"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, August 6, 2019

THE SEDIMENTS OF COLONIAL MASTERS SYMBOLS IN HADEJIA. By Ahmed Aliyu Ilallah

HADEJIA A YAU!


 


A rejoinder to Babangida Usman Hadejia
………………………
Com. Ahmed Ilallah 

It will be difficult to describe the moods of concerned people on this issue. we should note that, the disturbed feelings is beyond the people of Hadejia but a global issue. But what always muddled my mind and some people alike, this kind of issues is just like a children nights tells by elders, it will just pass-bye, no action will be taken to address it. 

Mal. Babangid Usman has given the prerequisite information on this historic matter. My quest on the issue and other related issues concerning the historic symbol of Hadejia, that may come later in trigger by me or other people, showed that the site of these buildings is not in possession of any public organization (LG, SG, EC..). The sites including the structures are sold by either the State Government or Local Government to private individuals for residential purposes. 

This action is direct insult to the legacy and history of Hadejia and purely demonstration of either obliviousness of the antiquity or unpatriotic custom to the legacy of colonial history in Hadejia.

Many states in the country haven’t destroyed their history, in abridged quest for Arewa House in Kaduna.

With due respect, I wish to refresh the memory of all the stakeholders on this issue. I am also drawing the attention of: the Jigawa State Government, HE Abdulkadir Namadi, Senator Ibrahim Hadejia, Hon. Ibrahim Kamfani  Auyo, Hon. Mallam AbubakarJallo, Hon. Maikanti to please retract these site back to the public authority and intimate the relevant authorities to develop it for  future economic and social development of the region.

I am appealing to the current possessors of the lands to please, stop developing and destroying the site for general public interest.

To the people of Hadejia to please, get ready for all of us to buy-back the lands and take it back to the relevant public authority, by donating at least N5 for an approximate over 1.8m Hadejiawa  to save the image of our region, if the above failed to consider
 (a suggestion).

alhajilallah@gmail.com

Thursday, August 1, 2019

THE NINGI MOUNTAINS OF NORTHERN NIGERIA 1846-1902

HADEJIA A YAU!

                   An Islamic Frontier Polity:

Frontier areas often provide refuge for those in rebellion against the metropolitan society. But once on the frontier, they face certain organizational problems. If there is a local population, they may meld into it, or keep apart from it, or try to use it for their own purposes. And the immigrants are often forced, sooner or later, lnw some kind of relationship with the metropolitan centers. This paper examines the case of a group of Hausa mallams (learned men) who fled their own society and established a polity on the fringe of the Sokoto Empire, in the Ningi mountains of the Jos Plateau of northern Nigeria. They came to live in an area occupied from time immemorial by vigorous but small-scale "pagan" societies, with rudimentary forms of organized political authority. At the same time, the immigrant mallams had not withdrawn entirely from the reach of the organized states-emirates led by the Sokoto Caliphate. Thus, paradoxically, this Muslim reformist polity came to depend on an alliance with its new non-Muslim neighbors in order to survive pressure from the Muslim states with which it had immensely greater cultural affinities. The contradictions that this entailed are at the heart of our story.

THE MALLAM REVOLT IN KANO
Kano Emirate was perhaps the most important of all the emirates in the Fulani-dominated Sokoto Empire that emerged after the successful Fulani jihad of 1804-1808. By the mid-nineteenth century, Kano had become not only an outstanding metropolitan center of Islamic learning but also the financial entrepot for the Caliphate. But like many empires, Sokoto began to suffer from the Costs of expansion and its citizenry responded in various
ways to the increasing burdens of rents and taxes. Most, to be sure remained loyal; others joined dissident brotherhoods; and some fled to the fringes of the empire (Last 1970;345-357). 

At the end of 1846, some sixteen Hausa learned men (mallams) and their families, led by Mallam Hamza, left the Islamic center of Tsakuwa in Kano Emirate, pursued by Kano forces for their refusal to pay the land tax (kurdin kasa) a tax from which they had been exempted before the Fulani Hamza never developed into a cohesive brotherhood (tariq). Instead, its retreat into a non-Muslim area on the frontier of Islam made it the founder of a predatory polity.

THE NINGI FRONTIER ZONE
The area into which Hamza's mallam community moved was peripheral to the Islamicized metropolitan centers of northern Nigeria sociologically, culturally, ethnically, politically, and geographically. In this sense, it may be regarded as a frontier zone. The Ningi area is the northern most extention of the Jos Plateau massif. It is mountainous, incised with valleys suitable for plain and terraced agriculture. Most of it is some 2,000 feet above sea level, the central area rising to 3,000 feet and peaks reaching 6,000. The Ningi area of our story nearly coincides with present Ningi Division, which is just under 2,000 square miles. The area expences a completely rainless season and it genetally shares in the hardships of the "famine zone" of the Western Sudan (Renner 1926:583- 596).

