5. Furya Abubakar Sadik (1860 - 1906)
6. Furya Muhd Sani Babale (1906 - 1940)
7. Furya Muhd Tukur (1940 - 1946)
8. Furya Usman Kunkun (1946 - 1950)
9. Furya Muhd Mustapha (1950 - 1958)
10. Furya Abdullahi Tukur (1958 - 1997)
11. Furya Muhd Danyaro (1997 - 2020).
12. Furya Abdullahi Muhd (2020 to date).
Asalin
Furyawa fulani ne na kasar Borno wato Fulata Borno, ance mutanen kasar Machina
ne wadda take Jihar Yobe a yanzu, mutane ne wanda suka kware a yaki sosai.
Dalilin da yasa suka yiwo kaura daga inda suke shine, shugabansu wanda akafi
sani da Sakaina dan Sarki ne bayan rasuwar mahaifinsa ya nemi sarauta a
maimakon a bashi sai aka bawa kaninsa, a sakamakon haka ya debi magoya bayansa
suka dawo wani gari da ake cewa Rinde. Furya tare da wani bufulatani ana ce masa
Gurunde (shima da Jama’arsa) sune fulanin farko da suka fara zama a Rinde kuma
Furya shine shugabansu wato ma’ana Furya Sakaina shine ya kafa garin Rinde
shine kuma kamar Sarkin su a wannan lokacin.
Bayan
rasuwar sarki Umaru Furyawa sun baro Rinde sun dawo Hadejia ta yau. A sakamakon
gayyata da Sambo yayi musu bayan ya gaji dan uwansa Umaru a sarauta sun kafa
gidansu ko unguwarsu dab da ganuwar Hadejia ta gabas kuma ana kiran wajen da
unguwar Furya a yanzu kuma ‘Yan koli.
Hakazalika,
akwai ahali da ‘yayan ‘yanuwan Furya da suka rungumi sana’ar yaki bayan barinsu
kasar Machina, shahararre a cikinsu shine Dan Furya wanda ya taya sarkin Gumel Habu
Nakata yaki a garin kanyar maikaho ya kori shararren mayakin nan wato Danwaire.
Daga baya sarkin Gumel ya bashi sarautar garin magajiya ta kasar Gumel a yanzu
haka akwai hakimi da ake kira dan Furya a Gumel. Bayan nan Dan Furya ya koma
Kano wajen sarkin Kano Alu yaci gaba da tayashi yaki, shima ya nadashi sarauta
a garin Ringim bayan ya mutu dansa Musa ya gajeshi. A yanzu haka ana kiran
dagacin Katutu ta garin Ringim da Dan-Furya, hakazalika akwai sunan unguwa Dan
Furya House a Katutu Primary School Ringim.
3.0 DANGANTAKAR FURYAWA DA GIDAN SARAUTAR FULANIN HADEJIA
Lokacin
da Umaru ya baro dan uwansa Sambo a Taurako (Digimsa) sai yayi yamma bai zame
ko’ina ba sai Rinde. Furya da Gurunde sune shuwagabannin garin wato manyan
Rinde sune suka bashi gida a tsakaninsu wato kowannesu ya matsa shi kuma yayi
gida a tsakiyarsu. Daganan ya koma wurin Sambo ya dauko matarsa tare da
shanunsa da sauran dabbobi.
Lokacin
da Umaru ya kira sauran ‘yan uwansa Fulani yayi musu maganar kaiwa caffa ga
Shehu Usman Danfodia sai suka nuna masa suna tsoron wulakancin sarkin Auyo
Jibrin Uban Nalara, bugu da kari kuma sun shagalta da sha’anin kiwon shanunsu
da sauran dabbobi. Asakamakon haka Umaru yace musu to ni zanyi aike wajen
Shehu.
Umaru
ya tura mutum shida Sokoto wajen Shehu Usman Danfodio, mutanen sun hada da: (1) Furya (Shugaban tawaga) (2)
Gurunde (3) Zatanku (Bawansa ne) sai
kuma sauran Rindawa mutum uku wanda ba’a fadi sunansu ba.
Bayan
sunje sun isar da sakon Umaru wajen Shehu sai Shehu yace na karbi caffarsa
saboda haka ga tuta kukai masa. Ya kuma ce su fada masa idan yaje kowane gari ya
daga tutar da ikon Allah zasu yarda dashi su kuma bishi. Da suka dawo daga
Sokoto suka zo da sakonnan na Shehu ga Umaru. Sai Umaru ya sake tara Fulani
yace dasu “Ga Furya da Gurunde da
zatanku da mutum uku mutanen gari dana aikesu wurin Shehu sun dawo amma sunzo
mini da tutar Musulunci” Bayan ya fada musu sakon Shehu daganan suka fara
fita Jihadi zuwa makwabtan garuruwa kamarsu Akurya, Asuwari, Abartayin, Tashena
da dai sauransu duka tare da Furya, Rindawa da sauran Fulani ‘yan uwansa.
