HADEJIA A YAU! Wannan Dandali Na kirkireshi don bada Tarihin Kasar Hadejia, da Tarihin Sarakunan ta, da wadanda suka bada Gudunmawa wajen Inganta Al'adun Gargajiya. Hadejia A yau. Ismailasabo@gmail.com
Sunday, February 12, 2017
TARIHIN ƊAN HAUSA (Sir Hanns Vischer)
Sunday, January 15, 2017
SARKIN MUSULMI SIR. ABUBAKAR III.
2. Sultan Muhd. Maccido in the shadow of his Ancestors, Littafin Hassana Isma'ila Bichi.
3. Gaskiya ta fi Kobo ta Hudu (4) 1939.
Tuesday, November 1, 2016
TARIHIN GARIN KANO.....
MADOGARA....
Razdan C.R Niven
Muhammadan Emirate.
Assessment report by colonial Administration.
Sunday, October 30, 2016
TARIHIN GARIN BARNO (MAIDUGURI)...
Saturday, October 15, 2016
BUPOLY HADEJIA... TRIBUTES TO PROF. M.A.HUSSAINI. By Auwal Abu Daud.

Wednesday, October 12, 2016
THE SHETTIMA OF HADEJIA, BARRISTER IBRAHIM HASSAN HADEJIA. By Muhammad Lawal Yahya.
Saturday, October 8, 2016
GALADIMAN HADEJIA USMAN.....Daga Suleiman Ginsau.

NAZARI AKAN TARIHI DA RAYUWAR GALADIMAN HADEJIA ALH. USMAN ABDUL'AZIZ. (USMAN II)
(TARE DA SULEIMAN GINSAU)
"SALSALAR HAIHUWA DA KARATUN GALADIMA"
Tsarawa
ISMAILA A SABO
Monday, October 3, 2016
TSARIN ZAMAN JAMA'A DA TATTALIN ARZIKI A KASAR HADEJIYA KAFIN ZUWAN TURAWAN MULKIN MALLAKA. (Kashi na 1). Daga Suleiman Ginsau...



