malami ne mazaunin gari Daura mai suna Malam Magaji, yana masa matsayin Babban Yaya ne, domin sun hada dangantaka da shi a Kakanninsu, Shine farkon wanda ya fara koya masa Bakaken Larabci, Wannan Malami, Mahaddacin Alqur’ani ne tun a wancan Lokaci. Baban Salim ya fara koyon karatun Alqur’ani ne a hannun Mijin Babbar Yayarsa mai suna Malam Haruna, wanda shima yana masa matsayin Dan’uwa ne, Daga hannun wannan Malamin ne aka maida Malam Ja’afar hannun wani Malamin kuma Dan’uwansa a kauyen Kuza mai suna Baba Rabe, Wannan Malamin shine ya kaurato tare da Baban Salim zuwa garin Kano a shekarar 1971 ko 1972, Sun sauka a gidan wani Gawurtaccen Mahaddacin Alqur’ani dan kasar Nijer ne mai suna Malam Abdullahi dan Zarmu a unguwar Fage a cikin birnin Kano. Baba Rabe yayi fatar ganin Malam Ja’afar ya haddace Alqur'ani tun yana raye, Amma Allah bai so hakan ya faru a Idanunsa ba, Wannan Malamin ya rasu a shekarar 1977 ne, Shi kuma Malam Ja’afar ya haddace Alqur’ani ne a shekarar 1978 DAGA KARATUN ALLO ZUWA JAMI’A Baban Salim ya haddace Littafin Allah mai girma bai wuce da shekara sha Bakwai ba. Ya fara karatun Alqur’ani gadan-gadan ne a hannun Malam Abdullahi Mutumin Nijar, Malami ne da aka san shi da tsanantawa Almajiransa da matsa musu kan inganta haddar Alqur’ani, Ina ganin wannan matsawar ta shafi har Baban Salim, Domin sakamakonta shine wannan ingantacciyar haddar Alqur’ani da Allah ya baiwa Baban Salim, wacce ba kasafai a ke samun Mahaddata Alqu’ani da irinta ba, In ban da ‘yan kadan cikin Tsarakunsa. Malam bai haddace Alqur’ani a hanun Malam Rabe dan Zarmu ba kamar yadda Malamin yayi fata, Dalili kuwa shine Malam Ja’afar da Tsarakunsa a wancan lokaci, wasan kwallon kafa da zuwa kallonta ya dauke musu hankali kan tsayuwar daka kan haddar Alqur’ani, Wannan ya sa, Malam Rabe ya daukeshi daga hanun Malam Dan Zarma ya maida shi garin Hadejiya ya damka shi a hannun wani Malami dan asalin gari Daura amma Mazaunin Hadejiya mai suna Malam Safiyanu,wanda shima Dan’uwa ne ga Malam Ja’afar domin sun hada dangi da shi ta Kakanninsu. Malam Rabe yayi masa haka ne don ya raba shi da kayaniyar Birni da kuma damuwa da Lamarin kwallon Kafa, Maiyiwuwa hakan zai sa shi ya maida hankali kan haddar Alqur’ani, Lalle kuwa hakan ya faru, domin Baban Salin a can ya kamala haddar Alqur’ani bayan rasuwar Malam Rabe. Bayan fara baiyyanar Kungiyoyin Musulunci a Nigeria, Musamman ma Kungiyar Izala, Sai jayayya ta yi yawa tsakanin Mutane kan wassu Mas’aloli kamar ; Hukuncin Salatul Fatih, matsayin Darikun Sufaye, Hukuncin Durkuso a gaisuwa, Sadakar Fida’u bayan Mutuwa, Taron Suna da wassu Al’adun kasar Hausa, Wannan ya tilasta Malam Ja’afar neman Ilimin Littattafai. Malam Ja’afar ya shigar da kansa Makarantu Biyu lokaci guda. Ta farko a wata cibiya ta kasar Masar da ke garin Kano, Ta Biyu kuma wasu Azuzuwa ne da aka bude don yaki da Jahilci. Malam Ja’afar bai shiga Makarantar Firamare ba saboda a wannan lokaci sun yiwa wannan matakin karatun girma. Ya yi karatu a wadannan Makarantu na tsawon shekara Uku a jere daga 1980 zuwa 1983.

