"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, November 5, 2013

TARIHIN MARIGAYI HARUNA UJI DA WAKOKINSA. MUHD. AJI HADEJIA...

Comrade Aji Kima Hadejia!
Free Web Proxy
HADEJIA A YAU!
Muna gayyatar yan uwa da Abokan Arziki zuwa wajen kaddamar da littafin da na
rubuta wanda na kira
"Tarihin Alh Haruna Uji da Wakokinsa"

Za'ayi Taron kamar haka:

Rana=Asabat 9th November 2013 Guri=Dakin Taro na sakandire fantai Hadejia Jigawa state Lokaci=10am

Baban Bako na musamman;

mai girma gwamnan jihar jigawa Alhaji Dr sule Lamido con.

Uban Taro;

Mai Martaba sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar Maje Con.

Shugabannin Taro;

1.Alhaji Suleman Baffa
2.Alh Muhammadu Daguro

Masu Masaukin baki:

1.Mai girma shugaban karamar hukumar Hadejia Alh Abba Haruna
2.mai girma dan majalissar jiha mai wakiltar Hadejia Alh Aminu Abus
3.Mai girma mai bawa gwamna shawara akan harkokin dalibai Alh Umaru Danjani.

Bako mai jawabi;

Mai girma kwamishinan Ilimi na jihar Jigawa Farfesa Haruna Wakili.

Mai bitar Littafi;

Shugaban kwalejin Ilimi ta jihar Jigawa Dr. Dahiru Abdulkadir.

Babban mai kaddamarwa;

Pharm.Hashim Ubale Yusufu

Mataimakan masu kaddamarwa

1.Mai Girma shugaban jam'iyar PDP ta jihar Jigawa Alh Salisu Mamuda.
2.Mai Girma kakakin majalissar dokokin jihar jigawa Alh Adamu Ahmed
sarawa.
3.Mai Girma mataimakin kakakin majalissar dokoki Abdu Alh Dauda Karkarna.
4.Masu Girma Ciyamomin Hadejia da Auyo da k/Hausa da Kaugama da m/madori da Guri da birniwa daKirikasamma.
5.Masu Girma yan majalissar Hadejia, Auyo. K/hausa, Kaugama, M/madori da Guri da Birniwa da Kirikasamma
6.Mai Girma kwamishinan matasa da raya al'adun gargajiya Alh Babandi Muhammad.
7.Alhaji Salisu Sambajo MFR

Masu Rera Waka;

1.Alh Aminu Ladan Ala
2.Fati Niger
3.Saddiq zazzabi
4.Surajo mai Asharalle
5.Dan Kwamarado

Masu Gabatar da Taro

1.Alh Baffa Bura FNICPR
2.Alh Umar Kiyari Jitau Madamuwa
3.Salmanu Adamu Rishi.

Allah ya bada ikon Zuwa.

Tuesday, October 22, 2013

KA SAN KANKA DA KANKA! (TAMBAYOYI 50) DAGA HARUNA AMINU HARUNA.

Hadejia A yau!

Muna cikin wani zamani, da mutane, sunfi damuwa da bayani akan wasu fiye da kansu, sunfi binciko laifin wasu fiye da nasu


Sayyadina Umar yace kuyi wa kanku hisabi kafin ayi muku, Abubawanda suke jawo tsira, Bautawa Allah shi kadai da Iklasi, akan sunnar Manzon Allah, a cikin Akida, da Ibada, Da mu'amalah, da Halaye masu kyau, yiwa kanka tambaya, hamsin don kasan matsayinka :


Allah yasa mu dace :

1- waye ya yika ?

2- mai yasa ya yika ?

3- kai waye ?

4- A ina kake ?

5- mai kake yi ?

6- Ina zaka ?

7- mai zai faru ?

8- mai kafi so a rayuwarka ?

9- mai kafi ki rayuwarka?

10- Duk abinda kakeyi, kana da hujja a sharia?

11- su waye abokanka?

12- Yaya zamanka da iyayanka?

13- Yaya zamanka yake da iyalanka?

