"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Monday, January 2, 2023

THE FULANI EMPIRE.....


HADEJIA A YAU. 


With place names, though there is a growing measure of standard- ization, a number of variations still have currency. Some of them, such as Garin Gabas and Kalembina, are incorrect and should be discarded. With others, however, where the best spelling is still an open question, a choice can legitimately be exercised. Hence Hadeija rather than Hadejia and, among proper names, Fodiyo and Jaidu rather than Fodio and Jedo.

At that time there were a number of small principalities Auyo, Bedde, Shira, and Tashena lying between Bornu and Hausa land. They were under the jurisdiction of the Galadima and it was there that the reformers now rose against the authority of Bornu. First of all a pastoral Fulani called Abdure, or Abduwa, threw off his allegiance and declared for Shehu. Although he himself died very soon afterwards, his two sons, Umaru and Sambo, obtained a flag and a commission to subdue the principality of Auyo.

This they very soon did. Next they took possession of the town of Hadejia, which they enlarged and strengthened, and from there they proceeded to extend their authority over the intervening and surrounding towns and villages. One of these, incidentally, was Garun Gabas, the only one of the original Hausa Bakwai which had failed to develop into even a principality. This territory became the nucleus of the Emirate of Hadejia.

Meanwhile, another Fulani, Ardo Lareima, had also joined the Jihad. He lived near Nguru and, before the war, had been the agent appointed by the Galadima to collect tax and tribute from the pastoral Fulani in the district. Although the Galadima had given him a daughter in marriage he declared for Shehu and urged the Fulani to rise. In the first clash Lareima was defeated, but later, when he had been reinforced by Sambo of Hadejia and Ibrahim Zaki of Shira, whom we shall meet again later, he was completely victorious.


Bornu forces were defeated, Nguru sacked, and the Galadima killed. The destruction of Nguru and the consolidation of Hadejia meant that in the northern sector of Bornu’s western frontier the reformers had been completely successful.

After the destruction of Nguru and the capture of Hadejia, the Fulani made their next move against Shira, which Ibrahim Zaki, whose adopted country it was, invaded and occupied in 1807. The three leaders then met near Damaturu and agreed upon a concerted plan of campaign. While Ibrahim Zaki attacked Tashena.

Although the Fulani had failed to crush Bornu, as before the emergence of El-Kanemi had seemed likely, they had nevertheless made substantial gains at Bornu’s expense. In the north-west Sambo Digimsa had established the new Emirate of Hadejia. In the west Ibrahim Zaki had welded Shira and Tashena together to form the new Emirate of Katagum. In the south Buba Yero had carved the new Emirate of Gombe out of pagan lands over which Bornu had previously held sway.

All these leaders had received flags from Shehu during the fighting and were now recognized by him as the rulers of the territory which they controlled.


By the year 1810 the first phase in the creation of the Fulani Empire was complete. The former States of Gobir, Zamfara, and Kebbi had been merged into one and had become the metropolitan Sultanate. In Kano, Katsina, and Zazzau, as we have seen, the Hausa Chiefs had been driven out and supplanted by Fulani Emirs. In western Bornu the new Emirates of Hadejia and Katagum had been created. Similarly, in the south-east the Emirates of Gombe, Adamawa, and Bauchi had been forged out of formerly pagan lands and were still in the process of enlarging their territory and influence.

the fulani empire of sokoto
by h. a. s. johnston
Publication date 1967.


Wednesday, August 17, 2022

GUMEL EMIRATE....

HADEJIA A YAU!



GUMEL.... The town lies at the intersection of roads from Kano city, Gujungu, Hadejia, Maigatari, and Zinder (Niger). The emirate was founded c.1750 by Dan Juma of Kano city (75 mil [121 km] southwest) and his followers of the Manga (Mangawa) tribe; shortly after his death in 1754, it became a tributary state of the Bornu Kingdom. 

The emirate survived the Fulani attacks of Usman dan fodio's jihad ("holy war") in the early 19th century and never became part of the Fulani Empire of Sokoto. 


