"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, September 20, 2025

SARAUTAR BARDE A HADEJIA.

HADEJIA A YAU!


Sarautar Barde, sarautar ce ta Habe wacce Fulani suka gada bayan Jihadin Shehu Usmanu Danfodiyo, kuma sarauta ce ta Mayaka ko Jarumai. Ma'anar sarautar Barde ita ce, duk lokacin da sarki zai yi wata tafiya mai nisa, Barde zai kasance a gaba har sai ya tabbatar da masaukin Sarki akwai kyakkyawan tsaro a wurin kafin Sarki ya iso ya sauka. Kuma yana binciken inda abokan gaba suke lokacin yaki sannan yana binciken inda abokan yaki suka buya don kawo harin samame. 

UNGUWAR TUDUN BARDE HADEJIA 1808 Ca

Wannan unguwa mai suna a sama, (Unguwar Tudun Barde) ta samo sunan ta ne daga Barde  Risku shugabanr rundunar yakin Hadejia, shi ne  ya fara sarautar Barde a Haɗejiya.

Barde Risku mutumin Takoko ne ta karamar hukumar Mallam Madori shi ne wanda mahaifin sa ya hada shi da Sarki Sambo lokacin jihadi bisa dalilin gayyatar mahaifin da Sarki Sambo yayi, yana da yar'uwa wanda Sarki Sambo ya aura wato DIBI mahaifiyar Sarki Buhari.


Barde Risku shi ne wanda da Sultan ya mikawa Sarki Sambo tuta shi kuma ya mikawa Risku, wannan tasa a lokacin sa  Tuta da shemar da ake kafawa  lokacin yaki suke karkashin kulawar sa.

Unguwar Tudun Barde tana Kudu masu yamma da fadar Haɗejia daga cikin ta aka samuTudun Mabudi koda yake babu unguwa Tudun Mabudi a hukumance.

Barde Risku yana  da da guda  daya da ya tabbata a tarihi wato Barde Fannami.
Kamar yadda tarihi na kunne ya girmi kaka ya nuna, bayan Sarkin Hadejia Sambo ya shiga garin Hadejia duka qasa ta zama tasa sai ya tasamma gyare gyare tare da nada hakimai da zasu taya shi jagoranci kasar Hadejia. Sambo ya nada hakimai daga kowanne bangare na kabilun da suke kasar Hadejia, wannan tasa ya nada Risku daga bangaren Kanuri. Daga wannan lokacin zuwa yau ga jerin mutanen da suka yi Sarautar Barde....
   1. Barde Risku 
   2. Barde Fannami 
   3. Barde Dandaku 
   4. Barde Zangoli
   5. Barde Ibrahim Hassan

Babangida Mukhtar Hadejia. 

Wednesday, July 23, 2025

HISTORY OF GAMAWA TOWN.


HADEJIA A YAU!

GAMAWA... 
The History of this District consists in the history of isolated towns, of which the most important is Gamawa owing to the fighting, which took place between Katagum and Sarkin Gamawa Magaji in the time of Sarkin Katagum Abdu. Makawa is also important as being formerly the stepping stone for 'yan Sarki to high Sarautas. A short account of the eldest and most important towns is given below.

A. Gamawa. There are three sites to this town of which the oldest is Gamawa Gujinbara {North east of present town} it is said to have founded by a Habe named Gamua who came from Kun near Lake Chad.

There are five Habe Chiefs, whose name are known.
1. Gamua
2. Bidboni
3. Mai baloneye
4. Warjabba
5. Mai karo