Tuesday, November 27, 2012

MANYAN 'YAN SIYASAR HADEJIA

Hadejia A yau. Wadannan mutane sune Ruhin siyasar Hadejia! Gudunmawar da suka bayar a siyasa da ci gaban yankin Hadejia sai dai Allah ya saka musu da Alkairi. Sunyi siyasa a lokacinda ba'a san Daga kai sai 'ya'yanka ba! Domin sun kafa mutane da dama a Hadejia da kewaye. Duk unguwa zakaga akwai mutanenda suka kafa a siyasa. Lalle sun cancanci yabo. Idan muka fara da Marigayi Alh. Bello Auyo zamuga cewa Ayyukanda yayi a Hadejia har yanzu babu wani ko wata gwamnati da tayi makamancin nasa. Kama da Secretaria, Maternity, da sauran abubuwanda har yau ana amfana dasu a Hadejia. Allah ya kyauta kwanciya. Mallam Ibrahim Kwatalo shima ya gina mutane daban daban a Tarihin siyasar Kasar Hadejia. Duk Wanda yanzu yake Cikin Gwamnati, in ba yaronsa ba sai wanda shine ya kafashi. Allah ya kyauta kwanciya. Alh. Shehu Mujaddadi (Alkali) shehu Illa shehu, shima kamar M. Ibrahim Kwatalo, ya gina mutanenda suka gina Mutane a Tarihin siyasar Hadejia. Kuma Har yau Taswirar siyasarsa ce take Tasiri a Hadejia. Allah ya kyauta Kwanciya. Alh. Muhammadu Danjani Hadejia tarihin siyasar Hadejia bazai manta da kai ba! Shi ya fara Dan majalissar Wakilai a Jamhuriya ta biyu. Kuma jigo ne a jam'iyyar NEPU. Wadanda sukayi yaki da mulkin Danniya da kama karya. Shaho birkita kaji na Garba, Bauna wanda ya dosheta babu maduhu sai wani ba tasa ba. Allah ya kyauta kwanciya. Ahmed Garba (M.K.) ko an kika irinka akeso. Har yau Taswirar siyasar Hadejia tana Hannunsa. Duk unguwarda kaje a Hadejia to akwai mutanen da a kafa kuma suka kafu. Ya samawa matasa aikin yi bansan Adadi ba! Amma nasan babu wanda yayi kamarsa kawo yanzu. Zabgai yabin Bauchi da kare dangi Maza sai kui Hankali, Mai tulu kaji tsoron fad da mai sanda ko yana a kwance! Kainuwa dashen Allah yaya zakuyi? Ruwa sai ya kare Kainuwa ta kare ba dai kaga bayanta ba. An karawa kogi Ruwa mai jinga kayi jingarka zai karya Inda yakeso yabi. Masu fura da zuma sun kula da gwangi, idan gwangin zakusha to, Allah ya bamu zuma ku ya baku Gwangin baya tana son gaba. Hadejia A yau.

Thursday, November 15, 2012

TAKAITACCEN TARIHIN SHETTIMAN HADEJIA DA M. BILYAMINU USMAN.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Musichttp://www.MyspaceImageCodes.net">Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau! Assalamu alaikum! Barkanmu da shigowa sabuwar shekarar Musulunci. A daidai lokacinda muke kokarin Bankwana da shekarar 2012, Allah cikin Ikonsa wannan shekara tazo mana da wani bubban Rashi wanda bazamu manta dashi ba! Wannan rashin kuwa shine na Alh. Bilyaminu Usman da Alh. Hassan Hadejia (shettiman Hadejia). A ranar Asabat 20/october/2012 Allah yayiwa M. Bilyaminu Usman Rasuwa yana da shekaru 83. Kafin rasuwarsa ya rike mukamai da dama musamman a hukumar Ilmi. M. Bilyaminu ya fara koyarwa a Middle school wato Abdulkadir a shekarar 1948, kuma yayi sakataren Ilmi a Hadejia kuma a shekarar 1976 yayi kwamishinan Ilmi a tsohuwar jihar Kano a lokacin Gwamna Sani Bello. Kuma M. Bilyaminu yayi ministan Ilmi a Jamhuriya ta biyu Lokacin shehu shagari. Kuma ya rike Mukamin Chairman primary Education Board a shekarar 1999. Allah ya kyauta kwanciya. Kuma ya bar mana abin koyi a sha'anin zaman rayuwa, wato Gaskiya da rikon Amana. Ko wadanne Irin darasi muka koya daga Rayuwarsa? Hadejia a yau. http://www.facebook.com/Ismailaasabo Haka kuma Ranar laraba 7/November/2012 Allah yayiwa Shettiman Hadejia Rasuwa Alh. Hassan Abbas, sakamakon 'yar gajeriyar jinya, Shettiman Hadejia tarihin Hadejia bazai manta da irin Gudunmawar da ya bayar ba ta hanyar ci Gaban garin Hadejia da Taimakon Addini, masu iya magana suna cewa ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Wannan Haka yake Kasar kago bata Maida Kago. Shettiman Hadejia ya rike mukamin Minista a lokacin Jamhuriya ta daya, bayan nan ya rike mukamin Ministan Man fetur a zamanin Ibrahim Babangida, kuma shine shugaban Kaduna polo club, sannan shine Chairman Board of Directors a kamfanin Leadway Assurance! Sannan Board member A Masallacin sultan Bello dake Kaduna. Allah ya kyauta kwanciya! A cikin abubuwanda ya bari wadanda zamuyi koyi dasu akwai kyautatawa al'umma da taimakawa Addinin musulunci da zumunci. Hadejia a yau. Muna rokon Allah ya bamu Albarkar wadannan mutane, Allah ya maida mana makamantansu, Allah ka kara mana Gaskiya da Rikon Amana da taimakon Al'umma. HADEJIA A YAU.

Monday, November 5, 2012

SULE LAMIDO SAI GODIYA.

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU! Alhamdulillahi Godiya ta tabbata ga Allah wanda yake bada Mulki ga wanda yaso, kuma a lokacinda yaso, Tsira da Aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu wanda Allah ya aikoshi da shiriya da rarrabewa tsakanin Karya da Gaskiya!

Bayan haka muna kara Godiya ga Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Dr. Sule Lamido, wanda Allah ya bashi Mulkin Jigawa domin ya Gudanar dashi bisa Gaskiya da Adalci. Alhamdulillahi Jigawa a yau.

Ranar Litinin 5/11/2012. Mai Girma shugaban kasa ya kawo mana ziyara Hadejia a karkashin mulkin Gwamna Sule Lamido, Inda kuma akayi hawan Daba kasaitacciya. Hakika wannan abin Alfahari ne a garemu Hadejiawa kuma babu abinda zamucewa Mai Girma gwamna sai godiya.