In 1845 Gumel's capital was moved from Tumbi (20 mil north in present day Niger) to the present site; and in 1851 Heinrich Barth, a German geographer, visited the busy Gumel market, where cloth, tools, pots, cattle, sheep, donkeys, horses, and agricultural produce were traded (described in his Travels and Discoveries in North and Cen- tral Africa [1857-58]).

Wars with nearby Hadejia, Kano, and Zinder (Damagaram) plagued the emirate from 1828; the war with Hadejia continued until Gumel's emir Abdullahi was killed in battle in 1872. Slave raids toward the end of the century by Damagaram further depopulated Gumel. Emir Ahmadu submitted to the British in 1903 and the Gumel emirate, reduced in size to its present 1,205 sq mi (3,121 sq km), was incorporated into Kano Province.


The new encyclopedia Britannica in 30 volumes by Macropaedia

Publication date 1978

HADEJIA EMIRATE...

HADEJIA A YAU!

Hadejia, town and emirate, Kano Province, Kano State, Northern Nigeria. The town is on the Hadejia River (a seasonal tributary of the Komadugu Yobe, which flows into Lake Chad) and lies at the intersection of roads from Nguru, Gumel, Katagum, and Keffin Hausa.
The emirate's savanna area of 2,720 sq mil (7,045 sq km) originally included seven small Hausa kingdoms (one of which, Hadejia, was named for a hunter of the Kanuri tribe) that paid tribute to the Kingdom of Bornu.

About 1805, Umaru, a Fulani herdsman who held the title sarkin ("chief) Fulanin Hadejia, pledged allegiance to the Fulani jihad ("holy war") leader, Usman dan Fodio. Umaru's brother and successor, emir Sambo (reigned 1808-45), officially founded Hadejia emirate in 1808, moved the Fulani headquarters to Hadejia town, established a market, and began to consolidate Fulani rule over the Hausa kingdoms.

Emir Bukhari (also Bohari, Bowari; reigned 1848-50, 1851-63) renounced Hadejia's allegiance to Sokoto (a town, 325 mil [523 km] west) in 1851, raided the nearby emirates of Kano, Katagum, Gumel, Bedde, and Jama'are, and enlarged Hadejia emirate to its present size. Heinrich Barth, the German geographer, described the devastation wrought by Buhari's conquests in his Travels and Discoveries in North and Central Africa (1857-58). Hadejia was brought back into the Fulani Empire after Buhari's death, but wars with neighbouring Gumel continued until 1872.

In 1906 the British installed an emir Haruna and incorporated the emirate into Kano Province. The present emirate council governs from Hadejia town.

The town is the emirate's chief market centre, handling cotton, millet, guinea corn, fish, and rice, which is grown in the river valley, and serves as its most important collecting point for peanuts, an export crop which is trucked to Kano city (110 mil west-southwest) for shipment by rail. Cattle, goats, guinea fowl, sheep, and donkeys are kept by the local Hausa and Fulani peoples. Several small lime industries exist in scattered parts of the emirate. Hadejia town has a hospital (1935), a health office, and a maternity clinic. Pop. (1972 est.) 29,172. •map, Nigeria 13:86... 

Reference..... The new encyclopedia Britannica in 30 volumes by Macropaedia

Publication date 1978 Topics Encyclopedias and dictionaries Publisher Chicago ; London : Encyclopedia Britannica. 

Hadeja, a  large  town surrounded with a beautiful  and very strong double clay wall, and well inhabited, the courtyards being  inclosed  with  clay  walls,  but containing only reed huts. The inhabitants employ  themselves exclusively in warlike expe¬ditions, and have no industry; but nevertheless there are  still to be seen here a few dyeing-pots, marking the eastern limit  of  this branch of industry.  On the south side of the town is a kogi, or komadugu,  with a  stream of running water in the  rainy  season,but  with only stagnant  pools in summer, along which a little wheat is  cultivated.  It is generally called Rani.