14- Wace kungiya kakeyi don me?

15- A kwai wani yanzu haka da bakwa shiri da shi?

16- Tsakaninka da Allah ka taba cin amanar wani?

17 Kanayin karya?

18- Kana Dun guma ashariya?

19- Yaya zamanaka da makotanka?

20- Wace shedar ilmi kake dauke da ita?

21- kana salloli a Jam'i musamman a masallaci?

22- yaya alakar ka da danginka take ?

23- shin kana sada zumunta?

24- shin kana bayar da sadaka ?

25- shin kana karanta Alkur'ani mai girma?

26- kana azumin litinin da Alhamis?

27- kana sallar Shafi'i da wuturi?

28- kana zuwa asibiti domin ziyarar marasa lafiya?

29- Kana yawan saba alkawari ?

30shin kana azumtar kwanaki masu haske, ranar
sha uku, sha hudu, sha biyar?

31- shin kana kiyamul- laili?

32-kana umarni da kyakyawa da hani da mummuna?

33- kana zuwa aiki akan kari kuma ka tashi akan lokaci?

34- kana zuwa gaban malami domin daukar karatu?

35-ka tabbatar abinda kake ci halal ne?

36- kana kuwa damuwa da halin da yan uwanka musulmi suke ciki?

37- kana taimaka marayu kuwa?

38- salati nawa kake yiwa Annabi saw kullum?

39- Istigfari nawa kakeyi kullum?

40- kana zuwa makabarta domin tuna lahira?

41- kana zuwa taaziyya da sallar Jana'iza?

42- ka taba yin kuka saboda tsoran Allah?

43- shin kana yiwa dukkan musulmi sallama ko
kuwa sai wanda ka sani?


44- kanayin rantsuwa akan karya kuwa?

45- kana shan taba ko wiwi ko giya ko hodar iblis?

46- kana jin kade- kade, da wake- wake?

47- kana aske gemunka?

48- ka taba karbar cin hanci?

49- kana kyautawa iyalanka?

50- kana gaba da wani kuwa?

Allah yasa mu dace.

Wednesday, September 18, 2013

CIWON KODA A KASAR HADEJIA! DAGA PHARM. HASHIM UBALE YUSUF.

Hadejia A yau! Daga pharmacy Hashim Ubale Yusufu


Bismillahir Rahmanir Rahim. Assalamu Alaikum.

CIWON KODA A KASAR HADEJIA: A bisa kididdiga, kimanin mutane miliyan talatin (30million) ne ke dauke da cutar Koda a tarayyar Nigeria. (National Association of Nephrology). Yawancin wadannan mutane na mutuwa kuwa katsam daga cutukan da suka shafi makwarar jini da zuciya, wanda ke da danganta da ciwon kodar. Wannan ya nuna cewa kimanin mutane ashirin bisa dari (20%) na ‘yan Nigeria na fama da wannan ciwo, wanda ana ganin alama daga yawan karuwar masu neman tace jini (dialysis). A wasu asibitocin zaka iske kimanin mutane 200 zuwa 300 ke zuwa neman tace jininsu a rana.



Cututtuka da dama na iya jawo ciwon Koda. Manyan dalilan dake hassada wannan ciwo anan karkarar sun hada da ciwo tsutsa (infections), kishirwa da kuma shaye shayen magunguna kai tsaye, Hawan Jini, shan taba da makamantansu.
Ita koda tana taimakawa jikine wajen tace dattin da kan taru a jikin mutum, sannan kuma tana taimakawa wajen tsotse ruwa, da sukari da sauran sinadaran gina jiki dake yawo a jini domin kar su bi fitsari su fice. Kenan zamu iya gani cewa idan har Koda bazata iya yin wannan tatar ba, to kuwa akwai matsala. Babban abun dazai faru kuwa shine, dattin na iya tare kofofin da jini da fitsari zasu bi, daga nan sai a fara kumbura, da kuma samun zazzafan ciwo na fitar hankali a hanyar da fitsari yake bi.