Bayanda shugaban kasa yazo Hadejia ya ziyarci fadar Mai martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje, bayan yaga Hawan Daba da aka shirya masa ya gana Da Mai martaba Sarki. Kuma ya nemi Alfarma guda Uku wadda zata kara Inganta wannan yanki na Hadejia. Na farko ya nemi Alfarmar Gwamnati da ta ci gaba da aikin B.E.C. Wanda a halin yanzu ya dakata, na Biyu ya nemi Alfarmar da ayi mana Maganin Ambaliyar Ruwa da ta Addabi wasu sassa na Hadejia.

Na uku ya nemi Alfarmar a Sake Inganta Jingar Kogi wadda ake samun Asarar Dukiyoyi da amfanin Gona.

Muna kara Godiya ga Wannan Gwamnati wadda A zamaninta ne Jigawa ta tabbata Jigawa. Hakika duk wanda yasan Jigawa shekara Bakwai baya Idan yazo zai tabbatarda Jigawa ta samu Uba. Jigawa abar Alfaharinmu, Sule Lamido Abin Alfaharin Jihar Jigawa.

Hakika abubuwanda mukeji a baya kunnenmu ne yaji Idonmu bai gani ba. Dan haka ka bada saida akan abinda Idonka ya gani yafi akan abinda kunnenka yaji. Muna kara jinjina ga Mai Girma Gwamna Wanda ya daga Darajar wannan Jiha tamu. Jigawa ada take Jaririya amma a yanzu Uwace a zamanin Sule Lamido.

Ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Jigawa ta tattara Manyan Mutane masu hazaka! kama daga Gwamnan zuwa comishinoni da sauransu. Jigawa tarin Allah Lamido Ikon Allah.

Allah ya huci gajiya, Allah ya maida kowa Gidansa Lafiya. Ameen. Hadejia a yau.

Sunday, November 4, 2012

WAKAR TARIHIN YAKIN HADEJIA DAGA LIMAN MUHAMMADU (Fassara daga Alh. Ibrahim katala).

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau. 1, Allahu sarki shi kadai yake wahidun, sammai da kassai jalla bashi da kishiya. 2, Shi ba fari shi ba baki ba ubangiji ba ja ba ba alkashi bashi ga rawaya. 3, Ba sake sake ba ba kamar yarani ba shudi da kore jalla bashi da mai kama. 4, Zatinsa baya tattara bai rarraba da kawai da motsi bayayi ko sau daya. 5, Sarkinda ba na biyunsa ba na uku nasa ka dadan basira zanyi waken shahidu. 6, Ranar talata munga tashin duniya Rannan Muhammadu yai shahada zahira. 7, Shi yai jawabi ya fada shi bai gudu kuma bashi mai kamu a darul duniya. 8, Raggo ake kora a bishi a cim masa amma sadauki bai gudu sai faduwa. 9, Sarki Muhammadu yai jawabi ya cika shi bashi mai kamu a jashi ya tunkiya. 10, Dan melle sarkin yaki shima ya fada in dai da rai sarkinmu baya kamuwa. 11, Ma'ajin Hadejia saleh shima ya fada mun dau shahada zahira bahakikiya. 12, Manya da yara duk shirin yaki suke kowa yana wanka yana yin alwalah. 13, Kowa yana yin sallama a gida nasa sunsa gabansu a lahira ba dawaya. 14, Jama'ar Hadejiawa fa duk sun hallara kowa yana cewa fa mun zama shahidai. 15, Sarki Muhammadu mai shahadar zahiri ba badili ko dai cikin tawaga tasa. 16, Shi bai kamar tsoro ba baya razana kan ya ije ma babu sauran hanzari. 17, Ajali idan yayi babu kwana duniya kai dai zamo kullum shiri duka safiya. 18, Shi bai kamar tsoro a baya razana baya gudu dan Garba sarkin jarumai. 19, Mutuwa tafarki wanda kowa zayabi ai kulli nafsin dukka rai zai dandana. 20, Aka daura sirdi nai ya hau bisa ya tsaya yace mu dau himmar shahada zahira. 21, Sarki Muhammadu baya tsoro ko kadan Allah ma'aiki su take tsoro kadai. 22, Hauninsa linzamin mayani ya rike damansa tasbihi salatin annabi. 23, Dan mai karatu tudun kasa ba dawaya dan garba jikan sambo sarkin adalai. 24, Duk mai shahada auwalinsa madacima suka barace da fari ya mutu shahidi. 25, Farkon hawa yaki galadima sai haru ranar talata sun ka sauka a barzahu. 26, Alkali sarkin yaki kaura amada sarkin arewa da sunkaje can sun tsaya. 27, Suka jeru sunka tsaya a nan kofar gabas kafin suje har mai ruwa ya taddasu. 28, Kasan igwa dokinmu shi bai santa ba duka dokuna na faduwa ba lissafa. 29, Igwa tana tashi madafa na zuba yau sai ta Allah babu sauran shawara. 30, Jaruman Muhammadu basu tsoro ko kadan sun gwammace mutuwa da dai subi kafiri. 31, kuma sabo jikan tete harbi nai ake anan a kofar fada duk suka tuntsure. 32, Firyan Hadejia shi da bori na salihu kofar gabas suka fadi nan aka cim musu. 33,Dan Dodo Barwa da shi da gwanki baran nufe, sun karbi hartashi a kwaryar kai nasu. 34, Ai babu mai mutuwa gaban ajali nasa kan surfa gero kan daka wasu sun fice. 35, iko idan Allahu yayi nufi nasa ai ba tsimi balle dabara ko daya. 36, Tamkar kamar inuwarka baka guje mata in kai gudun ta bika harma ka tsaya. 37, Hartashi na yawo kamar burduduwa tamkar zubar wake a can a masussuka. 38, Ya ratsa soraye ya ratsa katanguna tamkar kabewa ko kamar tumfafiya. 39, Yasha zarar soro ya keta katanguna da kago da zaure sun zube ba tambata. 40, Tsarnu da kurna har kasa durumi dada ya kar dabinai cediya da itatuwa. 41, Rannan Hadejia munga tashin hankali Allah da manzo su kadai ne magani. 42, Abdulwahabu baka tana hannu nasa artashi ya samar ya tsinke tsirkiya. Edited by (Idris M. Eddy) DA SAURAN BAITI SAI A SAURAREMU A GABA.