HADEJIA... A large town with five gates, excellent walls about 30ft high from the bottom of ditch, and 30ft thick at base. The gates are protected in such a way that guns could not get a direct fire at them. The population is estimated at from 8 to 10,000. The circumference of the walls is about 4 and half miles..."
From
Captain HCB. Phillips (MAITUMBI) to Larymore.. 17/02/1903.



Tuesday, June 14, 2022

GIDAUNIYAR MALLAM INUWA FOUNDATION TARE DA HADIN GWIWAR QATAR CHARITY FOUNDATION SUN TALLAFAWA MABUKATA DA KAYAN SANA'A DOMIN DOGARO DA KAI.

HADEJIA A YAU!

A jiya Litinin 13/6/2022, wannan gidauniya ta gabatar da taro a garin Hadejia domin tallafawa mabukata da masu karamin karfi abubuwan dogaro da kai. Abubuwan da aka raba sun hada da Kekunan Dinki da Baburan hawa da dai sauran su. Taron ya samu Halartar Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh Adamu Abubakar Maje CON tare da Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa Mallam Umar Namadi da Shugabannin Kananan Hukumomi na masarautar Hadejia. Da yake bayani mai Martaba Sarkin Hadejia ya yabawa Mallam Kashif Inuwa bisa amfani da Ilmin sa da yake wajen ciyar da Al'umma gaba da sanya farin ciki a zuciyar su. Mai Martaba Sarki ya kara da cewa Irin wannan ci gaban Al'umma suke bukata a wannan lokaci, domin wasu suna da zuciyar yin sana'ar amma rashin abin sana'ar ya hana su. Daga karshe mai Martaba Sarkin ya yi Addu'ah ga wannan Gidauniya Allah ya daukaka ta ya basu ikon ci gaba da ayyukan Alkairi.

Bayan wannan Gidauniyar ta bude rukunin gidaje da aka ginawa masu karamin karfi, da gina famfuna da kuma kafa harsashin gina Ajujuwa a masallacin Yorubawa dake Unguwar Gawuna a Hadejia. Da yake maida jawabi Shugaban wannan Gidauniya Mallam Yusuf Baban ya yabawa Wadda ya kafa Gidauniyar sakamakon namijin kokari da yake wajen samo abubuwan da za su taimakawa Al'umma. Ko a kwanakin baya Wannan Gidauniya ta bada kyautar mota ga wata kungiyar kare hakkin mata da kananan yara da ke garin Hadejia.

 

A bangare daya kuma wannan Gidauniya ta gabatar da Aikin gyaran Ido kyauta da bada Glass din karin gani ga mutane 600, a Masarautar Gumel. In dai ba'a manta ba kwanaki an gudanar da aikin gyaran Ido a Hadejia, wadda mutane da dama suka amfana. Da suke bayyana ra'ayoyin su Al'ummar da suka amfana da wannan tallafi sun yi godiya ga wannan Gidauniya tare da fatan Alkairi, domin wannan gidauniya ta basu abubuwan da za su dogara da kan su har ma su taimakawa wasu. Daga karshe sun yi Addu'ah ga Mallam Kashif Inuwa da Gidauniyar Qatar foundation da kuma Gidauniyar Mallam Inuwa foundation domin kawo wannan abin Alkairi ga Talakawa masu bukata. 

Sunday, March 6, 2022

ELLEMAN TIJJANI.

HADEJIA A YAU!


When Umar Futi died his son Ahmadu Shehu (from the union with Satiru) became Sarkin Tijjani, or king of the whole western Fulani empire extending from Kayes on the Senegal to Aribinta in the East, and Segu became the capital. Eventually Ahmadu changed his capital to Nioro, and his son Ahmadu Madaniyo remained as his representative in Segu. Both Ahmadu Shehu and Ahmadu Madaniyo refused to allow tree passage for French traders, and in about 1893 French pressure caused them to flee to the east. It took two years to reach Sokoto, and there Ahmadu Shehu died, to be succeeded by his brother, Bashiru.
 