Even in the remote past, Ningi appears to have been an isolated fringe area from the perspective of the flatlands on which arose the old Hausa city-scates. It shows a great deal of cultural and linguistic diversity and it had never developed, within historic times at least important integrative networks among its communities. It is impossible CO know what the 
population of Ningi was when the mallams arrived. The first assessment in colonial times, done in 1908 (Groom 1910), gave a total population of some 21,500, some 17,000 of these being of "original" stock. Among these, the largest groups were the Warji (ca. 7,000), the Pa'a (ca. 5,000), and the Buta (over 3,000); the other groups were each in the range of a thousand or less. These figures suggest that the non-Muslim population that the mallams found and thac came to represent their "reservoir" of economic and military strength was in the range of a score of thousands. 

Sunday, June 2, 2019

SABBIN MASARAUTUN KANO.... Daga Fatuhu Mustapha..

HADEJIA A YAU!

Sabbin Masarautun: Rano Gaya, Karaye da Tatsuniyar Bayajidda... 



Daga Fatuhu Mustapha.

Dama dai mun san meye asalin garin Bichi, domin bawani jimawa yayi ba. Amma meye asalin kafuwar wadannan garuruwa da na lissafa a sama? 

Akwai hanyoyi kusan hudu da zamu fahimci kafuwar wadannan garuruwa, sun hada da...... Tarikh Arbab Wato Kano Chronicle, Hausa Girgam, Wakar Bagauda da kuma kundin WaraĆ™a Maktuba fiha-asl al Wangariyun. Wadannan sune manyen kundayen da ake dogaro dasu akan tarihin kasar Kano.  

Amma kafin nan, bari mu koma baya mu fahimci me ake nufi da kasa, mai kuma ake nufi da gari. Kasa dai kamar yadda zamu ce kasar Kano, kasar Katsina, Kasar Zazzau, Kasar Zamfara, na nufin wata nahiya dake zaman kanta, Wadda a turance ma iya cewa tana da Sovereign power ko kuma authority, da take gudanar da alamuranta ba tare da wani katsalandan na wata kasa ba. Acikin littafin Raudatul Afkar, na Malam Gidado Bin Mustapha (Malam Dantafa), ya bayyana wannan yanki namu da sunan Sudan ta Tsakiya, wanda ya banbanta su da Sudan Madaukakiya da kuma Sudan Makaskanciya. Kasashen Sudan a cewar malamin sun hada da: Borno, A'ir, daulolin dake sahara, Kano, Katsina, Gobir da Zazzau. Wadannan a cewarsa sune kasashen dake Sudan ta Tsakiya. Ba shi kadai ne ya ambata haka ba, shehin Malamin nan na Timbuktu wato Ahmad Babq al Timbukti a wata amsa da ya aikewa wani almajirinsa dake zaune a kasar Masar wato Ibrahim al Isi, wacce ya kira da Al Kashf wal Bayn fi hukm mujallab al Suud, ya bayyana cewa " amma kasashen Hausa sune: Kano, Katsina, Zazzau, Gobir da kuma Borno " in banda Borno da ya sanya aciki, dukkan wadannan kasashe, an tabbatar da Dauloli ne masu zaman kansu a kasar Hausa. Duk wata Daula da kaji to daga baya ne. 


  1. Kafuwar Daulolin Tsakiyar Sudan 


Mafi dadewa a iya saninmu sune Daular Tumbi da Washa, wanda a yanzu Tumbi wani kauye ne a kasar Gumel, yayin da Washa ke kasar Damagaram. Wadannan dauloli sunyi karfi kwarai a wasu lokuta masu tsaho, sai dai bawani cikakken nazari a kansu, dalilin kafuwarsu, karfinsu da kuma dalilin rushewarsu. Amma dai mun san tun shekara sama da dubu, dakarunsu kan kai hari zuwa Kano da Katsina da Zaria. 

Kasar Kano da Asalin Mulkinta 

Shaidu na tarihi sun tabbatar da cewar kasar Kano ta samo asali ne, tun kusan fiye da shekaru 3000 da suka gabata, bayan da wasu kabilu da ake kira maguzawa (Majusawa: kamar yadda Murray Last ya bayyana asalin sunan), Wanda ake zaton sun taso ne daga tsibirin Dahlak na kasar Ethiopia wato Habasha. Wannan kabila sun zo nan kasar Kano karkashin jagorancin wani babban limamin addininsu maisuna Dala, da kuma wasu yanuwansa guda uku: Kanau, Ranau da kuma Gayya.

Wadannan mutane ba yan siyasa bane tun farko, hankalinsu yafi tafiya wurin yada addininsu na Maguzanci, daga sune aka samu firqoqi ko dariqu irinsu Gwandarawa dake jihar Nasarawa a yau, Arna da a yanzu kusan duk sun koma Kirista, da Domawa dake kasar Kazaure da Kismawa dake Dambatta da sauransu. 