Tuesday, October 30, 2012

TAKAICACCEN TARIHIN LIMAMIN HADEJIA M. YUSUF IMAM.

Hadejia A yau.
Hadejia A yau. HADEJIA A YAU!Hadejia A yau. A ci gaba da kawo muku Tarihin wadanda suka bada Gudunmawa a Hadejia, yau Zamu baku takaitaccen Tarihin Bubban Limamin Hadejia MALLAM YUSUF ABDURRAHMAN. Muna farawa da sunan Allah wanda da ikonsane komai ya kasance da kuma Abinda zaya kasance! Tsira da Aminci su tabbata ga Manzon Allah (s.a.w.) wanda ka aiko dashi bil’haqqi da Gaskiya.

An haifi Limamin Hadejia M. Yusuf Imam a unguwar Rumfa da ke cikin Garin Hadejia, a shekarar 10/1/1980, kuma ya fara karatun Addini a Gurin Mahaifinsa M.Abdurrahman Ya’u, bayan ya kai shekaru bakwai (7) shi da ‘yan uwansa an kaisu Makarantar Allo a unguwar Yayari, wato makarantar Mallam Muhammadu Dan birni. Bayan yakai shekaru Ashirin (20) ya koma Makarantar Malam Garba Dake ‘Yankoli, kuma anan ne ya sauke Alqur’ani mai tsarki.

A shekarar 1998 Malam Yusuf ya samu nasarar shiga Makarantar koyon karatun Addini ta Hadejia (S.A.I.S.) inda kuma anan ne ya sake sauke Alqur’ani a Ruwayar Hafsi. Tare da Na’ibinsa M. Habibu Aminu.

A shekarar 2002 Malam Yusuf ya samu nasarar shiga Makarantar Horar da Malamai dake Gumel (ATC.GUMEL) Inda ya samu saidar N.C.E. A bangaren Arabic. Kuma ya samu aikin koyarwa a ma’aikatar Ilmi dake Auyo, bayan shekaru ya dawo yaci gaba da koyarwa a Makarantar S.A.I.S. Dake garin Hadejia.

Malam Yusuf yayi karatun Ilmin Addini a gurin Malamai da dama kamar M. Usman danyaro, Malam Tela Majema, M. Akilu, M. Aminu Ibrahim Daurawa da sauran Malamai.

A ranar Asabat 5/1/2002 Malam Yusuf Imam ya fara bada Ilmi a soron Gidansu, Inda ya fara da Dalibai kamar haka:-

Mohd. Abubakar Malam namu, Ismaila A sabo, Baffale Muhd. Furdi (Baffaliya), Idris Baffa (Liyan), Yusuf abdulkadir wakili, da Adamu A Amar.

Ranar 12/feb./2006 an gayyaceshi da ya gabatar da Maudhu’i a masallacin Juma’a, Inda kuma yayi fadakarwa akan Alamomin tashin Alqiyamah. Wanda kuma wannan fadakarwa ta jawo hankalin mutane akan ranar tsayuwa,wato Alqiyamah.

A ranar Talata 29/Aug./2006 Malam Yusuf ya fara jan Sallah a masallacin juma’a. Sakamakon Rashin lafiyar Limamin wancan lokacin Malam Shehu Qassim.

Haka kuma ranar juma’a, 8/ september/2006 Malam Yusuf ya fara fassara Huduba a Masallacin Juma’a Kuma a wannan lokacine aka tabbatar dashi Na’ibi na biyu.

Ranar Litinin 2/june/2008 Allah yayiwa Limamin Hadejia rasuwa Malam shehu Qassim, kuma bayan mutuwarsa ne Ranar Litinin 23/june/2006 aka tabbatarwa Malam Yusuf Imam ya zama Bubban Limamin Hadejia. Da misalin karfe tara (9:m) na dare.

A Ranar Juma’a 27/June/2008 Mai martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu A. Maje ya nada Malam yusuf a Matsayin Bubban Limamin Hadejia. Da misalin karfe (10:am) na safe. Sannan a ranar ya fara sallar Juma’a Inda kuma yayi Huduba mai daidaita hankali da kuma tabbatar da Ikon Allah shine abinda za’abi a zauna lafiya.

A Gudunmawar da Mallam Yusuf Imam ya bayar a cikin Garin Hadejia ta bangaren Ilmi, Harda karatuka da littatafai da ya karantar A masallacin Juma’a. Kamar:- 1,UMDATUL-AHKAM 2, MUWADDA MALIK 3, LU’U-LU’U WAL MARJAN, IHYA-USSUNNAH Da sauran Littatafai. Da kuma Lecture da yayi a Gurare da dama a cikin garin Hadejia da kewaye.