According to colonial records, Bashiru started on a pilgrimage to Mecca, but on reaching the Emirate of Misau, Amadu, the father of the present Emir of Misau, persuaded him to stay and gave him a town. Subsequently the Sarkin Musulmi arrived in his fight from the British and Bashiru followed him to Burmi, where he was captured and then taken to Lokoja. Mr. Temple, Resident Bauchi, made Ahmadu Madaniyo to be Sarkin Tijjani, but after the encounter at Burmi, the Tejani scattered in all directions and settled in different parts of the country. Ahmadu Madaniyo went with a few followers to Hadejia where he was given a town Dakkayawa by the Sarkin Hadejia.

Many contemporary Kano mallams believe that the flight of Bashiru from Sokoto to Misau by way of Kano was the first major contact of Kano with Tijaniyya followers. Colonial records suggest that both Sokoto and Kano gave the refugees a warm welcome. According to oral testimony, however, both the Kano and Sokoto rulers were very much afraid of the refugees, for they were numerous and well armed. The contemporary successors to Bashiru, who live in Hadejia, maintain that he did not even stop at Kano but followed a course between Zaria and Kano."

When Ahmadu Shehu reached Sokoto he is reported to have had seven sons with him; Bashiru also is reported to have had seven sons with him. The sons of Bashiru, except Dahiru and Tijani, were to die before the battle of Burmi; these two surviving sons were exiled to Lokoja with Bashiru. Ahmadu Madaniyo did not oppose the British and after Burmi was given land in Hadejia at Yalleman, where he settled with about 200 families. The descendants of this group are still living there. Tijani followers who actively opposed the British at Burmi fled to a place in Sudan near Khartoum (a village called Sennar), by way of Nahud and El-Obeid. Descendants who fled to Sudan are still settled there under the leadership of Aliyu b. Usman.

According to Isa Warure of Kano, "When Ahmadu came to Nigeria from French territory, he went to Sokoto, but was refused entry. This was probably because Ahmadu was well equipped with guns and a powerful army. The people of Sokoto were afraid of him. Therefore the Tijani people went to a place in Sokoto province called Mai Kulki, where they lived until Ahmadu died. Then the people of Ahmadu came to Kano where they asked Emir Abbas if they could have land. Again they were refused, so they went to the Emir of Hadejia, Mai Shahada, where they were received and given a place called Yelleman. 

The leader of the Tijani at this time was Ahmadu Madani. His descendants still lead the Tijaniyya in Hadejia. This settlement was quite large and was built on the banks of the river Dakayyawa. Some of the Tijani did not stop in Hadejia, but went on to the Sudan, to a place called Sennar Taqāțțu on the banks of the River Nile, near Khartoum. They called their village Dar-es Salam. They still live there" interview, Kano November 1, 1964; Hausa).

According to Muhammad Ghali, Sarkin Tijaniyya, "The trip from Sokoto to Hadejia took eight years. When the refugees had arrived in Sokoto they included about 60 chiefs, each with several hundred followers. They did not ask to stay in Sokoto because they intended to settle in Mecca. From Sokoto they did not come to Kano, but followed a route between Kano and Zaria. One representative from Sokoto accompanied them on the journey. The emir of Zaria said they could not enter Zaria; they had no communication with the emir of Kano. The actual route from Sokoto to Hadejia was as follows: From Sokoto to Gusau [Sokoto Province] to Garko [Kano Province] to Gaya [Kano Province] to Darajiya [Bauchi Province] to Bisirka [Bauchi Province] to Darazu [Bauchi Province to Wura-Dugga [Bauchi Province] to Jego [Bauchi Province] where they spent two years to Misau [Misau emirate] to Nafada [Gombe Emirate] to Hashidu [Bauchi Province] to Gungura [Bauchi Province] to Hadejia [Kano Province]" (interview, Yelleman, Hadejia, May 12, 1965, Hausa).