Sau tari zaka tarar mutane na aikin dake sa su zubad da gumi mai yawa, amma babu ruwa a kusa dasu. A kauyuka da rugage, zaka samu rijiyoyi sun kafe, ko kuma zasu sha ruwa gurbatacce, saboda ba inda zasu samu ruwan mai kyau su sha. Wannan bala’i ne.
Sannan kuma, yanzu wani abu wanda yake kamar gasa shine shaye shayen magunguna babu dalili ko kuma babu neman shawarar masana.




Wannan ka iyasa shan gurbatattun magunguna ko na jabu wadanda zasu iya cutar da ita kodar ta daina aiki. Haka kuma shaye shayen maganin gargajiya na daya daga cikin abubuwan da ke jawon wannan ciwo.
Akwai gazawar kayan aiki a asibitocinmu na tace jini da musayar koda, wanda hakan na jawo matsalar kai marasa lafiyar kasashen waje don warkarwa. A inda kuwa babu halin haka, sai addua kenan.

Tuesday, September 17, 2013

MARIGAYI SARKIN DOGARAI DA SAURAN MARIGAYA...

ALLAHU AKBAR! A Satinda ya Gabata ne Masarautar Hadejia tayi Rashi Bubba wanda Tarihi bazai Manta da wannan Rashi ba.


A cikin wadanda suka rasa rayukansu a sanadiyyar Hatsarin Mota a Hanyar Kano, Mutum goma sha daya ne! A wannan hoto kuma akwai Sarkin Dogarai da Galadiman Dogarai da Madakin Dogarai da Wamban Dogarai da Makaman Dogarai da Magayakin Dogarai da Garkuwan Dogarai da Chiroman Lema da Shitu Dogari da
Manu Mai Hoto.



Ya Allah Muna Rokonka da sunayenka tsarkaka Allah ka Gafarta musu. Amin.
Hadejia A yau!

SARKIN DOGARAN HADEJIA
Free Web Proxy
WAMBAN DOGARAI.Free Web Proxy
Galadiman Dogarai Free Web ProxyMadakin DogaraiFree Web ProxyFree Web Proxy Free Web ProxyImage Hosted by ImageTitan.com[URL="http://img4.imagetitan.com/img4/small/8/8_s.dogarai.jpg" border=0 alt="Image Hosted by ImageTitan.com">Image Hosted by ImageTitan.com KOLI DIREBA
Free Web Proxy SHITU DOGARI
Free Web Proxy

Sunday, September 8, 2013

****TAURARINMU HADEJIAWA PART SIX(6)****

Free Web Proxy
Hadejia A yau.. Daga Muhammad Idris.
A ci gaba da kawo muku Tarihin wadanda Suka baiwa Kasar Hadejia Gudunmawa, yau Mun Tabo kadan daga Tarihin Marigayi Shatiman Hadejia Alh. Hassan Abbas.
****SHATIMAN HADEJIA ALHAJI HASAN ABBAS*****

Marigayi Shatiman Hadejia yana daya daga cikin dattijan arewa,manya a jihar kano da jigawa.Ya fara aiki tun daga Native Authority(NA) daga nan ya koma tarayya.Ya rike mukamin karamin ministan fetur a zamanin IBB. Shatiman Hadejia mutum ne mai kishin kasa da rikon addini. Shi ne sanadin aikin mutane da yawa a kaduna kuma har ya rasu akwai mutane da dama a zaune a gidansa.


Shatima ne ya fara gina katafaren gida domin saukar bakin kunya a Hadejia. Shi ya dauki dawainiyar
gyaran masallacin juma'a na lokaci mai tsawo.


Ya dauki nauyin sayen likkafani ga mamata har tsawon rayuwarsa. Arzik insa ya amfani 'yan uwa da sauran jama'a matuka domin akwai wadanda ya dauki nauyin ba su albashi har ya koma ga Allah subhanahu wa ta'ala.Muna addu'a Allah subhanahu wa ta'ala ya ji kansa ya albarkanci zuriyarsa.
Daga Muhammad Idris.

Wednesday, August 28, 2013

DANGANTAKA TSAKANIN BIRNI DA KAUYUKAN KASAR HADEJIA. DAGA M. HUSAINI SHEHU..