In the time of Mai karo one Hardo Yero came from Bagirmi and settled at Gurbiri East of Koron. When Mallam Zaki captured Tashena, he made his submission and asked for a town to settle in. Mallam Zaki gave him Gamawa but before occupying it he died and his son Ibrahim Kura with the aid of Mallam Zaki captured Gamawa and killed Mai karo. Ibrahim Kura lived in the town for five years and then died. Adamu or Gorko, his brother succeeded him and lived for twenty nine years in the place. In his time Shehu Laminu captured the town and Gorko fled to Kirehabi, where he died. In this engagement Shehu Laminu killed about 200 men and captured a great many cattle. He however only stayed for 24 days and then returned to Bornu. 
For two years Gamua was unoccupied. Then Sarkin Katagum Dan Kauwa gave the place to Sarki Atawa, who belonged to the same family as the former Chiefs. He was the Hardo Manuwa and cousin to Gorko. He reigned for six years and was then removed from the Sarauta by Dan Kauwa, because he was too old to keep authority. He went to Korori and was there for one year before his death. He was succeeded by Dan Baba, son of Liman Adandaya, brother of Mallam Zaki, who after a brief Sarauta of five years was turned out by Sarkin Katagum Abdurrahman for depopulating his town. He then went to live in Katagum. He was succeeded by Ibrahim, son of Gorko who in his turn was removed from Sarauta by Sarkin Katagum Abdulkadir after seven years for the same reason as Dan Baba. During these years raide were made continuously by the slaves of the Shehu and so during the reign of Ibrahim they removed to the recent site known as Gamawa Kori. After Ibrahim, Suruma Meddi, a distant relation was given the Sarauta but after a reign of only seven month he died.

Abba Shua, son of Balarabe and Mairam, grandson of Dan Kauwa succeeded but after a reign of three years he was driven out of Gamawa Kori by Danbabuje, a Bedde Chief and fled to Shira. Ibrahim was then restored Kadr and was Chief fo twenty four years but was again turn out by Haji for permitting highway robbery and murder on the road to his town. During this time Gamawa Kori was evacuated and they removed to the present site Gamawa Bureri owing to serenity of water. He was succeeded by Magaji son of Alkali Adamu of Keffi. In whose reign the war with Katagum arose. 

There was a further reason for this war a full account of which has been given in the report on the Galadima District, of which I was not informed before. It would seem that the Sarkin Musulmi sent to Sarkin Katagum Abdu, calling him in to Sokoto. He was unable to go and sent Waziri Saidu in his place. Sarkin Musulmi then wrote to all Chiefs under Sarkin Katagum ordering them to break from their allegiance, as he had refused to obey his orders. He wrote to Sarkin Katagum and told him he would not allow him even to drink the water outside Katagum town, called Kabajam, or the Sarkin Ruwa, if he did not come in to Sokoto. Yariman Chinade was to be made Wakili of the Emirate. The Sarkis in obedience to orders refused to follow Katagum. 

Sarkin Gamawa at this time was at the height of his power and had collected horses and guns from Rabeh Mamadu son of Sarkin Katagum Abdu, hearing of this conflagration, collected a force at Sokwa, of which he was then Sarki and set out to attack Sarkin Gamawa. Yerima Chinade had advanced as far as Gadia and reinforcements had came in from the other Chiefs. Mamadu drove them all away at Bagalu, west of the site of the new station at Gadia and then went on to Korori where he defeated and killing Sarkin Gamawa.

After Magaji's death Gorko, grandson of Atawa the father of the present Chief, was given the Sarauta and was succeeded this year by his son Ibrahim. There are no less than five walls in the present town of Gamawa, all of which were filled with people in the time of Magaji; since his time the town has been depleted and is now comparatively small.

2. KEFFI..... 

Archive Eap535/blu. 






Thursday, July 17, 2025

END OF TENURE AS PROVOST JICORAS BABURA

HADEJIA A YAU!


On Tuesday, 15th July 2021, the then Jigawa State Governor appointed me as Provost of Jigawa College of Remedial Advanced Studies, Babura, for a first term of 4 years, renewable for a maximum of 8 years as enshrined in the college's law.

 Alhamdulillah, I announce my departure and handing over of my position as PROVOST with the successful 5 year Accreditation of the 10 ND Programs I introduced in the college after been appointed as provost, and a Historic First Certification Exams ever conducted in Jigawa State for 2 National Diploma on Health Science Courses (ND Public Health Technology and ND Epidemiology & Desease Control Technology) with over 120 external candidates from within and outside Jigawa State. This marks the end of my First Tenure of four (4) years as the Pioneer Provost of the College.