The contemporary Tijani community in Yalleman exists as an enclave of about 500 to 1000 families mainly traders, farmers, and mallams-under the leadership of Sarkin Tijaniyya Muhammad Ghali b. Umar, a grandson of Ahmadu Shehu. Contact is maintained between Yalleman and Senegalese. Umarian Tijaniyya, and also with the Traditional Tijaniyya of Zaria and with Reformed Tijaniyya of Kano. The emirs of Hadejia were initiated into Tijaniyya in the twentieth century (they are reported to have been sympathetic to Mahdiyya in the late nineteenth century) and are of the Umarian persuasion. The major center of Umarian Tijaniyya in northern Nigeria in the nineteenth century was Adamawa, which was partly due to the influence of Raji. These same Umarian areas were among those that came to follow Mahdiyya.

The lines of Umarian succession to authority in Kano Province (Hadejia) have been dynastic, and the Umarian community has come to be associated primarily with those who had some kin or disciple relationship with Umar. The link that Umar represents with the Jihad leadership, however, has been of major importance to the twentieth century legitimization of a "northern religious community" composed of both Tijaniyya and Qadiriyya. 

Reference… Religion and political culture in Kano by Paden, John N. Publication date 1973. 




Thursday, December 9, 2021

FURYAN HADEJIA...

HADEJIA A YAU!

TARIHIN FURYAWA


1.0 JADAWALIN WANDA SUKA RIKE SARAUTAR

 1. Furya Sakaina

(1760 – 1804)

2. Furya Muhammad Tsangwai
(1804 - 1810)

3. Furya Muhammad Ganuwa
 (1810 – 1856)

4. Furya Muhammad Babaru
 (1856 – 1860)

5. Furya Abubakar Sadik (1860 - 1906)

6. Furya Muhd Sani Babale (1906 - 1940)

7. Furya Muhd Tukur (1940 - 1946)

8. Furya Usman Kunkun (1946 - 1950)

9. Furya Muhd Mustapha (1950 - 1958)

10. Furya Abdullahi Tukur (1958 - 1997) 

11. Furya Muhd Danyaro (1997 - 2020). 

12. Furya Abdullahi Muhd (2020 to date).

2.0 TARIHI DA ASALIN FURYAWA

Asalin Furyawa fulani ne na kasar Borno wato Fulata Borno, ance mutanen kasar Machina ne wadda take Jihar Yobe a yanzu, mutane ne wanda suka kware a yaki sosai. Dalilin da yasa suka yiwo kaura daga inda suke shine, shugabansu wanda akafi sani da Sakaina dan Sarki ne bayan rasuwar mahaifinsa ya nemi sarauta a maimakon a bashi sai aka bawa kaninsa, a sakamakon haka ya debi magoya bayansa suka dawo wani gari da ake cewa Rinde. Furya tare da wani bufulatani ana ce masa Gurunde (shima da Jama’arsa) sune fulanin farko da suka fara zama a Rinde kuma Furya shine shugabansu wato ma’ana Furya Sakaina shine ya kafa garin Rinde shine kuma kamar Sarkin su a wannan lokacin.

Bayan rasuwar sarki Umaru Furyawa sun baro Rinde sun dawo Hadejia ta yau. A sakamakon gayyata da Sambo yayi musu bayan ya gaji dan uwansa Umaru a sarauta sun kafa gidansu ko unguwarsu dab da ganuwar Hadejia ta gabas kuma ana kiran wajen da unguwar Furya a yanzu kuma ‘Yan koli. 


Hakazalika, akwai ahali da ‘yayan ‘yanuwan Furya da suka rungumi sana’ar yaki bayan barinsu kasar Machina, shahararre a cikinsu shine Dan Furya wanda ya taya sarkin Gumel Habu Nakata yaki a garin kanyar maikaho ya kori shararren mayakin nan wato Danwaire. Daga baya sarkin Gumel ya bashi sarautar garin magajiya ta kasar Gumel a yanzu haka akwai hakimi da ake kira dan Furya a Gumel. Bayan nan Dan Furya ya koma Kano wajen sarkin Kano Alu yaci gaba da tayashi yaki, shima ya nadashi sarauta a garin Ringim bayan ya mutu dansa Musa ya gajeshi. A yanzu haka ana kiran dagacin Katutu ta garin Ringim da Dan-Furya, hakazalika akwai sunan unguwa Dan Furya House a Katutu Primary School Ringim.