Hadejia A yau!
Daga M. Hussaini Shehu


DANGANTAKAR BIRNI DA KAUYE

Dangantaka tsakanin birni da kauye a kasarmu ta Hadejia tanada tsohon tarishi. Yana da wuyar gaske kasami bahadeje ko bahadejiya dake birni ko kauye da bashi da gidan yan’uwa ko gonar gado a daya daga wadannan wurare dana ambata.DA

Bukukuwan sallah-: shekarun baya zakaga kowane gida cike da baki yan’uwanmu na kauye sunzo cikin Hadejia domin sada zumunci da juna da kuma kallon buku kuwan sallah.

Wannan al’ada tamu tataimaka wa kasarmu sosai wajen jaddada hadinkai a tsakaninmu , kuma tataimaka wajen kawarda kyama tsakanin junanmu. Yanzu a wannan zamani irin wannan kyakkawar al’ada tamu tazama tarishi, sai ayi bukukuwan sallah a
gama bazakaga kowa a gidajenmuba. Kai koda wakilan kananan hukumominmu dawuya kasami guda uku daga cikin takwas sunzo domin sada zumunci kamar yadda akeyi a shekarun baya.


Kuma abin mamaki saika iske sauran masarautu bahaka sukeba, zakaga kowane shugaban karamar hukuma yazo sun hallara domin tattauna matsalolin wannan masarauta.




Shin minene yajawo
hakan? Nomi jide-: Inna tsammanin wannan al’ada tamu itace tasa ake cemana “Hadejia tsintsiya madaurinki daya”. Watau dadama daga cikin mutanan dake cikin Birnin Hadejia a shekarun baya sunada gidajensu nagado dakuma gonaki a kauyuka, aduk lokacinda damina ta sauka sukan koma gidajensu dake kauyuka
domin yin noma. Bazasu dawo gariba sai bayan damina. Zan iya tunawa mahaifina wata shekara muna shira game da wannan dabia tamu, sai yace mini: aduk cikin lokonmu gidanmune kawai yake ragewa da mutane idan damina ta sauka. Sauran makwabta kowa yakan koma kauye dominyin noma.


Saboda haka yan’uwa tayaya idanba hudubar shedanba zamu banbanta mutumun birni da kauye? Amsata shine duk mutumin kauyen Hadejia Dan Garin Hadejia ne sannan kuma duk mutumin Birnin Hadejia dan kauyen Hadejiane.


Tambaya anan itace idan Maganar danayi a baya gaskiyace, shin akwai maana idan mukayi maganar rabuwar kawuna tsakanin mutumin kauye dana birni?


Ga-manda-: wannanma wata tsohuwar al’adace tamu ta Hadejiawa da take kara nuna mana karfin dangan taka tsakanin kauye da birni. Bayan al’adar Nomu jide wanda kamar yadda nafadi a baya take nufin zuwa kauyukanmu da damina donyin noma, idan mungirbe mu kwaso amfanin zuwa gidajenmu na birni. Ha’ilayau mutumin birni musamman ma Mata sukan je ziyarar yan’uwa kauyu kammu bayan an kawo amfanin gona gida.


Ayayinda zasu tafi sukanyi guzurin
kayan miya wanda baa fiya samunsu a karkaraba, sukuma ayayin da suka gama zayararsu, yan’uwanmu na kauye sukan basu
amfanin gona kamar su: gero, dawa, wake dadai sauransu domin yin guzuri. Inna tsammanin wannan alada tamu haryanzu tananan anayinta tsakaninmu, to kaga kuwa ashe idan akwai wadannan dagantaka to ashe gaba dayanmu Hadejiawa yan’uwan junane. Saboda haka miye dalilin rabe raben kawuna tsakanin kauye da birni?