Sun kafa wurin bautarsu a kan dutsen Dala dake cikin garin Kano Wanda suka kira Kakuwa, inda Suke bautar wani aljani da suke kira da Tsumburbura, Danko, ko Shamus, Wanda Malam Adamu Na Maaji yace shine Yaquqa da ake bautawa tun zamanin Annabi Nuhu acikin littafinsa: Iilan bi Tarikh Kano. Wasu kuma yanki suka kafa nasu bautar a Bakin Ruwa, inda suke bautar Ruwan Jakara (sai dai wadannan ana ganin ba Maguzawa bane, asalinsu Abagayawa ne). Akwai kuma wasu masu bautar bishiya wata Tsamiya da ake kiransu da Gazargawa, wadanda ke zaune a Madatai. Da Gwandarawa dake bautar farji a dutsen Bompai da sauransu. 

A wannan lokacin garin Kano ba komai acikinsa in banda wuraren bauta, a saboda haka baa noma kasar, ko ayi farauta, ko yaki ko a haki maadananta. Wannan babban laifi ne ga addinansu. A wannan hali bukatar siyasa da ta tattalin arziki ta taso, Wanda ya sanya, bayan rasuwar Dala, wasu daga cikin kannensa suka ga bukatar lallai su nemawa kansu da mutanensu mafita. A saboda haka suka fara tarwatsewa daga Kano. Ranau da yake zaune a Kusurwa (nan inda gidan Galadiman Kano yake a yanzu wato gidan Wambai) ya tashi ya koma wani wuri da ake kira Zamna Gaba (wato Rano a yau) ya kafa gari. Gayya ma ya tashi ya koma ya kafa garin Gaya. A ka bar Kanau a matsayin babban limamin addininsu a Kano. Amma duk da wannan suna tare da cibiyarsu ta addini dake Dala. Babu wata shaida da ta nuna, wadannan garuruwa sun kafa wata kasa tasu mai zaman kanta. 

Bagaudawa da Sabon Canji 

Asalin Bagaudawa dai Hausawa ne dake zaune a yankunan kasar Bauchi. Akwai masu raayin kalmar Bauchi na nufin Bahaushe. A wani kaulin kuma ana zaton tana nufin 'Bawa'. A wani rangadi da Firauna Hausal ya fito, a jirgin ruwa, an bayyana cewa ya fado ta tafkin Chadi, ya biyo ta kogin Jakara, ta Hadeja Jamaare, ya shiga kasar Bauchi (Baushe)inda ya iske mutane, daga nan ya bi ta kogin Binuwai ya je har Bargu (Barku), ya bi ta kogin Kwara ya fada zuwa Tekun Atlanta ya koma gida.....

(Zamu cigaba inda zamu ji alakar Bagauda da Daura, da karairayin tatsuniyar Bayajidda) insha Allah..... 

Tuesday, March 5, 2019

JIGAWA THE SECOND HIGHEST POVERTY STATE IN NIGERIA MY ARGUMENT AND THE CHALLENGES IN THE NEXT LEVEL... By Comrade Ahmed Ilallah

HADEJIA A YAU!



My mind vibrates, when I read the report that put Jigawa as the second poverty state in Nigeria, just after Zamfara, many can easily admit the position of Zamfara, due to the current insurgency, which is taking years now.

But my concern, dismay and arguments is the position of Jigawa. Jigawa cannot be in the highest poverty level in this country, I am questioning the methodology used for obtaining the result. What are the variables and modules used in the statistics that produced the said result? If employment generations, women & youth empowerment and increased in per capita incomes are instruments against poverty, Jigawa is among the realistic state in these capacity.

Jigawa a rural state, means the majority of the population are rural residents.  The present administration policy of empowering rural women with the programme titled “Goat Multiplication Programme” has not only enriched our local women, but has also increased the populations of small ruminants in the state. The programme is just an addition to the cluster farming programme and many empowerment programmes that are professorial of Jigawa State. In fact, the government policy has attracted private investors, like Dangote Rice, Gwiwa Independent Power Project and many others, that are all on stream.

Jigawa state as agricultural state, the state, the government of federation and the private investors in the last four years have hugely invested in agriculture, specifically in rice, sesame and wheat production, which yields a significant result especially in the Northeast of Jigawa and Southwest. Jigawa State is at the top in rice production in the country. I am assured of great economy and investments development and transformation in the state in the last years, through Jigawa Invest, we have factories that are now fully working. All these are visible.

The report can be a starting challenge to the incoming administration in the state, both the executive and legislative, if the report is against our expectation and has the facts that we are at that level. The challenges would be for the leaders to have a fresh strategy of alleviating poverty in the state with good understanding of the generality of Jigawa.

Though, I am googling to have the full report, I personally question the accuracy of this investigation. 

I boldly call the state government and all the CSOs that, we are working independently for good governance to perusal the report, and enlighten the public to disregard it.

This report is faulty, Jigawa is beyond many of the overrated states.

Friday, January 4, 2019

AVM. HAMZA ABDULLAHI..

HADEJIA A YAU!