         3.0 DANGANTAKAR FURYAWA           DA GIDAN SARAUTAR FULANIN HADEJIA

Lokacin da Umaru ya baro dan uwansa Sambo a Taurako (Digimsa) sai yayi yamma bai zame ko’ina ba sai Rinde. Furya da Gurunde sune shuwagabannin garin wato manyan Rinde sune suka bashi gida a tsakaninsu wato kowannesu ya matsa shi kuma yayi gida a tsakiyarsu. Daganan ya koma wurin Sambo ya dauko matarsa tare da shanunsa da sauran dabbobi.

Lokacin da Umaru ya kira sauran ‘yan uwansa Fulani yayi musu maganar kaiwa caffa ga Shehu Usman Danfodia sai suka nuna masa suna tsoron wulakancin sarkin Auyo Jibrin Uban Nalara, bugu da kari kuma sun shagalta da sha’anin kiwon shanunsu da sauran dabbobi. Asakamakon haka Umaru yace musu to ni zanyi aike wajen Shehu.

Umaru ya tura mutum shida Sokoto wajen Shehu Usman Danfodio, mutanen sun hada da: (1) Furya (Shugaban tawaga) (2) Gurunde  (3) Zatanku (Bawansa ne) sai kuma sauran Rindawa mutum uku wanda ba’a fadi sunansu ba.

Bayan sunje sun isar da sakon Umaru wajen Shehu sai Shehu yace na karbi caffarsa saboda haka ga tuta kukai masa. Ya kuma ce su fada masa idan yaje kowane gari ya daga tutar da ikon Allah zasu yarda dashi su kuma bishi. Da suka dawo daga Sokoto suka zo da sakonnan na Shehu ga Umaru. Sai Umaru ya sake tara Fulani yace dasu “Ga Furya da Gurunde da zatanku da mutum uku mutanen gari dana aikesu wurin Shehu sun dawo amma sunzo mini da tutar Musulunci” Bayan ya fada musu sakon Shehu daganan suka fara fita Jihadi zuwa makwabtan garuruwa kamarsu Akurya, Asuwari, Abartayin, Tashena da dai sauransu duka tare da Furya, Rindawa da sauran Fulani ‘yan uwansa.

Bayan rasuwar sarkin Fulani Umaru sai aka aikawa Shehu labarin rasuwar. Shehu Usman ya turo wazirin Sokoto domin yazo yayi ta’aziyya ya kuma nada sabon sarki. Lokacin da yazo ya sauka ne a Rinde garin da sarki Fulani Umaru yake zaune. Fulani suka taru waziri yayi musu ta’aziyya amma a lokacin Sambo bai samu labarin zuwan waziri ba yanacan Mairakumi inda gonarsa take.

Da waziri ya kwana bakwai sai yace wa su Furya (Rindawa) a aikawa Fulani suzo don muyi shawara dasu akan wanda za’a zaba ya zama shugaba (wato sarki). Bayan duka sun hallara sai furya da jama’arsa suka lura Sambo kanin Umaru baya cikin wadannan manyan fulanin, kuma ba’a kula a kirashi bama, saboda haka cikin dare sai Furya, Gurunde da mutum biyu suka tafi wurin Sambo a sirrance suka ce masa yazo su tafi Rinde saboda anyi baki daga Sokoto, sai Sambo yace musu “mezanyi idan naje?” suka dai matsa masa suka kuma nuna masa rashin jin dadinsu kasancewarsa baya wajen, ganin ransu ya sosu shine ya amince ya biyosu Rinde, da isowarsu garin suka shiga gidajensu ta kusfa (A boye) saboda basa son agane sune suka kirashi, shi kuma ya biyo ta kofar gari ya iske su waziri da sauran manyan Fulani a rumfar kofar masallaci.