My special prayers and appreciation go to His Excellency Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, Mni, MON, the Former Governor of Jigawa State and Minister of Defence of the Federal Republic of Nigeria, who found me worthy and appointed me to head this wonderful institution. This is after several attempts to include me in his government.

A special thanks go to my Leaders in struggle, the Former and the Present Chairmen of our great association, “HADEJIA INA MAFITA INITIATIVE”, in persons of DR ISAH BILLAMI and SIR. Dr Baidi Mohammed Gajo Yalleman and the entire Mafita family, who not only supported me but also made this wonderful journey a success and a reality. 


I also thank the pioneer Chairman and members of JICORAS Governing Council, Professor H.I. Bayero. And the present Governing Council of Hajiya Gaji Bello Hussain for their support, cooperation and giant efforts to uplift JICORAS in achieving academic excellence.

My Colleagues, the Management and other teaching staff of JICORAS, especially my former Registrar, Dr Rabiu Sale Kazaure, and the present Acting Registrar, and the entire management.  My appreciation also goes to my Deputy and Ag. Provost whom I handed over the affairs of the college to in person of Malam Bashir Ubale Gumel, who is always with me in every decision (soft or hard) I took in ensuring high academic standards and quality assurance in the system. 
I pray and hope that the person who will succeed me will do better than I to uplift the image and academic standard of the college.   I learned a lot, heard a lot, and saw a lot during these short but important and memorable four years in office as provost of this institution.

I thank the entire Babura Community and the CBO, Movement for Better Babura, who always supported me with positive advice as a community-based organization.

I always believed in the saying of the Premier of the Defunct Northern Region, Sir Ahmadu Bello, Sardauna, on the civil service
BA A IYAWA!
BAA GAMAWA!!
BASU YABAWA!!!
Dr. Hussaini Shehu
Former Provost JICORAS, Babura and Vice Chairman, Hadejia Ina Mafita Initiative

Wednesday, June 4, 2025

A FADAWA HADEJIYAWA KASUWA. TARIHIN KAFUWAR GANDUN BUNDUGOMA

HADEJIA A YAU!
TARIHIN KAFUWAR GANDUN BUNDUGOMA. 

Daga Umar Yusuf Da'awa 

A Zamanin Mulkin Sarkin Haɗejiya Haru Bubba wadda ya yi mulki a shekarar 1865-1885 ne, kasuwa ta mamaye Kudancin Haɗejiya, Ma'ana ɓagaren Kudu da garin Haɗejiya. Kasuwa ta kafu jama'a sun shigo garin Haɗejiya, kama daga Turawa (Turkiyya) Larabawa dama Hausawammu na gida da na wajen kasar nan. 

Saboda shahara da Haɗejiya tayi na noman Gyaɗa da Auduga da Dawa da Gero dadai sauran su, wannan tasa jama'a suka shigo Haɗejiya daban daban. Haka aka yi ta kasuwanci a wannan yanki, har akwai lokacin da Jirgi yakan sauka a Haɗejiya mai sauƙar Ungulu na larabawa da Turawa a basu Auduga da gyaɗa, su kuma su kawo mana tufafin irin su Abaya da kayan mulki irin na gabas. Kasuwa tayi ƙarfi jama'a sun cika, sai ɓarayi suka fara ziyartar wannan kasuwa suna yin wasoso, har labari ya iskewa Sarki, nan take sarki ya tashi ɗaya daga cikin Fadawansa a bangaren 'Yan Baka wadda ake ƙira da Bundugoma, yace yaje ya sa ido ga yan kasuwa ya tabbatar sun yi saye da sayarwa lafiya babu tsoro. 