Air Vice Marshal (retired) Hamza Abdullahi (2 March 1945-3 January 2019.
Hamza Abdullahi was born in Hadejia in Jigawa State, on 2 March 1945. He attended the Nigeria Air Force Tactical Training Wing, Kaduna in 1964. He completed the Aircraft Technical Officer’s Course in West Germany (1964–1966), and studied at the Royal Military Training Centre in Chichester, England in 1974. In July 1975, Lt. Colonel Abdullahi was air provost marshal and assisted in the coup that removed General Yakubu Gowon from power, replacing him with General Murtala Mohammed.

Hamza Abdullahi was appointed the Governor of Kano State in January 1984, he announced in January 1985 that his government was revitalizing the Expanded Program on Immunization, targeting children and pregnant women at risk from preventable diseases. As Minister of Federal Capital Territory from 1986 to 1989, Abdullahi oversaw the construction of Phase 1 of Abuja. His goal was to have 75% of the ministries in Abuja by 1990, the target date for the official transfer of the capital from Lagos. He described the new city as "a symbol of our unity". Abdullahi was promoted air vice-marshal in October 1988 and retired from the Nigerian Air Force two months later. He dead 3/1/2019. May his gentle soul rest in Jannatul firdaus. 

Sunday, November 11, 2018

MATASA A FAGEN SIYASA.....

HADEJIA A YAU!



1. MATASA A FAGEN SIYASA.  
Da farko zamu dubi kalmar matasa ko matashi, me ake nufi da matasa?
Matasa ko matashi wata kalma ce ta Hausa wadda ake kiran wasu mutane da ita, (Mai Tashe) ana nufin wadanda shekarunsu ya fara daga goma sha takwas  18, zuwa shekara Arba’in 40. Domin ko a musulunci matasa su aka fi bukatar su bada gudunmawarsu don ci gaban al’umma, sannan matasa sune suke shirya duk wani tsari mai inganci na zaman rayuwa wadda idan sun gyaru hakika al’umma ta gyaru.

Matasa a fagen siyasa suna da muhimmiyar gudunmawa da zasu taka domin dorewar Demokradiyya, duk wata gwamnati  bata zama ingancacciyar gwamnati saida matasa. tarihin siyasar duniya  ya nuna matasa sune kan gaba wajen juya akalar rayuwar al’umma, domin sune masu zabe kuma daga cikinsu ake zaba. Babu wata siyasa da zata ci gaba ba tare da matasa ba, kuma matasa zasu iya tsare mutuncinsu a siyasa ba tare da anyi amfani dasu an gurbata siyasa ba. Tun lokacin NPC ta Sardauna da NEPU ta Aminu Kano aka baiwa matasa dama wajen tsayawa takara a kujeru daban daban don inganta rayuwar Al’umma, misali duk dan takarar da ya tsaya takara a lokacin Npc da Nepu babu wadda shekarunsa suka wuce 40, duk daga 35 ne zuwa 37. Haka akayi har zuwa zamanin NPN da PRP Idan ka debe shekarun Shehu Shagari daga lokacin da yayi mulki zuwa yau zaka gane lalle yayi Shugabancin Nigeria ne yana Matashi, Haka Gwamnonin zamaninsa irin su Rimi da sauransu har zuwa Senatoci da ‘yan majalissun Tarayya da na jihohi. Tun daga wancan lokacin zuwa yau matasa ne suke jan akalar Siyasar Nigeria, dukda cewa ana samun tsarmi da yawa da mutanen da muke kira Dattijai. Idan muka dubi lokacin Gwamnatin Saminu zamu ga yayi gwamna ne shekarun sa basu kai Arba’in ba, haka Mataimakin sa Barrister Ibrahim Hadejia ya zama Deputy Governor yana da Shekara 37 zuwa 38. Wannan yana nuna mana cewa Matasa sune dai a fagen Siyasar Nigeria, amma yanzu abin haka yake kuwa? Wadannan mutane da na saka hoton su wato Mustapha Sule Lamido, Ahmed Bello, Hussaini Rally, Barr. Mallam Abubakar Jallo, sune suka fanshi Matasa a fagen Siyasar wannan lokaci, kuma sune zasu zama fitila ga sauran matasan mu zuwa nan gaba, domin sun kasance sun karfafawa matasa Gwuiwa wajen damawa dasu a fagen Siyasa.

MECECE SIYASA?
Ma’anar siyasa itace tsara rayuwa ko samar da shugabanci da duk abinda yake ta’allake dashi, kamar tsarin zabubbuka, yin doka, umarni da hani. Tsarin horo ga wanda ya karya doka, kira ga hukuma da tayi ko ta bar wani abu.

Haka kuma kalmar siyasa kalma ce ta larabci aka arota zuwa harshen Hausa, ita kalmar siyasa ta samo asali ne daga ‘SASA’ ko ‘SULASI’. Kaga kenan wannan kalma ta “SIYASA” tana nufin Jagoranci, hikima, kiwo, horarwa da gudanarwa. Haka kuma ana amfani da siyasa yayinda wani abu na son zuciya ya shiga, amma wannan ba shine ainihin  kalmar ba. Ilmi yana da matsayi mai girma a tsarin siyasar kowace Al’umma. Daga kaarshe ina Addu’ar samun Nasara ga Matasa da suka tsaya Takara a kujeru daban daban, Allah ya tabbatar mana da Alkairi a Nigeria baki daya.