Da zuwansa sai Jimagara (Kawun Sambo) yace da waziri, “To ga wanda muke jira yazo, amma fa bamu aika masa yazo ba amma gashi Allah ya kawoshi” (saboda basu san su Furyane suka kirashi ba). Da jin haka sai waziri ya fidda takardu na kuri’a guda goma wanda Shehu ya bashi saboda gudun rigima. A takaice dai Allah ya taimaki Sambo yaci kuri’ar zama sarki, waziri kuma ya koma Sokoto yayiwa Shehu Usman bayani.

3.1 DANGANTAKAR AURATAYYA

Haka zalika, tarihi ya nuna akwai dangantakar auratayya tsakanin Umaru da Furyawa. Furya Tsangwai ya aurawa sarkin Fulani Umaru ‘Yarsa kuma sun haifi diya mace tare wadda aka sa mata suna Gabdo. Ita kuma Gabdo ta auri sarki Garko dan Sambo sun haifi ‘ya wadda ake kira da Maryam (Furatu).


4.0 ASALIN SARAUTAR FURYA DA AIKIN SU A MASARAUTAR HADEJIA

Kalmar Furya sunane na wasu Ahali ko haula a kasar Machina (kamar yadda bayani ya gabata). Sunan Furya ya zama sarauta a kasar Hadejia tun lokacin da Furya Tsangwai kanin Sakaina ya nada sarkin Fulani Umaru sarki bayan Shehu Usman Danfodio ya basu tutar musulunci da Jahadi. An zabi Furya ya nada sarki Umaru sakamkon shine shugaba a Rinde bugu da kari shine ya jagoranci tafiya Sokoto karbo tuta wajen Shehu Usman Danfodio. Tun daga wannan lokaci zuri’ar gidan Furya suke nada sarki a Hadejia harya zuwa yau. A sakamakon haka ake kiran duk wani mai nada sarki a Hadejia Furya. Haka zalika bayan sarki Sambo ya hau gadon sarauta ya sake tabbatar da sarautar furya ma’ana furya tana daya daga cikin manya-manyan sarautu tara da ya fara yi, sarautun kuwa sune:

1.     Sarkin Auyo (Yusufu, Kaninsa)

2.     Garko (Ciroma, Babban Dansa)

3.     Furya (Rindawa)

4.     Galadima (Mangawa)

5.     Madaki (Fulanin Sambo)

6.     Ma’aji (Fulanin Damagaran)

7.     Maidala (Auyokawa)

8.     Sarkin Yara (Fulanin Sambo)

9.     Sarkin Wanzamai (Auyokawa)

A takaice aikin Furyawa a masarautar Hadejia shine nada sabon sarki da hakimansa idan bukatar hakan ta taso, a sabili da haka ake yiwa Furya kirari da “Duk Mainan (Dan sarki) daka dafa kansa ya taka gacci”. Yana da kyau a sani, a tarihin Hadejia Furya shine kadai wanda sarki yake nadawa da hannunsa.

Bayan haka, yaki yana daga cikin aikin Furyawa a kasar Hadejia, sune akan gaba idan yaki ya tashi sabili da kasancewarsu jarumai kuma yakin sana’arsu ce, a sakamakon haka ake musu kirari da “Bahago tausa dama, jinni tsar Bahago”.

5.0 JADAWALIN MUTANEN DA SUKA RIKE SARAUTAR FURYA DA SHEKARUN DA SUKA YI

Furya Sakaina shine ya fara yin sarki ko shugaba a garin Rinde, a kiyasi ya kafa garin Rinde wajajen shekarar 1740 wanda sun zauna ne a karkashin mulkin sarkin Auyo. Bayan rasuwarsa sai Furya Muhammadu Tsangwai ya karba, shine Furya na farko daya fara nada sarki Umaru a matsayin sarkin Fulani bayan sun karbo tutar musulunci daga wajen Shehu Usman Danfodio, ya fara sarauta daga (1804 – 1810).