Bayan
rasuwar sarkin Fulani Umaru sai aka aikawa Shehu labarin rasuwar. Shehu Usman
ya turo wazirin Sokoto domin yazo yayi ta’aziyya ya kuma nada sabon sarki.
Lokacin da yazo ya sauka ne a Rinde garin da sarki Fulani Umaru yake zaune.
Fulani suka taru waziri yayi musu ta’aziyya amma a lokacin Sambo bai samu
labarin zuwan waziri ba yanacan Mairakumi inda gonarsa take.
Da
waziri ya kwana bakwai sai yace wa su Furya (Rindawa) a aikawa Fulani suzo don
muyi shawara dasu akan wanda za’a zaba ya zama shugaba (wato sarki). Bayan duka
sun hallara sai furya da jama’arsa suka lura Sambo kanin Umaru baya cikin
wadannan manyan fulanin, kuma ba’a kula a kirashi bama, saboda haka cikin dare
sai Furya, Gurunde da mutum biyu suka tafi wurin Sambo a sirrance suka ce masa
yazo su tafi Rinde saboda anyi baki daga Sokoto, sai Sambo yace musu “mezanyi
idan naje?” suka dai matsa masa suka kuma nuna masa rashin jin dadinsu kasancewarsa
baya wajen, ganin ransu ya sosu shine ya amince ya biyosu Rinde, da isowarsu
garin suka shiga gidajensu ta kusfa (A boye) saboda basa son agane sune suka
kirashi, shi kuma ya biyo ta kofar gari ya iske su waziri da sauran manyan
Fulani a rumfar kofar masallaci.
Da
zuwansa sai Jimagara (Kawun Sambo) yace da waziri, “To ga wanda muke jira yazo,
amma fa bamu aika masa yazo ba amma gashi Allah ya kawoshi” (saboda basu san su
Furyane suka kirashi ba). Da jin haka sai waziri ya fidda takardu na kuri’a guda
goma wanda Shehu ya bashi saboda gudun rigima. A takaice dai Allah ya taimaki
Sambo yaci kuri’ar zama sarki, waziri kuma ya koma Sokoto yayiwa Shehu Usman
bayani.
3.1 DANGANTAKAR
AURATAYYA
Haka
zalika, tarihi ya nuna akwai dangantakar auratayya tsakanin Umaru da Furyawa.
Furya Tsangwai ya aurawa sarkin Fulani Umaru ‘Yarsa kuma sun haifi diya mace
tare wadda aka sa mata suna Gabdo. Ita kuma Gabdo ta auri sarki Garko dan Sambo
sun haifi ‘ya wadda ake kira da Maryam (Furatu).
4.0 ASALIN SARAUTAR
FURYA DA AIKIN SU A MASARAUTAR HADEJIA
Kalmar
Furya sunane na wasu Ahali ko haula a kasar Machina (kamar yadda bayani ya
gabata). Sunan Furya ya zama sarauta a kasar Hadejia tun lokacin da Furya
Tsangwai kanin Sakaina ya nada sarkin Fulani Umaru sarki bayan Shehu Usman
Danfodio ya basu tutar musulunci da Jahadi. An zabi Furya ya nada sarki Umaru
sakamkon shine shugaba a Rinde bugu da kari shine ya jagoranci tafiya Sokoto
karbo tuta wajen Shehu Usman Danfodio. Tun daga wannan lokaci zuri’ar gidan
Furya suke nada sarki a Hadejia harya zuwa yau. A sakamakon haka ake kiran duk
wani mai nada sarki a Hadejia Furya. Haka zalika bayan sarki Sambo ya hau gadon
sarauta ya sake tabbatar da sarautar furya ma’ana furya tana daya daga cikin
manya-manyan sarautu tara da ya fara yi, sarautun kuwa sune:
1. Sarkin
Auyo (Yusufu, Kaninsa)
2. Garko
(Ciroma, Babban Dansa)
3. Furya
(Rindawa)
4. Galadima
(Mangawa)
5. Madaki
(Fulanin Sambo)
6. Ma’aji
(Fulanin Damagaran)
7. Maidala
(Auyokawa)
8. Sarkin
Yara (Fulanin Sambo)
9. Sarkin
Wanzamai (Auyokawa)
A
takaice aikin Furyawa a masarautar Hadejia shine nada sabon sarki da hakimansa
idan bukatar hakan ta taso, a sabili da haka ake yiwa Furya kirari da “Duk Mainan (Dan sarki) daka dafa kansa ya
taka gacci”. Yana da kyau a sani, a tarihin Hadejia Furya shine kadai wanda
sarki yake nadawa da hannunsa.