Matsayin Ilmi a siyasar Turai... masu ilmin falsafar Turai sunyi  ijma’i  game da muhimmancin Ilmi a siyasa. Plato yana ganin masu ilmi ne kadai suka cancanci su shugabanci jama’a, yayinda shi kuma  Aristotle yace A’a idan ana son siyasa ta inganta sai a baiwa jama’a  Ilmi. Shi kuma Spinoza cewa yayi amfanin siyasa shine ‘yanta Dan-adam da samar masa da Adalci, wannan kuwa bazai samu ba sai an bashi Ilmi. Shi kuwa Emanuel kant yana ganin rayuwa ce gaba daya sai da ilmi, yadda zaka kare lafiyarka, yadda zaka nemi Aure ka rikeshi, yanda zaka zabi shugaba.

Wasu mutanen su dauki ma’anar siyasa kamar wata kasuwa ce ta baje hajoji, inma a samu riba ko a samu faduwa. Irin masu wannan tunanin ne ake kira ‘yan siyasa marasa akida, domin su babu ruwansu da abinda ya dace illa abinda Aljihunsu ya dace dashi. Wasu kuma sun danganta siyasa kamar  dabi’a ce ta halittu masu rai aga uwa tana gaba ‘ya’yanta suna biye da ita, wato mai hankali shike shiga gaba domin na baya yayi koyi dashi.

Ismaila A Sabo
Ismailasabo@gmail.com

Sunday, July 29, 2018

TARIHIN SARKIN ZAZZAU JAFARU......

HADEJIA A YAU!




TARIHIN SARKIN ZAZZAU JA'AFARU....1936-1959.
Na rubuta wannan labari nawa don in bayyana godiya ta ga Ubangiji, kuma mutane kuga tsaunukan da na taka har na kawo ga wannan matsayi.

A cikin shekarar 1911, watau ina da shekara Ashirin da hudu (24) da haihuwa kenan, aka aika dani makarantar Dan-Hausa dake Kano. Na shekara guda acan na dawo gida. rannan ina zaune sai ga Shehu Baloha masinjan Joji, yace wai Joji yana kira na a Bariki. bayan naje sai naga Razdan ya dauki lambar Masinja ya lika mini a riga ta, yace "Yau ka zama Masinja" sai na durkusa nayi godiya. aka yanka mini albashin sule Talatin (30).

 Bayan nayi shekara uku ina wannan aikin sai rannan na roki Razdan ya maida ni makarantar Turawa ta Zariya, in rika koyawa 'yan makaranta Larabci.
Razdan yace "A'a wannan aiki bazai yi maka ba" saboda haka ya kai Magatakardar sa M. Kwasau can, Malami guda kuma Malam Umaru ya maida shi aikin Shanu, nikuwa aka game mini aikin su duka nake karbar Sule saba'in (70).

Ina cikin wannan aiki a cikin shekarar 1918 sai wani Hakimi na Zangon Katab ya taba kudin Jangali, aka fishe shi, ashe Allah ya nufa Sarautar a kaina zata fada, aka nada ni Hakimcin Zangon Kataf na koma can.

Sa'ad da nake Hakimi a wannan Kasa, naga abubuwan Tashin hankali guda biyu. wata shekara ina karbar Haraji sai Arnan Unguwar Gayya suka yi mini Tawaye. ina zuwa kauyen sai naji sun dauki kuwwa, nan da nan baka suka taru makil, kowa daga kwari sai baka a hannun sa, sai kayi tsammani wani abu ne yasa wannan bore. Dalili kuwa wai sun gaji da biyan Haraji ne kawai! Abu kamar wasa sai wani Arne wai shi Gankwan ya dana kibiya, yako duban ya sako mini ita. Sai ya kuskure mini ya samu Sarkin fada na a kafada. Yara na daga ganin haka sai suka yi kazam akan Arna! da Arnan nan suka ga bamu da Alamar tsoro sai suka bada baya, suka shige Kurmi gidan Tsafi.

Muka shiga garin muka tarar ba kowa, duk sun gudu mazan su da matan su. Na kira Sarakunan su da basu cikin tawayen, na gaya musu su lallashi mutanen su su dawo, babu komai. Washegari ni kuwa na yi zuwa Mabushi. A can na samu labari sun dawo sai shi Gankwan da ya harbi Sarkin fada na shine ba'a gani ba. Na aika ga Sarkin Zazzau Dalhatu da abinda ya faru duka, yace in kara matsawa kan neman Gankwan. Amma Ina? Ai har yau ba'a same shi ba, kamar an biya bashi dashi. Sarkin fada na kwanan sa wajen Arba'in a Mabushi yana jinyar daffin kibiyar nan.