Bundugoma ya amsa umarnin sarki, in ya tafi tun Safe har yamma shi da yaran sa suna kula da 'yan kasuwa. Da yaga haka kawai sai ya tare wannan wuri gaba ɗaya da zama, ya share fili ya gina bukkar sa tare da yaran sa. Wannan tasa har yau ake ƙiran wannan wuri da Gandun Bundugoma. Bundugoma kuwa ana nufin mai Bindiga a yaren Manganci, domin shi Bamange ne. Kuma sune suke Sarautar Galadiman Bindiga a Hadejia. Kasuwa ta ci gaba da ci, kuma tafi cika ranar Lahadi saboda Baki suna zuwa ne ranar Asabat su kwana lahdi su ci kasuwa su wuce. 

A zamanin sarkin Hadejia Abdulkadir Turawa suka umarci a dawo da kasuwa yamma da gari don dacewa da zamani, sai kasuwa ta dawo duriyar yamma da gari wato Unguwar Rinde inda kasuwa take yanzu.

Friday, April 12, 2024

GOMBE EMIRATE.

HADEJIA A YAU!
GOMBE EMIRATE.. 


Gombe Emirate was the headquarters of the Emir of Gombe, who, like the Emir of Bauchi, was one of seven Fulani Emirs imposed on an existing Hausa ruling structure by the great 19th-century Fulani Islamic reformer, Uthman dan Fodio. Built as a new town in the 1920s, Gombe was systematically laid out on a grid pattern. The original site of Gombe town was at a place called Gombe Aba, 60 miles to the north on the River Gongola, but it had been condemned as unhealthy due to its proximity to a swamp and so an entirely new town had been constructed. The baked mud houses were large and well built.

Last Man In: The End of Empire in Northern Nigeria
by John Hare

Publication date 2013.

Gombe Emirate comprises an area of 5,114 square miles, with a population of 159,831. Something approaching one fifth of these are Fulane the Bolewa, Terawa and Beri-beri are, as in order mentioned, the next most important tribes numerically speaking. (Vide ' Tribes, Bauchi Province.") The Emirate lies in the great bend of the Gongola River, which bounds it north and east, while on the west it marches with the Bauchi Emirate and to the south abuts on the Tangale Hills. The area is mostly a flat low sandstone plateau, lacking in water, most of the population living near the Gongola River.

For purposes of administration the Emirate is divided into four districts, Gombe, Nafada, Ako and Dukul. The Emirate and divisional headquarters have been moved from Gombe to Nafada (population 7,000), on the Gongola River, which is navigable as far as Nafada from July to October for barges, from early June to end of October for canoes. Steam craft have reached Gombe, but the passage is dangerous. Other big towns are Duku, Tongo, Gadam, and Debba Habe.


Buba Yero, the first Emir of Gombe, was by birth a fulane of the Tara clan, who came from Dilara. His father sent him to Kukawa to study, but he was captured by the Kerre-Kerre on the way thither, and spent three years as a slave at Potiskum, On obtaining his liberty he journeyed to Sokoto and spent his early years in study under Othman dan Fodio. When the Jihad commenced he took part in the capture of Zanfara and was given a flag, authorising a Jihad amongst the pagan states, the Sarkin Musulmi, giving him precedence over Bauchi, Katagum, Katsina, Zau-Zau, Zanfara and Hadeija.

This campaign was concurrent with that waged by his powerful neighbour, Yakubu, Emir of Bauchi, with whom he came into conflict at Beri-beri where he was defeated. Yakubu refused to allow him to extend his dominion west of the Gongola. Buba Yero, therefore, extended his conquests to the River Benue and deputed a lieutenant to rule over Muri town and the southern dominions as his vassal. This lieutenant was, however, subsequently killed by Buba Yero for failing to render obedience, but his son and successor succeeded in throwing off the yoke of Gombe. To the east of the Gongola, Buba Yero subdued the country as far as Adamawa, and then turned his attention to the north. It is related that he made a joint campaign with Messau, resulting in the capture of Birnin Bornu. In after years the Emirs of Gombe and Messau were constant allies. After this he moved to Nafada, and undertook the pacification of the Fika Bole, but met with considerable opposition. Kalam was broken later.