Sarauta-: Kowa yasani Sarautarmu ta Hadejia dama ta sauran kasashen Hausa ana nada Mai sarauta watau hakimi ko dagaci daga cikin yayan sarakai dake cikin gari a turasu kauyukammu domin yin mulki. Sannan ayayin
da hakimi zai tare kasarsa yakan tafi da sauran yaransa wadanda zasu tayashi mulki yazuwa kauye. Kuma dadama daga cikinsu idan sukaje zasu auri mata acan daganan sunzama yan can kauyen.


Shiyasa duk wani mai sarauta ko yaran mai sarauta a kauye idan aka binciki tarishinsu zaka iske zuwa yayi tare da hakiminsa ko dagacinsa Watau mutumin birnin Hadejiane, musamman ma da ya kasance al’adarmu ta Hadejiawa ta banbanta data Kanawa maana duk wanda fada ta tura kauye domin wakilci to zai zauna ne dindindin watau babu canji. Shiyasa idan shekaru sukayi yawa bama iya gane cewar zuwa mukayi donyin sarauta ba a nan muke ba shekarun baya. To amma abin mamaki saika iske yaron hakimi ko dagaci yana korafin nuna banbanci tsakanin birni da kauye. Shin akwai ma'ana a wannan dabia?


Allah yasa mugane.

Sunday, August 11, 2013

JAWABIN ALH. BAIDI GAJO YELLEMAN A BUBBAN TARO DA AKAYI DON HADIN KAN Al'UMMAR MASARAUTAR HADEJIA. (KASHI NA DAYA 1)

Free Web Proxy
Jamaa Salamu Alaikum. Na tsaya gabanku ne a game da izinin da aka mani akan in yi bayani gameda “Cusawa matasa kishin masarautar Hadejia”. Shi dai kishi wani kauna ne da mutun yake dashi na wani abu, ko Kasa, Addini, Mutum da sauransu. Misali Kishin da mutum yakewa kasarsa, Mace da take game da mijinta, mutum yake game da addinsa. Wannan tsanannin kishin zai iya sa mutum yayi dukkan abinda zai iya domin yaga cewa ya amfani abinda yake kishin kuma yakare
martabarsa. Kakan yi amfani da kishi don ka cimma kyakkyawar manufa mai amfani.


Wani babban alamarine da zai sa kayi duk abinda zaka iyayi iyakar karfinka domin shi wanda kake kishin ko abinda kake kishin.


Kasar Hadejia al’ummace da Allah Yayiwa dimbin albarka ta fannoni daban daban na rayuwa Kamar dimbin masu Ilimin addini dana zamani, Manyan Sarakuna, Attajirai, Manyan yan siyasa, Manyan Maaikata tun shekaru aru aru. Idan nace kasar Hadejia ina nufin Hadejia, Auyo, Birniwa, Guri, Kafin Hausa, Kaugama, Kiri kasamma da Malam Madori.


Bari muga yanda maganar kishi ta shigo a harkar jamaar Hadejia. Sanin kowane cewa yakamata ace Hadejia ta wuce inda take dinnan kasancewarta Mai sarautar daraja ta daya tun shekaru aru aru, kuma mutanenta ne suke mamaye aikin Gwamnati tun Kano State har yanzu a Jigawa State sannan kuma a gwamnatin tarayya. To amma har yanzu mun san akwai sauran abubuwa da yawa da muke bukata don mu cimma burinmu na samarda abubuwan more rayuwa ga jamaarmu. Su
wadannan abubuwan more rayuwa kuma suna samuwane ta hanyoyi daban daban. Jamaa zasu taru su hada karfe da karfi don su
samarda wadannan abubuwa.


Amma almuhimmi shine abinda zaa samowa jammaa daga hukuma, wato Gwamnati.
Hanyoyin samu wadannan abubuwa shine zai nuna tsananin kishin da zakayi na samosu daga hukumar da abin ya shafa. Babban
maaikacin Gwamnati zai iya samawa matasa aiki a gwamnati, zai iya kawo Maaikata (Project), ko Makaranta, Titi, Asibiti. Ko ruwansha a bangarensa. Dan Siyasa zai iya amfani da mukaminsa yakawo duk abubuwan da na lissafa a sama. Attajirai zasu iya kawo kamfanoni. To idan wadannan suka hada karfe da karfi, nan da nan zaka ga
abubuwa sun bunkasa ta kowane fanni kuma jammaa sun sami biyan bukata. Ina tunanin ko muna da irin wannan tsananin kishi da nake nufi anan. Idan kuma muna dashi, to ina tunani ko muna amfani dashi yanda yakamata don ciyarda alummarmu gaba.