Kai Arnan Zangon Katab a lokacin suna da wuyar sha'ani wajen al'amarin Haraji! Dubi wata shekara kuma da ni da wani Joji muna kama Awakin wadanda basu biya Haraji ba a Zankuwa, ba sai muka kama na wani wadda ya biya ba? sai gashi faram faram da matar sa suka zo suka durkusa suka ce mana "Wadannan Awaki namu ne, mu kuwa mun biya Haraji" Joji yace "To mu dai mun kama Awaki. Watau Makwafcin ka ya biya kenan, in ya samu kudi sai ya biya ka."
Da suka koma gida sai matar sa ta shiga zuga mijin ta na cewa "Allah wadan ka! Ashe dai kai ba Namiji bane? yaya don tsoron Sarauta zamu yarda a kwace mana Awaki? Ina ruwan mu da Makwafcin mu da zamu biya masa Haraji? Kai in baka dauki Kwari da baka ka tarad da Baturen nan ba, ina sa Wuta in kone su in kuma rabu da kai." Daga nan sai maigida ya dauki Kwari da baka ya tanka, 'ya'yan sa kuwa kowa ya dauko tasa, suka nufo wajen mu zasu tada Jihadi. Da na hango shi sai na daka masa tsawa sai ya yada Baka sai yazo ya fadi gabanmu yana haki. Na lallashe shi, na bashi magana sa'an nan ya koma. Ka ji tashin hankali da na hadu dasu lokacin ina Hakimcin Zangon Katab.

Na samu wannan Sarauta zamanin Sarkin Zazzau Aliyu ne, bayan shi aka nada Dalhatu. Daga nan sai Sarkin Zazzau Ibrahim ya kama Sarauta, shi kuma ranar 31/1/1937 ya rasu. Allah yaji kan su Amin. Bayan rasuwar Sarkin Zazzau Ibrahim, ina Hakimci a Zangon Katab sai ga waya ana nema na a Zariya, don Gwamna da manyan mashawartan Zazzau sun yarda in zama Sarki a shekarar 1936.

Madogara... Gaskiya Ta fi Kwabo ta 17. 1939.

 Daga nan sai na koma Zazzau da zama, muna rokon Allah da ya taimake mu rikawa Amin.

Sarkin Zazzau Ja'afaru shine dan M. Isyaku Sarkin Zazzau, dan Sarkin Zazzau Abdu dan Hammada. Allah ya masa rahma. 

Wednesday, February 14, 2018

HADEJIA.....

HADEJIA A YAU!


                     MASARAUTAR HADEJIA………

  1. Takaitaccen Tarihin Masarautar Hadejia .
Masarautar Hadejia dadaddiyar  masarauta ce wadda ta kafu shekaru da dama da suka gabata, daga lokacin kafuwarta kawo yanzu masarautar tayi fice da kuma yin suna bisa ga muhimman tarihi da take dashi. sannan tana daga cikin masarautun da sarakunan Habe suka mulka kafin Jihadin Shehu Usmanu Danfodiyo, kuma tana daya daga cikin masarautun da suke KarKashin Daular Usmaniyya. Daga Gabas ta yi iyaka da Tsohuwar Daular Borno da Gorgaram, daga yamma tayi iyaka da Masarautar Kano, daga Kudu kuma ta yi iyaka da Masarautar Katagum sannan daga Arewa ta yi iyaka da Masarautar Gumel. Birnin masarautar yana cikin garin Hadejia dake Arewa maso gabashin Jigawa a Arewacin Nigeria, sunan garin ya samo asalinsa daga wani Maharbi wadda shine ya kafa garin, wannan maharbi ana Kiransa da suna HADE, yana da matarsa da ake Kiranta da suna JIYA, Sunayen wadannan mutane shi aka hada ya zama Hadejia . A wancan lokacin mutanen wasu garuruwa in zasu zo sukan ce mun tafi garin Haden jiya, wato ana masa Lakabi da sunan Matarsa. Saboda taKaita kalma ta Hausawa shine yasa aka hade sunan ya zama Hadejia . A wani littafi da Marigayi Tafidan Hadejia Abdu Maigari ya rubuta ya bayyana cewa ‘‘Shi wannan mutumin da ya kafa Hadejia wato Hade ya taho ne daga yankin Machina a yawon farauta da yake har ya iso wannan yanki, kuma da ya shigo sai yaga Daji mai Ni’ima da tsuntsaye da namun daji ta ko ina, kuma ga kogi ya fito daga yamma ya gangara zuwa gabas Sannan ga ‘ya’yan itatuwa kala kala. Da ganin haka sai ya kewaye dajin sosai don ya samu inda ya dace ya zauna, sai ya samu wuri ya kafa Gadonsa irin na maharba yaci gaba da farautar Namun daji da tarkon tsuntsaye’’. Bayan kwanaki wannan maharbi yana zaune a wannan wuri sai yayi shawarar ya koma ya Dauko matarsa don suci gaba da zama a wannan wuri. A lokacinda yayi niyyar komawa sai ya debi abinda zai iya diba na naman da yayi farautarsa ya dawo garinsu ya Dauki matarsa ya koma wannan dajin da yanzu ake kira da suna Hadejia , sai ya kafa bukkarsa a kan jigawa kuma yaci gaba da farautarsa a wannan wuri har mazauna karkara dake kusa da wurin suka san da zamansa suke zuwa sayen nama da sauran dabbobin daji. Ana haka ne jama’a suka rinKa zuwa suna kafa bukkokinsu wasu masunta wasu kuma mafarauta da masu kamun tsuntsaye har gari ya zama gari ake Kiransa Garun Haden Jiya, sannan akayi shugabanci, zuwa wani dogon lokaci aka takaita Kalmar ta zama Hadejia . Ance a lokacinda ya zauna a bangaren Arewa akwai wani gari da ake Kira Hadegwaigwai inda yanzu Rubban Dakata take, sannan a bangaren gabas akwai gari da ake kira Kulunfarda inda ada can yake kan hanyar Tandanu. A yamma kuma akwai garin Kadime sannan a Arewa akwai garin da ake Kira Majeri, a bangaren kudu kuma akwai garin Tunawa wadda yanzu ake Kira Auyakayi. Sannan akwai Kudiginda HadebaKo wadda a lokacin take kusa da Kafur, sannan akwai Urki wadda yanzu ake Kira Unik sannan akwai Majawa, da kuma manyan garuruwa irinsu Auyo, Garungabas, Kazura, Dawa da Fagi.