In 1824 he made his camp at a Filane settlement, where he founded Gombe town, and he lived to enjoy the fruits of his conquests till the mature age of seventy-nine. However, a large number of pagans subsequently revolted and successfully threw off the Filane yoke.

Notes on the tribes, provinces, emirates and states of the northern provinces of Nigeria; by Temple, O.; Temple, Charles Lindsay, 1871. Publication date 1919.


Wednesday, May 31, 2023

TARIHIN SARKIN KANO ABDULLAHI BAYERO.

HADEJIA A YAU!


Abdullahi Bayero CBE CMG dan Muhammad Abbas (1881-1953) shi ne Sarki (Sarkin Kano ), wanda ke da hedikwata a Kano , Jihar Kano , Nijeriya daga 1926 zuwa 1953 . 

Sarki Abdullahi Bayero shi ne sarki na 53 a jerin sarakunan Kano kuma sarki na 10 a jerin sarakunan Fulani. Sannan kuma sarki na 3 da Turawa suka naɗa. An naɗa sarki Abdullahi a matsayin sarkin Kano lokacin yana Ciroman Kano. Shi ne farkon Ciroman Kano da ya zama sarki. Sarki Abdullahi Bayero mutum ne mai haƙuri da kuma tattalin jama’arsa.

An haifi Bayero a shekara ta 1299 bayan hijira (1881). Ya yi karatunsa na farko na addinin Musulunci a fadar Sarki, kuma manyan malaman addinin Musulunci na zamaninsa ne suka Karantar Dashi. Yayin da yake Chiroma na Kano kuma Hakimin Bichi ya samu kusanci da manyan Malamai .

Lokacin da Turawan mulkin mallaka na Ingila suka gabatar da sabon tsarin gudanarwa na gundumomi Abdullahi Bayero, wanda a lokacin shi ne Chiroma, aka nada shi Shugaban Gundumar Gida mai hedikwata a Dawakin Kudu daga baya (1914) a Panisau. An nada shi Sarkin Kano a watan Afrilu 1926 kuma an nada shi a hukumance a ranar 14 ga Fabrairu 1927. Shi ne wanda ya fi kowa gogawa A yan takarar sarautar, kuma An tabbatar da cewa shi mai gaskiya ne, kwararre, Da sadaukarwa da gaskiya.

Sarki Kano Abdullahi Bayero ya yi nade-nade da dama a tsawon mulkinsa. Daga cikin wadanda ya nada akwai ‘ya’yansa Muhammad Sanusi wanda ya nada Ciroma kuma Hakimin Bichi, mukamin da ya rike kafin a nada shi Sarki; da Aminu wanda aka nada Dan Iya da Hakimin Dawakin Kudu. Bayan sauke Muhammad dan Sarki Kano Shehu Usman daga Turaki kuma Hakimin Ungogo ya nada ’yan uwansa Abdulkadir da Muhammad Inuwa a matsayin Galadima da Turaki a shekarar 1927. Ya rage tasirin Cucanawa ( Bayin Sarki ) ya kuma ‘yantar da duk wasu bayin sarauta, wanda hakan ya sa ya ‘yantar da sauran bayi. ya yi dai-dai da tsarin mulkin Burtaniya na yaki da bauta. 

Kamar yadda Sarki Kano Bayero ya himmatu wajen bunkasa kasuwanci da masana’antu na Kano, ya karfafa ayyukan masana’antu Da gaske: misali masana’antar Gwamaja Textile Mills, wacce ita ce farkon masana’anta na zamani a Najeriya . Ya kuma karfafa guiwar ’yan kasuwa masu zaman kansu irin su Alhaji Alhassan Dantata. Majalisar masarauta ta baiwa bangaren hidimar jin dadin jama'a kulawar da ta dace.

Garin Kano shi ne wuri na farko a Arewa da aka samu wutar lantarki da ruwan Famfo, Wannan ya samo asali ne sakamakon yunƙurin da Abdullahi Bayero ya yi, wanda a shekarar 1927 ya ba da shawarar cewa za a yi amfani da rarar kuɗaɗen da ke cikin asusun gwamnatin ƙasar wajen samar da wutar lantarki da kuma samar da ruwan sha ga Kano baki ɗaya. Har zuwa lokacin, ana ba da waɗannan ayyuka ga yankin Gwamnati kawai.