A watan August na wannan shekara Malam Yusuf ya tafi kasar Sudan Domin Karo Ilmi. Muna Addu’a ga Malam Allah ya haskaka zuciyarsa ya kyautata jinsa da Ganinsa ya kara masa Ilmi da Basira. Ameen.

Allahumma badi’ussamawati wal’ardhi, zaljalali wal’Ikrami, wal-izzatullati la tarami, As’aluka ya Allahu, ya rahman bi jalalika, wa nuru wajhika, antalzim qalbi hifzu kitabuka, kama allamtani, warzuqni antilawahu alannahwullazi yardhika anni. Ameen. Hadejia A yau. HADEJIA A YAU!

Monday, October 29, 2012

HAWAN ZIYARA..


HADEJIA A YAU!
Kamar yadda aka sani Æ™asar Hadejia tana gabatar da Hawa guda uku a kowace shekara, wato Sallar Azumi, Sallar Layya da kuma Maulidi. Sannan kuma a kowace Sallah ana gabgaba da hawa guda biyu...  Hawan sallah da Hawan Bariki, Sannan  rana ta uuku yara suyi Hawan daushe da La'asar.

Kamar yadda Tarihi dai ya nuna Sarkin Hadejia Mallam Abdulkadir shine ya kirkiro Hawan Bariki, a wata fira da mukayi da Galadiman Jauje ya tabbatar mana cewa Sarki Abdulkadir mutum ne Mai son nishadi,  hakan yasa a zamanin sa aka kirkiri Hawan Bariki. Sarki yaka je washegarin sallah da hakimansa da Dagatai su kaiwa D.O. Ziyara.

Ranar Laraba 20/April/2005 Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu AbuAbuba Maje ya kirkiro Hawan Ziyara kokuma Hawan Mai Bubban Daki, wannan hawa an fara yinsa ne a sallar Mauludi, wadda kuma za'a rinka yinsa ko wace sallah da yamma. Wato za'a hau washe garin Hawan Bariki.

Ranar Juma'a 22/April/2005, Mai martaba ya hau da yamma. Inda yabi ta tudun mabudi Har zuwa Tudun Barde ya shiga yayi ziyara ga Mai bubban Daki, Bayan ya fito sai yabi ta makera ta Dubantu ta Ganuwar kofar yamma, sannan sai yabi ta bakin kasuwa ta Makwallah ta kofar Jarma sannan In yazo kofar Fada sai ya Tsaya Hakimai kuma su Fara zuwa daya bayan daya suna Jafi. Bayan sun Gama sai ya shiga Gida ya sauka. Hadejia A yau.
Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music
HADEJIA A YAU!
Kamar yanda aka sani kasar Hadejia tana Hawan sallah da Hawan Bariki a kowace sallah. Sannan kuma yara suyi Hawan daushe da La'asar.

Kamar yanda Tarihi ya nuna Sarkin Hadejia Abdulkadir shine ya kirkiro Hawan Bariki, a wata fira da mukayi da Galadiman Jauje ya tabbatar min cewa Sarki Abdulkadir mutum ne Mai son Hawa. Kuma shine ya kara hawa ake yin Hawan Bariki, zaije da hakimansa da Dagatai su kaiwa ( Resident) da D.O. Ziyara.
Ranar Laraba 20/April/2005 Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Maje ya kirkiro Hawan Mai Bubban Daki, A sallar Mauludi, wanda kuma za'a rinka yinsa ko wace sallah da yamma. Wato za'a hau washe garin Hawan Bariki.
Ranar Juma'a 22/April/2005, Mai martaba ya hau da yamma. Inda yabi ta tudun mabudi Har zuwa Tudun Barde ya shiga yayi ziyara ga Mai bubban Daki, Bayan ya fito sai yabi ta makera ta Dubantu ta Ganuwar kofar yamma, sannan sai yabi ta bakin kasuwa ta Makwallah ta kofar Jarma sannan In yazo kofar Fada sai ya Tsaya Hakimai kuma su Fara zuwa daya bayan daya suna Jafi. Bayan sun Gama sai ya shiga Gida ya sauka. Hadejia A yau.

Friday, October 26, 2012

BARKA DA SALLAH. (Layya)

Free Web Proxy HADEJIA A YAU! HAWA LAYYA
Yin layya sunnah ce mai karfi da ta kasance
wajibi ga dukkan musulmi. Maza da mata
kowacce shekara. Ta kan fadi a kan mutum in
ba shi da sarari. To ko maras sarari da ya
sauka a wannan shekara ko bai taba hawa
ba . Ya shiga cikin daya daga raguna 2 da
Annabi(s) ya yanka. Ya ce daya nasa ne daya
na masu karamin karfi cikin al'ummarsa har
zuwa tashin kiyama.
Ya tabbata daga ma'abuta ilmi cewa in kana
da riguna 2 ka sayar guda ka yi layya. Annabi
(s) ya ce duk wanda ya ke da dama kuma ya
ki yin layya to kada ya kuskura ya zo wuraren
sallar Idin mu. Annabi(s) ya ce za a ba mai
layya lada kan kowanne gashi guda na adadin
gashin da ke jikin dabbar da ya yanka.

Monday, October 22, 2012

KWANAKIN HAJJI DA GURARE GOMA MASU ALBARKA. DAGA (M. AMINU DAURAWA)

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music HADEJIA A YAU!