Bayan rasuwarsa sai Dansa Muhammadu Ganuwa ya gajeshi a shekarar (1810 – 1856) Furya Muhammadu ya samu lakabin Ganuwa ne a sakamakon jagorantar ginin ganuwar Hadejia da yayi. Sarki Sambo ya dora masa alhakin kula da aikin ginin, ance shine mai alhakin yankawa kowane gida iya ginin da zasu yi sannan ya kula da aikin. Haka zalika tarihi ya nuna furya Ganuwa yayi fice a fagen jarumta da sanin dabarar yaki kasancewarsa barde, ya halarci yaki da dama tare da sarki Sambo. Hakazalika ya nuna bajinta da kwarewa a lokacin da akayi yaki da Katagum a zamanin sarkin Hadejia Buhari, sabili da irin bajintar daya nuna sarki Buhari yayi masa kyautar Gandun noma a gabas da Hadejia wanda ya fara tun daga kofar gari ta gabas har zuwa tandanu, ana kiran gandun Gudarin Furya.

Bayan rasuwar furya Ganuwa sai dansa Muhammadu Babaru (Furya Babaru) ya gajeshi daga shekarar (1856 – 1860). Bayan rasuwarsa ne ‘ya’yansa Guda Biyar suka gajeshi daya-bayan-daya, kuma ya rasune kafin zuwan turawa.

Babban dansa Abubakar Sadiq (Furya Sadi) ya gajeshi a shekarar (1860 – 1906) ya kwashe shekara arba’in da shida yana sarautar Furya yayi mutuwar shahada tare da sarki Muhammadu Maishahada a yakin turawa da akayi a 1906. An kawo sunansa a wakar da akayi ta shahadar Hadejiawa wadda Alhaji Ibrahim Katala ya rubuta a baiti na 32 inda yake cewa “Furyan Hadejia shi da Bori na Salihu kofar gabas suka fadi nan aka cim musu”.

Bayan shahadarsa sai kaninsa Furya Muhd Sani Babale ya gajeshi daga shekarar (1906 – 1940). Bayan rasuwar furya Babale sai Dan’uwansa Furya Muhd Tukur (Furya Tukur) ya gajeshi daga shekarar (1940 – 1949).

Bayan rasuwar furya Tukur sai kaninsa Usman Kunkun ya gajeshi ya fara daga shekara ta (1949 – 1950). Bayan rasuwar Furya Kunkun sai aka bawa kaninsa Muhd Mustafa sarauta, ya fara daga shekara ta (1950 – 1958).

Bayan rasuwar Furya Muntsafa sai aka nada dan dan uwansa Furya Abdullahi Tukur sarauta (Furya Tumalle). Ya fara sarauta daga shekara ta (1958 – 1997). Bayan rasuwar Furya Abdullahi sai dansa Furya Muhammadu Abdullahi Danyaro ya gajeshi a shekara ta 1997 wanda shine akan gadon sarauta a yanzu.

A takaice aikin Furya a masarautar Hadejia shine nada sabon sarki da kuma hakimansa. Kuma yanada kyau a sani, a tarihin Hadejia Furya shi kadaine wanda sarki yake nadawa da hannunsa idan sarautar ta fado. 

Ismaila Muhammad Danyaro. 

References

1.     Tarihin (Fulanin) Hadejia by Ma’aji Amar for Hadejia N.A (1956).

2.     Kasar Hadejia by Muhammad Ilallah for Hadejia N.A (1956)

3.     Three Nigerian Emirates: A study of oral history. (Victor N. Low, 1965 P. 134).

4.     Verbal interview with Furya Abdu, Baba Ubali, Baban Juji and many more among elders of the family.

5.     Kano daga Garko “Tarihin sarautar Kano” by Muhd Uba Adamu, Najib Hussain Adamu, Prof. Muhd Sa’idu Gusau.

6.     Kano history and culture bureau Archive.