Ma’aikatar Ayyukan Jama’a a Legas ta yi kakkausar suka ga wadannan shawarwari bisa dalilan kashe kudi da kuma rashin samun ma’aikatan da za su gudanar da aikin. Duk da haka, Hukumar Kula da Ƙasar ta ci gaba da samun ƙididdiga daga wani ɗan kwangila kuma aikin ya fara. An fitar da ruwa daga kogin Challawa mil goma daga garin, kuma kowane fili da ke cikin birnin an samar da akalla fitila guda daya. A cikin 1929 an buɗe shirin a cikin ƙa'idar a cikin manyan bukukuwa. Da farko ma’aikatan Hukumar Mulkin ƙasar suka kula da shi.

Sarkin Kano Abdullahi Bayero ya kasance mai matukar sha’awar ilimin addinin Musulunci, kuma ya ba da gudunmawa ta fuskar dabi’a da abin duniya wajen ci gabanta. Wannan ya sa Kano ta samu manyan malaman addinin Musulunci a zamaninsa, wadanda suka hada da Shehu Muhammad Salga da dalibansa Abubakar Mijinyawa da Umar Falke. Ya kafa makarantar shari'a ta Shahuchi a shekarar 1348 bayan hijira (1929), irinta ta farko a Najeriya. tare da Shaikh Sulaiman, abokin aikin sa na dogon lokaci, wanda ya fara tunanin a matsayin shugaban makarantar na farko. Makarantar koyon aikin lauya ta Kano, wadda daga baya ta zama makarantar koyon harshen Larabci, ta Samo ne daga Makarantar Shari’a ta Shahuchi, ta hanyar kokarin Waziri Gidado wanda a lokacin shi ne Babban Mashawarcin Shari’a na Sarki. Shi kuma Shaikh Sulaiman wanda ya kafa shi a cikin darikar Tijjaniyya ( 'yan uwantakar Sufaye ta sufanci wanda Shaikh Ahmad al -Tijani na Aljeriya ya kafa ) ya karfafa masa kwarin gwiwa.

Sannan a zamaninsa aka gina makarantar ‘Middle School’ da ta koma Kwalejin Rumfa (Rumfa College) a yau. Wannan makaranta tana nan a kan titin zuwa Jami’ar Bayero daga Gidan Murtala.

Sarki Kano Abdullahi Bayero shi ne Sarki na farko da ya fara aikin Hajji , don haka aka fi saninsa da Sarki Alhaji. Ya samu rakiyar kanensa Galadima Abdulkadir da Ma'aji Mallam Sulaiman wanda daga baya ya zama Walin Kano na farko. A wannan tafiya ta Hajji ne suka fara haduwa da Shaikh Ibrahim Niass na kasar Senegal kuma suka karbe shi a matsayin Shaihinsu. Bayan kammala aikin Hajji Sarki Abdullahi ya ziyarci Masar inda ya ga masallatai masu ban sha'awa. Da ya dawo sai ya fara ginin sabon masallacin Kano, ( Masallacin Gidan Sarki Na Yanzu ) wanda shi ne irinsa na farko a arewacin Najeriya, kuma har yanzu yana daya daga cikin mafi kyawun masallatai a yankin.

A karshen mulkinsa aka kafa kungiyar ‘yan siyasar Kano: Abba Maikwaru, Bello Ijumu, Babaliya Manaja, Musa Kaula, Abdulkadir Danjaji, Musa Bida, Magaji Dambatta da Mudi Spikin Wannan jam'iyyar siyasa ce mai tsattsauran ra'ayi wacce ta ke Addawa da mulkin mallaka da Sarakunan gargajiya. Amma Sarkin Kano Abdullahi Bayero ya yi taka tsantsan. A lokacin da aka gabatar da shugabannin NEPU a gaban kotunsa bisa zargin tayar da fitina, sai kuma jami’an fadar da suka hada da Malamai suka shawarci Sarkin cewa su ba Musulmi ba ne, kuma sun cancanci a kashe shi, sai ya ki amincewa da wannan nasihar, yana mai cewa ‘Lallai mun yi wa wadannan matasa wani abu da ba daidai ba. da Su ke kalubalantar mu'.