Na daya ranar takwas ga watan hajji, sunanta yaumuttarwiyya,
shine alhazai suke zuwa mina su wuni su kwana,
Na biyu ranar tara ga wata itace ranar arfa, itace alhazai suke wuni a
filin arfa zuwa faduwar rana, daganan su tafi Muzdalifa su kwana
Na uku ranar goma ga wata, itace alhazai suke gabatar da aiyuka
guda biyar a cikinta, jifa, yanka, aski, dawafi, saayi,
Na hudu ranar sha daya , da sha biyu, da sha uku, sune ranakun
kwanan mina da jifa, Abubuwa goma masu daraja a Macca
wadanda suke da alaka da aikin hajji, wadanda ake aiwatar da aikin
hajji, daura da su sune, na daya, Ka'aba ana kewaya ta sau bakwai,
na biyu, alhiji (wanda ake cewa hijri isma'ila) ana shiga ciki ayi
salla,daidai yake da yin sallah a cikin Ka'abah, na uku, makamu
ibrahim, wanda ake sallah Raka'a biyu a bayansa bayan gama
dawafi, na hudu, Alhajrul'aswad, (dutsen aljannah) ana sunbatarsa
(kiss) a shefeshi, ayi sujjada akansa, ko anunashi daga nesa ayi
kabbara, na biyar ruwan zamzam, ana sha a shafa a fuska, a zuba
ajiki, ayi addu'a, aroki Allah bukarar duniya da lahira hadisi ya
tabbata, akan haka, na shida Dutsen safa da marwa, wanda ake
zirga-zirga tsakanin su sau bakwai a fara daga sama a kare a marwa,
na takwas, mina wajen kwana da ranakun jifa, na tara arfa da
muzdalifa, a wuni a arfa a kwana a muzdalifa, na goma wajen jifa
guda uku, inda ake jefa tsakuwa guda saba'in, Allah ta'ala yace
wanda ya girmama alamomin addinin Allah, yana daga cikin tsoran
Allah na zuci, wanda duk yayi sallah a masallacin macca yana da
lada dubu dari, wanda ladan ya shafi dukkan fadin iyakokin harami,
tun daga ka'abah, Manzon Allah saw yace :Duk wanda yayi hajji,
baiyi kwarkwasaba (maganar batsa da mata) baiyi fasikanciba, zai
dawo kamar ranarda mahaifiyarsa ta haifeshi, kuma yace, Hajji
kubutacce(shine wanda akayishi akan sunnah da iklasi da ilmi) bashi
da sakamako sai aljannah, ku tayamu da addu'a mu sami wannan
garabasar, Allah ya karbi ibadarmu yasa mu dace da sunnah da
iklasi na gode

Saturday, October 20, 2012

HADEJIA TO DATE!

Hadejia A yau! Hadejia, town and traditional emirate,
eastern Jigawa state, northern Nigeria. It lies
on the northern bank of the Hadejia River (a
seasonal tributary of the Komadugu Yobe,
which flows into Lake Chad). The emirate’s
savanna area originally included Hadejia and
six other small Hausa kingdoms that paid
tribute to the kingdom of Bornu.



About 1805, Umaru, a Fulani leader who held the
title sarkin Fulanin Hadejia,
pledged allegiance to the Fulani jihad (holy
war) leader, Usman dan Fodio.


Umaru's brother and successor, Emir Sambo
(reign 1808–45), officially founded the Hadejia
emirate in 1808, moved his headquarters to
Hadejia town, established a market, and
began to consolidate Fulani rule over the
small neighbouring Hausa kingdoms.


Emir Buhari (reigned
1848–50, 1851–63) renounced Hadejia’s
allegiance to the Fulani sultanate centred at
Sokoto in 1851, raided the nearby emirates
of Kano, Katagum, Gumel, Bedde, and
Jama’are, and enlarged his own emirate.

Hadejia was brought back into the Fulani
empire after Buhari’s death, but wars with
neighbouring Gumel continued until 1872.

In 1906 the British installed an emir, Haruna, (Maikaramba)
and incorporated the emirate into Kano
province.
The emirate became part of newly
created Jigawa state in 1991.


The town is now a market centre handling
cotton, millet, sorghum, fish, and the rice
grown in the river valley. It serves as an
important collecting point for peanuts
(groundnuts), an export crop. Cattle, goats,
guinea fowl, sheep, and donkeys are kept by
the local Hausa and Fulani peoples.
Several
small lime industries exist in scattered parts
of the area. Hadejia town is located on the
secondary highway between Gumel and
Nguru, which links it to the main highway at
Kano and to the railway at Kano and Nguru.
Pop. (2006) local government area, 105,628.

Saturday, October 6, 2012

THE 19TH CENTURY JIHAD AND ESTABLISHMENT OF HADEJIA EMIRATE (PAGE 2)

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU!
The new ideas generated as a result of their policies had brought together people of diverse (descent) linguistic and occupational groups under one
umbrella. Although ever since their migration into Hausa land, some fulani Jihadists in due course became confidants and advisers to some Hausa rulers, there was a strong and persistent tendency among the Jihadists of avoiding close association with HABE SARAKUNA, either because of
the fear or being contaminated with Illigally acquired wealth or because most of the Habe palaces remained a stronghold of various traditional cultssuch as BORI Cult.




This made the devoted Ulamas keep their distance from the rulers (sarakuna). It was the relationship between these two classes the Ulamas and the Habe rulers that
eventually led to the outbreak of the Jihad in Hausa land at the beginning of the 19th Century.
The condition of Hausa society at the eve of Jihad was anything but fair, especially the socio-economic system.




Virtually all the rulers were norminal Muslims and therefore hardly enforced the Sharia system. At the same time enforced excessive taxation. Yet in the midst of the suffering and hardship, the rulers continued to be corrupt, unjust and indifferent to the plight of the oppressed.