A wancan lokacin ance Hadejia tana Karkashin Daular Auyo ne amma wasu sunce a’a tana KarKashin Ikon Garungabas ne tunda daga can ne ake nada Sarki ake kawoshi Hadejia, masu wannan da’awa sun bada labari kamar haka…  ‘A zamanin Sarkin Kano Yakubu Dan Abdullahi Barja wadda yayi sarautar kano a cikin shekarar (1452-1463), Algalfati Dan sarkin Machina yaje kano tare da ‘yan-uwansa guda uku inda sarkin kanon ya bashi sarautar Gaya, dan-uwansa na farko kuma yaje Rano sarkin Rano ya bashi sarautar Dal, na biyun kuma yaje Zazzau Sarkin Zazzau ya bashi sarautar Gayan, na ukun yazo Biram Garungabas inda Sarkin Gabas ya bashi sarautar Hadejia . Zuriyarsa ne sukayi mulkin Hadejia har tsawon lokacinda Sarkin Borno Mai Ali Ghaji ya tura Dansa Mai Idris Aloma ya yaki kano, sai ya biyo ta Hadejia ya yake ta ya cinyeta da yaki da sauran Kasashen dake yammacin Borno, sai ya danka ikon Hadejia da Garungabas da Dawa da Fagi a hannun Galadiman Borno, kuma shi Galadiman Borno sai ya barsu a rarrabe kamar yadda suke tun farko. Sashen Auyo ya barshi a hannun sarkin Auyo, Hadejia ya barta a hannun sarkin Hadejia , Garungabas ya barta a hannun sarkin Gabas, sannan Dawa da Gatare da sauran duk sai ya barsu a hannun fadawansa, amma duk a wurinsa suke karbar umarni kuma shi ake kaiwa Albarkar Kasa har zuwa tsawon lokaci’.  Koda yake ba’a samu rubutaccen tarihi game da sarakunan Habe da suka mulki Kasar Hadejia ba, ance anyi sarakuna guda Talatin da biyu (32), kafin mulkin Fulani. Masarautar Hadejia tana da fadin Kasa wadda ta kai Murabba’in kilo mita dubu shida da Dari tara da sittin da uku (6963), wannan yanki yana da shimfidaddiyar Kasa mai kyau wadda ake kwatanta yanayinta da na Kasar Chadi, kuma tana da Jigayi masu tarin yashi da kuma kwari mai tabo da laka amma bata da tsaunuka ko Duwatsu. Kasar Hadejia tana da Kogi wadda ya kasance akwai ruwa kowane lokaci, sannan tana da fadamu masu yawa wadanda suke Kafewa lokaci zuwa lokaci. Kogin Kasar Hadejia ya taso ne daga Kudancin Katsina ta Arewa da Zaria sannan ya nufi Arewa maso gabas ya shigo ta Kasar Kano ya ratsa Kasar Hadejia, sannan ya nufi Tafkin Chadi. Wannan Kogi ya ratsa ne ta Kudancin Hadejia da Gabashinta, wannan bangare ne da yake samarda ruwan sha da kamun kifi da kuma aiwatar da Noman rani. A lokacin damina kogin yakan cika inda yake samarda Kananan fadamu a sassa daban daban wadda ake amfani dasu a wajen noman lambu. A bangaren Noma Masarautar Hadejia tana gabatarda noma a lokuta biyu wato Rani da Damina, inda masana yanayin Kasa suka tabbatar cewa duk abinda aka shuka a wannan Kasar zai fito yayi kyau da iznin Allah saboda yanayin kyawun Kasar.