Bayan
haka, yaki yana daga cikin aikin Furyawa a kasar Hadejia, sune akan gaba idan
yaki ya tashi sabili da kasancewarsu jarumai kuma yakin sana’arsu ce, a
sakamakon haka ake musu kirari da “Bahago
tausa dama, jinni tsar Bahago”.
5.0 JADAWALIN MUTANEN
DA SUKA RIKE SARAUTAR FURYA DA SHEKARUN DA SUKA YI
Furya
Sakaina shine ya fara yin sarki ko shugaba a garin Rinde, a kiyasi ya kafa
garin Rinde wajajen shekarar 1740 wanda sun zauna ne a karkashin mulkin sarkin
Auyo. Bayan rasuwarsa sai Furya Muhammadu Tsangwai ya karba, shine Furya na
farko daya fara nada sarki Umaru a matsayin sarkin Fulani bayan sun karbo tutar
musulunci daga wajen Shehu Usman Danfodio, ya fara sarauta daga (1804 – 1810).
Bayan
rasuwarsa sai Dansa Muhammadu Ganuwa ya gajeshi a shekarar (1810 – 1856) Furya
Muhammadu ya samu lakabin Ganuwa ne a sakamakon jagorantar ginin ganuwar
Hadejia da yayi. Sarki Sambo ya dora masa alhakin kula da aikin ginin, ance
shine mai alhakin yankawa kowane gida iya ginin da zasu yi sannan ya kula da
aikin. Haka zalika tarihi ya nuna furya Ganuwa yayi fice a fagen jarumta da
sanin dabarar yaki kasancewarsa barde, ya halarci yaki da dama tare da sarki
Sambo. Hakazalika ya nuna bajinta da kwarewa a lokacin da akayi yaki da Katagum
a zamanin sarkin Hadejia Buhari, sabili da irin bajintar daya nuna sarki Buhari
yayi masa kyautar Gandun noma a gabas da Hadejia wanda ya fara tun daga kofar
gari ta gabas har zuwa tandanu, ana kiran gandun Gudarin Furya.
Bayan
rasuwar furya Ganuwa sai dansa Muhammadu Babaru (Furya Babaru) ya gajeshi daga
shekarar (1856 – 1860). Bayan rasuwarsa ne ‘ya’yansa Guda Biyar suka gajeshi
daya-bayan-daya, kuma ya rasune kafin zuwan turawa.
Babban
dansa Abubakar Sadiq (Furya Sadi) ya gajeshi a shekarar (1860 – 1906) ya kwashe
shekara arba’in da shida yana sarautar Furya yayi mutuwar shahada tare da sarki
Muhammadu Maishahada a yakin turawa da akayi a 1906. An kawo sunansa a wakar da
akayi ta shahadar Hadejiawa wadda Alhaji Ibrahim Katala ya rubuta a baiti na 32
inda yake cewa “Furyan Hadejia shi da
Bori na Salihu kofar gabas suka fadi nan aka cim musu”.
Bayan
shahadarsa sai kaninsa Furya Muhd Sani Babale ya gajeshi daga shekarar (1906 –
1940). Bayan rasuwar furya Babale sai Dan’uwansa Furya Muhd Tukur (Furya Tukur)
ya gajeshi daga shekarar (1940 – 1949).
Bayan
rasuwar furya Tukur sai kaninsa Usman Kunkun ya gajeshi ya fara daga shekara ta
(1949 – 1950). Bayan rasuwar Furya Kunkun sai aka bawa kaninsa Muhd Mustafa sarauta,
ya fara daga shekara ta (1950 – 1958).
Bayan
rasuwar Furya Muntsafa sai aka nada dan dan uwansa Furya Abdullahi Tukur sarauta
(Furya Tumalle). Ya fara sarauta daga shekara ta (1958 – 1997). Bayan rasuwar
Furya Abdullahi sai dansa Furya Muhammadu Abdullahi Danyaro ya gajeshi a
shekara ta 1997 wanda shine akan gadon sarauta a yanzu.
A
takaice aikin Furya a masarautar Hadejia shine nada sabon sarki da kuma
hakimansa. Kuma yanada kyau a sani, a tarihin Hadejia Furya shi kadaine wanda
sarki yake nadawa da hannunsa idan sarautar ta fado.
Ismaila Muhammad Danyaro.
References
1. Tarihin
(Fulanin) Hadejia by Ma’aji Amar for Hadejia N.A (1956).
2. Kasar
Hadejia by Muhammad Ilallah for Hadejia N.A (1956)
3. Three
Nigerian Emirates: A study of oral history. (Victor N. Low, 1965 P. 134).
4. Verbal
interview with Furya Abdu, Baba Ubali, Baban Juji and many more among elders of
the family.
5. Kano
daga Garko “Tarihin sarautar Kano” by Muhd Uba Adamu, Najib Hussain Adamu,
Prof. Muhd Sa’idu Gusau.
6. Kano
history and culture bureau Archive.