There seem to be some confusion as regards the exact time when the fulani Jihadists first came and established their wet-season camps in the plentiful grazing land of the Auyo/Hadejia riverrine savannah land, the confusion is due to the multiple causes of Nomadic Fulani movements in the
Nigerian Savannah in general and the Hadejia area in particular. H.M. Brice Smith, has placed the coming of the Fulani into the Hadejia area at themiddle or late 1700 A.D.




But according to A. Abdu Maigari, the Fulani came to Hadejia area from Machina in Borno during the 15th Century.
An early Fulani settler in Hadejia who became very influential in one Hardo Abdure dan Jamdoyji, wealthy Fulani who traced his Origin to Machina in Borno. Hardo Abdure established his dry season camp in Hadejia at Jarmari during the early 18th Century.
Jarmari is located few kilometres from Hadejia town. As the case will all Nomadic Fulani camps the one established by Hardo Abdure at Jarmari was not meant to be permanent abode.





Rather it was ment to serve the
purpose of their seasonal movements.
HADEJIA A YAU!

Thursday, October 4, 2012

THE 19TH CENTURY JIHAD AND THE ESTABLISHMENT OF THE HADEJIA EMIRATE. (page 2)


HADEJIA A YAU!
The new ideas generated as a result of their policies had brought together people of diverse (descent) linguistic and occupational groups under one umbrella. Although ever since their migration into Hausa land, some fulani Jihadists in due course became confidants and advisers to some Hausa rulers, there was a strong and persistent tendency among the Jihadists of avoiding close association with HABE SARAKUNA, either because of the fear or being contaminated with Illigally acquired wealth or because most of the Habe palaces remained a stronghold of various traditional cults such as BORI Cult. This made the devoted Ulamas keep their distance from the rulers (sarakuna). It was the relationship between these two classes the Ulamas and the Habe rulers that eventually led to the outbreak of the Jihad in Hausa land at the beginning of the 19th Century.


The condition of Hausa society at the eve of Jihad was anything but fair, especially the socio-economic system. Virtually all the rulers were norminal Muslims and therefore hardly enforced the Sharia system. At the same time enforced excessive taxation. Yet in the midst of the suffering and hardship, the rulers continued to be corrupt, unjust and indifferent to the plight of the oppressed.

There seem to be some confusion as regards the exact time when the fulani Jihadists first came and established their wet-season camps in the plentiful grazing land of the Auyo/Hadejia riverrine savannah land, the confusion is due to the multiple causes of Nomadic Fulani movements in the Nigerian Savannah in general and the Hadejia area in particular. H.M. Brice Smith, has placed the coming of the Fulani into the Hadejia area at the middle or late 1700 A.D. But according to A. Abdu Maigari, the Fulani came to Hadejia area from Machina in Borno during the 15th Century.

An early Fulani settler in Hadejia who became very influential in one Hardo Abdure dan Jamdoyji, wealthy Fulani who traced his Origin to Machina in Borno. Hardo Abdure established his dry season camp in Hadejia at Jarmari during the early 18th Century.

Jarmari is located few kilometres from Hadejia town. As the case will all Nomadic Fulani camps the one established by Hardo Abdure at Jarmari was not meant to be permanent abode. Rather it was ment to serve the purpose of their seasonal movements.

Monday, October 1, 2012

MOVEMENT FOR CREATION OF HADEJIA STATE SINCE 1975.

HADEJIA A YAU! The struggle for the creation of
Hadejia State traces its history back
to 1975 when the community
forwarded its request to the then
military head of state, the late
General Murtala Ramat Muhammad.
Since then, the community has
never failed in exploiting every
opportunity offered by the government for
the creation of more states.
According to findings, the request for the
creation of Hadejia State received a boost
between 1982 and 1983 when the then
National Assembly endorsed the request for
the referendum, but due to a change of
government, the long-awaited dream could
not be actualised.
Also in 1991, a similar request was put
before the then Military Head of State,
General Ibrahim Badamasi Babangida. In
1994 another request was submitted to the
then National Constitutional Conference
under late General Sani Abacha.
Pyramid Trust learnt that when the National
Constitutional Conference submitted its
report to the Provisional Ruling Council (PRC)
, the proposed Hadejia State was among the
seven states recommended for early
creation by the PRC.
The community, our correspondent learnt,
made a fresh request for the creation of
Hadejia state in 1996 through the Local
Government and Boundary Adjustment
Committee, a committee set up by the
federal government to re-examine the
recommendations of the National
Constitutional Conference on creation of
states and local governments as well as
border adjustments.
However, following the PRC’s
recommendation that suggested the
creation of one state in each of the six geo-
political zones, Hadejia community lost their
bid to the present Zamfara State being the
only state created from the North-West zone
then.
In October, 2009, the request for the
creation of Hadejia State was also
forwarded to the National Assembly for
endorsement and onward conveyance to
the executive arm of government for the
final approval. Furthermore, in 2009, a
memorandum requesting the creation of
Hadejia State was also presented to the
NASS. The community also requested the
creation of 11 additional local governments
that included Bualngu, Biram, Diginsa,
Dakaiyawa and Fadama local governments.
Others are Sarawa, Jarkasa, Kadira, Ruba,
Jabo and Ayama local government areas.
This makes the number of local
governments for the proposed Hadejia State
to 19, as initially, the Hadejia Emirate
comprises of only eight local government
that include Auyo, Birniwa, Guri, Hadejia,
Kafin-Hausa, Kaugama, Kirikasamma and
Mallam-Madori.
Findings indicated that the proposed
Hadejia State has a land mass of not less
than 7000sq km with a population of
1,245,571 according to the statistics of the
2006 National Population Census. The
population might have increased by now
given the average national growth rate of
2.83% per annum.
Under the provincial system of
administration, Pyramid Trust gathered,
Hadejia Emirate was the second largest
emirate in the then Kano province in terms
of size, economy, population and other
socio-economic indices. The area was also
blessed with enough human and natural
resources that include water and fertile soil
suitable for all kinds of agricultural activities.
However, just last Wednesday, the July 28,
2010, Hadejia community under the auspice
of Movement for the Creation of Hadejia
State again put another request before the
National Assembly for the creation of
Hadejia State.
The delegation was led to the NASS from
Jigawa State by the Speaker, Jigawa State
House of Assembly, Alhaji Adamu Ahmad
Sarawa.
In a separate presentation, the Speaker
informed the leaders of the NASS that, “From
the information available to us, each of the
requests previously put before the
concerned authorities made progress
towards realisation of our proposed state,
but only to be scuttled apparently due to the
undemocratic nature of the situation.”
Alhaji Adamu further recalled that the
proposed Hadejia State and its people were
the most unfairly treated in the history of
state creation exercise of the military
nationwide. He added that although
pessimistic Nigerians have the belief that
due to the cumbersome provision of the
constitution, new states could not be
created under a democratic setting, the
people of Hadejia do not share this
pessimism.
“We believe the National Assembly can break
that jinx and create more states during the
lifetime of the present administration. And
we hope that Hadejia State would be one of
the new states to b