In Ciyaman Local Government bashi da kishi, ina zaiyi aiki?


Idan Dan Majalisa bashi da kishi, ina zai yiwa jamaa kyakkyawan wakilci?


Idan babban maaikacin gwamnati bashi da kishi, ina zai kawo ayyuka (Projects) garinsu?
Da sauransu.


Anan ina so inyi wasu yan tambayoyi: MU HADU A KASHI NA BIYU (2) DON JIN TAMBAYOYIN.

JAWABIN ALH. BAIDI GAJO YELLEMAN A BUBBAN TARON HADIN KAN AL'UMMAR MASARAUTAR HADEJIA. (KASHI NA BIYU 2)

Free Web Proxy Hadejia A yau.


Anan ina so inyi wasu yan tambayoyi:


1. Kana da kishi ne sai ka jira Mai Martaba Sarki ya tura ma tawaga a gaya maka jamaar Hadejia suna bukatar abu?


2. Kana da kishi ne sai ka jira har jamaa sunyi zanga zanga kafin ka biya musu bukata?


3. Kana da kishi ne baka son zuwa garinku ko cikin jamarka?


4. Kana da kishi ne kake yiwa garinka shigar dare kuma a mota mai tinted glass don kada a ganka?


5. Kana da kishi ne zaka rike mukamin gwamnati har kayi ritaya baka kari jamaarka da komai ba? Da sauransu.


Shi kishi ne zai sa kayi abu ba sai an sa ka ba, kuma in kayi ba sai an gode makaba. Rashin wakilci mai kyau duk rashin kishi ne yake kawo shi. Saboda haka idan dai muka dore akan wadannan abubuwa biyar da na lissafa a sama, to gaskiya babu inda zamu.


A duniyarmu ta yau, da wuya wani ya dafa maka abinci ya sa ma a bakinka. Kai ne zaka yunkura ka nemowa kanka yancinka ko kuma abinda zai amfaneka. Sabida haka dole musa kishi a zukatanmu don mu samowa lardinmu abinda yakamata daga gwamnatin Jiha har gwamnatin tarayya.
Babban burinmu shine mu sami Jiha (Hadejia State). Domin idan ka sami jiha, to duk wasu abubuwa na ci gaba zasu zo da sauki.


To amma kafin mu sami jihar, yakamata muci gaba da amfani da dimbin arzikin da Allah Ya bamu na masu ilimi, Sarakuna, maaikata,
manyan yan siyasa da yan kasuwa domin cimma duk wani cigaba da muke bukata.


Alhamdulillahi muna da Manyan maikata kamar Directors Permanent Secretaries, Ministoci, Soja, Yan Sanda da sauransu. Idan muka hada karfe da karfi muka sa kishi a alaamuranmu babu inda bazamu kaiba. Tarihi ya nuna akwai inda mutum daya mai kishi ya kawowa jamaarsa cigaba.
Saboda haka kara jaddadawa iyayenmu da yayyenmu da kuma musamman matasa manyan gobe gameda duk abinda zasuyi su sa kishi da hadin kai a gaba. Mu zama tsintsiya madaurinki daya muna haduwa da juna muna tattaunawa muna tsaida shawarwari kuma muna daukan dukkan matakin da yakamata don muga cewa mun cimma burinmu.
Matasa kune kunnenmu, kuma kune idanunmu. Saboda haka duk abinda yakamata Jamaa su sani, ku yakamata ku jaddadashi domin a dauki mataki. Har abada yin shiru baya warware matsala sai dai ya kawo rashin jituwa marar amfani Allah Yasa wannan taro ya zama dalilin samarda hadin kai da cigaba ga alummar Hadejia da Jigawa baki daya.