Sarki Abdullahi shi ya sa aka yi ta ciccike kududdufan da ke cikin birnin Kano saboda kiwon lafiya.

A tarihin Kano za a rika tunawa da shi a matsayin Sarki na kwarai, mai gaskiya, mai tsoron Allah da hakuri. Mutum ne mai saukin kai wanda ya kasance yana dinka kayan sawa Da Kansa, yana kuma kula da kananan ma’aikatansa sosai, kamar yadda ya faru a Inuwa Wali, lokacin da Sarki ya umarci daya daga cikin hakiman Unguwanni, ba tare da son fadawa ba, ya tabbatar da hakan. cewa a bashi gida. Daga karshe aka ba shi gida a unguwar Mandawari, inda ya rayu sama da shekaru hamsin.

A Wata Babbar Sallar Layya, Bayan An Idar Da Sallar Idi Sai Sarki Abdullahi Bayero Ya Mike Yace: Duk Wanda Allah Ya Baiwa Ikon Yin Layya Yaje Gida Ya Gabatar Da Layyarsa Bana Allah Bai Horewa Sarki Abinda Zaiyi Layya Ba.

Sarki Abdullahi Bayero ya mulki Kano na tsawon shekara ishirin da bakwai. (27)

Sarkin Kano Alhaji Abdullahi Bayero ya rasu a ranar Alhamis 13 ga Rabi al-Thani 1373 (23 Disamba 1953).

Monday, May 1, 2023

KASUWAR KWADI A HADEJIA... Daga Usman Rangis Mawallafi

HADEJIA A YAU!


KASUWAR KWADI DAKE HADEJIA ( Hadejia Market of Toads)

Babbar kasuwa da Masayen Kwadi ke zuwa daga Jahohin Benue da Kogi da Nasarawa da kuma wasu daga cikin Jahohin Kudu Maso Gabashin Nageriya domin sayen Kwadi.

Ni da kaina ajiya Lahadi na ziyarci Kasuwar kuma na zanta da Madam Inya-Ozi-Ohinoyi daya daga cikin dinbin Masu ziyartar Kasuwar duk sati tana sayen Kwadi.

Da farko dai Mun gaisa kuma na tambayeta ko daga ina take zuwa sayen wannan Kwadi? Sai ta ce min tana zuwa tun daga garin Igumale da ke jahar Benue, sai kuma na Tambayeta ko tun yaushe suke tasowa daga garinsu zuwa Nan?  Madam Inya sai tace tun ranar Juma'a  da yammaci suke tasowa suwayi gari  har ranar Asabat kuma Nan da Maraice sun iso Hadejia kafin washegarin Lahadi ranar da Kasuwar ke ci.

Bayan haka na tambaye ta ko nawa take sayen duk tsinke daya na Kwadi (Stick of Frogs) sai tace kananan tsinke suna sayensa dari 700 zuwa 800 Manya kuma suna sayensa dubu 2800 zuwa 3200, na kuma ta cigaba da tambayarta  cewar idan ta sayi kwadin ina take kaiwa sai ta ce min daga Nan suna loda sune a babbar Mota da take Kai musu Kasuwar Garin Gboko da ke Benue daga Nan kuma akwai Wadanda suke zuwa suke saya Musamman masu gidajen sayar da abinci (Restaurant) da Otel da kuma daidaikun Mutane.

Kasuwar ta Kwadi da ke garin na
 HADEJIA ta fara kafuwa ne kusan shekaru 10 da suka Gabata, Amma a wadancan lokutan Kasuwar bata girma ba sakamakon kyama da kuma rashin Takamemen wajen sana'ar.