Saturday, September 29, 2012

GAMON KAFUR

HADEJIA A YAU!
Bayanda Sarkin Hadejia Buhari da jarumansa suka kare Yakin Takoko inda kuma anan ne Allah yayiwa sarkin Hadejia Ahmadu Rasuwa Inda wani Jarumin Buhari mai suna Barde Risku ya kasheshi. Dukda Umarnin da Buhari ya bayar cewa kar a kasheshi, Buhari da jarumansa sai suka shigo Hadejia wato ya zama shine Sarkin Hadejia. Sarkin Hadejia Buhari ya Rubuta wasika Zuwa ga Sarkin Musulmi, ya masa Ta'aziyyar Sarkin Hadejia Ahmadu, kuma ya nuna cewa yanzu shine Sarkin Hadejia yana neman sarkin Musulmi ya amince dashi. Kuma hakan bata samu ba.


Sarkin Musulmi Alu Bubba
sai ya gayyaci duk sarakunan dake
Karkashin Daular sokoto da su hadu su
yaki Buhari. Ko a kamashi da rai ko a
kashe shi. Wannan kuwa ta faru ne a
shekarar (1853). An hada wannan
rundunar yakin ne karkashin Jagorancin
Galadiman Kano Abdullahi maje Karofi
kafin ya zama Sarkin Kano. An gayyaci
mayaka a Garuruwa daban daban kamar
Kano,zamfara,Bauchi,Katagum,Misau,zaria
da sauran garuruwan Daular Sokoto.


Masana tarihi sunce an tara mutum A kalla
Dubu Ashirin (20,000) Abdullahi Maje
Karofi ya Umarci Sarkin Miga da ya zame
musu Jagoran Tafiya, ganin cewa ya fisu
sanin Kasar Hadejia saboda Iyakarsu daya.
Koda suka shirya sai aka Umarcesu da su
shiga Hadejia ta Kudu Maso Yamma, wato
kar su shiga kai tsaye ta yamma. Akan
Hanyarsu ta zuwa Hadejia ne Sai suka
Yada Zango a Kafur, kusa da Hadejia.
Domin su kwana da safe su shiga Hadejia
su Yaki Sarki Buhari. Sai dai da zuwansu
Kafur Buhari ya samu Labari, Ance wani
makiyayi ne yana kiwo ya Gansu, kuma
Har ya bar gurin baiga Iyakarsu ba. Sai ya
rugo ya sanarda Sarki Buhari Abinda ya
gani. Sai Buhari ya Umarci Mayakansa
cewa "Tunda ance Basu da iyaka kuma ga
Magariba ta shigo, mu shirya muje mu
shiga cikinsu ba tare da sun ganemu ba"
hakan sukayi yace Duk Lokacinda sukaji
Dan fatima ya Buga Ganga to su fara
Bugun mayaka.

Haka akayi Mayakan
Buhari suka shimmace su suka shiga
cikinsu ba tare da sun gane ba,Saboda
Garuruwa da dama ne suka Hadu. Ance
wasu mayakan nasu Dauresu akayi wai
dan kar su shiga Hadejia kafin Gari ya
waye. Ashe Ajali ne ya dauresu.
Koda Sarkin Hadejia Buhari yayi shirinsa
yayi Addu'ah sai ya Daga Kai sama.
Sai Dan-fatima ya zuba Kirari:-

(Fasa maza dan
Sambo, Garba Bakin Tandu da Man Madaci,
wanda ake jira yazo, fasa Maza gagara
gasa, sai ya buga Gangar yaki).

Anan
Mayakan Hadejia suka fara bugun
mayakan Daular Sokoto suna kashewa.
Wadansu duk suka razana suka fita a guje
kowa yana kokarin ya ceci Ransa.
Wadanda aka dauresu dan kar su shiga
Hadejia da wuri, duk anan aka kashesu.
Sauran kuwa suka zubar Makamansu suka
Gudu. Dawakai suka Razana, su kuwa
mayakan Hadejia Suna bi suna kashewa
suna kama Bayi.