GUDUNMAWAR DA MASARAUTAR Hadejia TA BAYAR GA DAULAR USMANIYYA….
Masarautar Hadejia kamar sauran Masarautu ta bada gudunmawa sosai wajen tabbatar da kafuwar Daular Usmaniyya, domin tana daga cikin masarautun da suke iyaka da Daular Barno. Masarautar Hadejia ta nuna goyon bayanta ga Jihadin Shehu Usman Danfodiyo a zamanin Sarkin Fulanin Hadejia Umaru. Sarkin Fulani Umaru yana nan yana sarautar fulani sai suka samu labarin jihadin Shehu Usman Danfodiyo , Bayan yaji labarin jihadin shehu sai ya tara jama’ar Fulani sukayi shawara da suje suyi Mubaya'a da Da'awar Shehu,  anan wasu manyan Fulani suka ki yarda da hakan, ciki harda Kawunsa mai suna Jinagana. Sai sarkin Fulani Umaru ya tura mutanensa Karkashin jagorancin Dan uwansa Malam Sambo, sukaje suka miKa mubaya'arsu ga Shehu da kuma nuna goyon baya ga da'awarsa ta jaddada Addinin musulunci. Shehu yayi maraba da zuwansu kuma ya baiwa Sambo Tuta kuma yayi musu umarnin shiryar da sauran yankunan nan biyar na Kasar Hadejia . Sannan yacewa Laraima ya kula da yankin Gabashin Hadejia inda Marma da Fagi da Dawa suke yaje yayi kokarin shiryar dasu kan tabarkin Addinin musulunci. Amma bai bashi Tuta ba, sai sukayi bankwana da Shehu suka dawo Hadejia suka isarda sakon Shehu ga Sarkin Fulani Umaru suka sanar dashi kyautar da Shehu ya yiwa Laraima, sai aka hada Laraima da mutane suka tafi yankinda Shehu yace yaje ya shiryar dasu wato Marma da Fagi da Dawa. Laraima sai ya zauna a Marma saida suka shiryar da duk mutanen wannan yankin, kuma ‘ya’yansa ne sukaci gaba da shugabancin wannan yanki na gabas har zuwa lokacinda Sarkin Hadejia Buhari ya hade Kasar da tasa, wadda a baya MaDaci ce iyakar Hadejia daga gabas. Wannan yana nuna mana cewa masarautar Hadejia ta bada gudunmawa game da tabbatar Daular Usmaniyya, domin tana iyaka da Daula mai Karfin gaskekuma dadaddiyar wato Daular Kanem Borno.
A zamanin Sarkin Hadejia Sambo masarautar ta bada gudunmawa sosai wajen tabbatar da Umarnin Shehu na Jaddada Addinin Musulunci, bayan rasuwar Dan uwansa Sarkin Fulani Umaru an nada Dan wansa wato Mamman Kankiya, wadda shima ya rasu cikin watanni takwas. A lokacin da Sarkin Hadejia Sambo yayi shekara yana sarautar Hadejia sai yayi niyya ya tafi wurin Shehu, da zuwansa Shehu yayi murna kuma yayi godiya ga irin KoKarin da Sambo yake a Kasar Hadejia . Bayan Sambo yayi kwanaki a wurin Shehu ya gama abinda zaiyi sai yayi sallama da Shehu yayi shirin dawowa gida, Shehu ya Kara yin godiya ga Sambo kuma ya baiwa Sambo ikon duk wani Bafulatani wadda yake da Jar Saniya (Aborawa) tun daga bakin Dajin Rubu har zuwa iyakar Kasar Barno. Daga nan sai sambo yayi godiya sukayi bankwana ya dawo Hadejia tare da mabiyansa. Wannan kyauta da Shehu ya masa ta Ikon duk Fulani masu jar Saniya (Aborawa) tasa Sambo yawan Dawainiya domin nemawa wadannan Fulani matsuguni, kuma har zuwa wannan lokaci duk Bafilatanin da ka ganshi da Jar Saniya idan ka tambayeshi zakaji Asalinsa daga Kasar Hadejia yake.  

Sarkin Hadejia Sambo ya sake faÉ—aÉ—a Kasar Hadejia daga Gabas har saida ya mamaye galibin Kasashen da Galadiman Barno yake iko dasu suka dawo KarKashin ikon Hadejia , amma banda Dawa da Fagi domin Shehu ya bada su ga Laraima. Daga yamma har saida ya kai Kaugama da Sharkawa, da Majeri a yamma ta Arewa. Daga Gabas maso kudu saida yakai har Damaturu inda ya YaKi garin, sannan daga Gabas kuma ya tsaida iyakarsa a Madachi. A bangaren Arewa kuwa galibin garuruwan sun bishi ba tare da wata jayayya ba saida ya mamaye Garungabas da Kazura da Gatare har zuwa iyakar Machina da Damagaram.
Saboda irin gudunmawa da Masarautar Hadejia ta bayar ga Daular Usmaniyya, an taba baiwa Sarkin Hadejia Muhammadu Sarautar Sarkin YaKin Sarkin Musulmi.