A Dan shekarun baya bayan Nan dai Kasuwar ta kafu a dan wani waje na wucin gadi da ake Kira Kasuwar "Jam Bulo" bayan da ruwan sama da ke taruwa akasuwar lokacin Damina, sai Masu sana'ar kamin kwadin sukayi kaura zuwa wani wuri na wucin gadi a gefen filin Ma'aikatar Raya Kogin Hadejia jama'are (Hadejia Kama'are river Basin), inda suke har yanzu.

Kungiyar Masu sana'ar kwadin da ke garin na HADEJIA bukaci da Hukumomin jahar da su nema musu wuri na dindindin (Permanent site) domin cigaba da sana'arsu ganin cewar Gwamnatin karamar Hukumar.

Saturday, April 29, 2023

A tale of forgotten Hadejia airstrip

HADEJIA A YAU!



Many years ago the residents of Hadejia and adjoining villages, mostly Fulani herders saw an airplane hovering around while descending slowly; they all abandoned what they were doing and thronged to the airstrip located about two kilometers away from Hadejia town in order to catch a glimpse of the gigantic flying object.

Daily Trust on Sunday gathered that the airstrip which was said to have been opened in 1954 was only used for transporting high profile personalities, who were mostly colonial masters.

It was gathered that the former Premier of the regional government of defunct Northern Nigeria and the Sardauna of Sokoto, Ahmadu Bello, used the airstrip while on a campaign rally in Hadejia emirate.

The airstrip which had only a windsock as landing and take-off instrument was used only for very important occasions.

Although there are various versions on how the airstrip looked at that time as some sources said there was a literite compacted runway, while others said it was just a dusty plain land that served as the runway.

In any case, what remains of the airstrip include two dilapidated structures and a plain land with demarcation signs, suggesting it is no longer in use. The land has also been allocated for development.

As most of such airstrips across the country, it could only accommodate small planes which carry six to seven passengers.

Daily Trust on Sunday gathered that when it was in use, a canopy was always erected for receiving personalities. 

Security agents drafted to the airstrip during such visits were the royal guards and the Native Authority policemen.

Adamu Dede, a Fulani herder who said he witnessed the landing and take-off of an airplane from the airstrip on about three different occasions, said though he was only seven years of age, he could remember the dust that took over the entire area whenever the plane was taxing for taking off.

He added that at that time, whenever they noticed “the big flying object coming close to the ground, we would rush to the airstrip because that meant that a plane was about to land.”

Dede, who was seen rearing cattle on the land once used as the airstrip, told our correspondent that at that time, their major concern was to see the airplane land, not the personalities on board.

Dede, who is now about 60 years of age, added that at that time age or sex didn’t matter as they all rushed out each time a plane approached the airstrip. 

On how long the plane usually stayed on ground before taking off, Dede said it remained at the airstrip for about three to four hours before it flew back to base.

He said he could remember that there was a flag in the place, probably that was the windsock which aided the pilot in determining not only the direction of the wind but also the velocity of the wind.

Dede who spoke with excitement recalled that the plane he saw on three different occasions bore different designs.

He said they were all white in colour but with different stripes.

He added that the royal guards, who were fully in charge of security, were always on horse- back.

“No one could go close to the plane let alone touch it. Apart from the few who were privileged to go to Saudi Arabia on pilgrimage, nobody can say exactly what the interiors of the plane was like. I was a child then and you know children of those days were not so inquisitive,” he said. 

Speaking to Wazirin Hadejia, Alhaji Hashim Amar, said the airstrip was established in 1954, and that he was a primary school pupil at that time.

The Waziri recalled that when the Premier of Northern Nigeria, Ahmadu Bello, came to Hadejia they assembled at the airstrip to welcome him.

Amar, however, added that he could not speak much about the airstrip, which functioned mainly between 1954 and 1965, because he left Hadejia for school in Kano.

He added that the airstrip was last used by Ahmadu Bello in September,1965, when he came for political campaign, saying, there was information that apart from Ahmadu Bello, the military also used the airstrip.

By Haruna Aliyu Hadejia