Kasar Hadejiya tana da kabilu daban daban, amma duk da haka wannan masarauta a cure take a waje daya. Addinin Musulunci shi ne ya dada hada su da kuma harshen Hausa wadda suke magana da shi a matsayin harshen kasa. Babu wata tababa cewa Addinin Musulunci shine Addinin da mafi yawan jama'a suke bi a wannan masarautar ta Hadejiya. Ka'idoji da dokoki da hukunce-hukuncen Musulunci su ne suke tafiyar da rayuwa da ayyukan mutanen wannan kasa. Addinin Musulunci ya hada kan jama'a kuma ya samar da hanya madaidaiciya ta zaman al-umma. Ta hakane Musulmi masu rinjaye da wadanda ba Musulmi ba marasa rinjaye mazauna kasar Hadejiya kafin mulkin mallaka suna ganin sarkin Hadejiya nada mutukar kima kuma shugaba ne babba duk da yake suna da hakimai da dagatai wadda suke jagorancinsu, Mutanen Hadejiya sukan hadu a kowace shekara su gudanar da bukukuwan Sallah karama da Sallah babba a Hadejiya.
Ta haka al'ummar Hadejiya take cudanya da juna cikin walwala, farin cikin, nishadi, jindadi da annashuwa da sakin fuska. Kuma bisa dukkan alamu, kabilun da suke zaune a Hadejiya sun shiga juna, za'a taras bisa asali, Bahaushe, Bababbare ne, ko Bamange, ko babade, ko kuma bafulatani. Haka dai kabilun kasar Hadejiya suka sarki juna.
Jama'ar da ba Musulmi ba suna karkashin kariya ta wannan masarauta, amma su kuma suna bayar da jizya. Al'adun Hausawa/Fulani Hadejiya suna da babban tasiri na mutanen Gabas wato al'adun Barebari. Akwai misali da yawa da za a iya bayarwa a kan haka, kauki misalin sunayen wasu mukaman sarautu kamar Zangoma da Bulama da Kacallah da Maina (dan Sarki) duka daga wajen Barebari a ka samo su.
Hatta ma bikin Sallar maulidi ana gudanar da shi ne dai-dai yadda Barebari suke yi. Ashe ke nan al'adun Barebari sun yi tasiri. (Sulaiman Ginsau )
Kari a kan wadanan kyawawan huldodi na mutanen Hadejiya a tsakanin junansu, tsarin da masarautar ta bi wajen tafiyar da al'amuranta na mulki ya dada kara wannan dankon zuminci. Tun daga farkon kafuwar daular, Sarkin Hadejiya Malam Sambo ya dora kowace kabila daga cikin kabilun kasar a kan wani mukami na sarauta. Wannan tsari da aka ci gaba da aiwatar da shi, ya sanya jama'ar kasar sun zauna a dunkule tamkar tsintsiya domin kowace kabila ta san tana da wakilci a majalissar wannan masarauta.
Ta fuskar tattalin arzikin kasa kuwa, Hadejiya tana da yalwataccen arziki tare da sana'o'i da masana'antu iri-iri, duk da yake harkokin noma sunfi daukar kaso mai yawa. Magidanci shi ne tushen arziki a tsarin zaman jama'a tare da iyalansa a matysayin masu taimakawa. Talakawa sun tsayu sosai wajen yin noma na lokacin damina da noman fadamu a lokacin rani, sannan kuma kamun kifi da kiwo sun zama ruwan dare a tsakanin mazauna kasar Hadejiya. Amfanin gonar da aka fi nomawa sun hada da:-
1. Gero
2. Dawa
3. Shinkafa
4. Wake
5. Masara
6. Gyada
7. Auduga
8. Alkama
9. Ridi da Kankana
10. Rake da sauran kayan lambu kamarsu Timatir da Tatttasai da Taruhu da Rake da sauran kayan lanbu ana noma su ne ta hanyar noman fadama a lokacin rani. Kasar Hadejiya, kamar sauran kasashen wannan nahiya, tana da kyakkyawar kasar noma Gero da Kiwon Dabbobi. Har wa yau kuma wannan yanayin wuri ne mai albarka ya ba da damar aiwatar da wasu sana'o'I kamar su Rini da Saka da Kira da Ginin Tukwane da Jima da Dukanci da Gini da sauransu.
A bangaren saka kuwa kauyen Bangelu wanda yake tsakanin Auyo da Hadejiya ya shahara sosai wajen saka da dinka Rigar Bullamai tare da sauran Rigunan Saki Fari masu inganci. Haka kuma kauyen Hadejia ya yayi suna a sana'ar Rini. Mutanen Hadejiya da suke zaune a daura da kogin Hadejiya sunyi fice a sana'ar Su ta kamun kifi. Haka kuma dajin Hadejiya cike yake da kudan zuma inda ake samun zuma mai tarin yawa. Diban zuma ya zama wata sana'a mai riba ga jama'ar kasar Hadejiya musamman yadda take tallafawa wajen warware matsalolin rayuwar yau da kullum.
Bugu da kari mutanen Hadejiya kamar sauran wurare, sukan sayar da amfanin gona wanda ya yi rara, ta haka suka shiga hada-hadar kasuwancin amfanin gona daga cikin hanyoyin da suka kara habaka Tattalin Arzikin Kasar Hadejiya kafin zuwan turawan mulkin mallaka. Ta wannan hanya masarautar Hadejiya ta zama wata cibiya kuma muhimmiyar mahada ta cinikin kayan amfanin yau da kullum a gabacin kasar Hausa a karni na sha tara (K19). Masarautar ta yi fice wajen fitar da kayayyakin abinci kamar Alkama da Kifi zuwa Kano da wasu wurare, ita kuma sai ta sayo Goro da makamancin abubuwan da masarautar take da bukata. Kamar yadda aka fada a baya, mutanen Hadejiya na kasuwancin Rigunan Saki ko Rigunan Fari da Zuma da Kiraga wato (Fatu) da Shanu, su kuma su sayo Gishiri da Dawakai da Kanwa. Ana kuma jin cewa Hadejiya ta zama wata hanya ta fatauci na fataken da suke ratso Sahara zuwa Kano ta yamma da kuma Barebari da Larabawan Fezzan da Azbinawa da Buzaye daga gabas da kuma yamma. Wadannan fataken sukan hadu a kasuwar Hadejiya su gudanar da harkokin cinikayyarsu na kayayyaki kamar Rigunan kano da kanwa da Shanu da Bayi da kayan Yaji (Sulaiman Ginsau).
A wannan lokacin da ake Magana, a Hadejiya akwai manyan kasuwanni guda biyu (2) daya kasuwar an yi ta a wajen ganuwa, an kakkafa rumfunan da kuma masaukai na baki wadanda aka yi don samar da wuraran zama da jin dadin fatake da sauran yan kasuwa. A cikin ganuwa ta birnin Hadejiya akwai wata kasuwa wadda take kula da bukatun mazauna birnin Hadejiya da makwabtanta. Wannan ya nuna cewa bayan kasancewar Hadejiya cibiyar mulkin da ayyukan jin dadi jama'a, haka kuma tana matsayin ingantacciyar cibiya ta kasuwanci. Wannan kasuwa tana karkashin kulawar Zangoma wato Sarkin kasuwa. Zangoma shi ne yake karbar dukkan haraji na wannan kasuwa tare da masu taimka masa.
A dunkule, wannan yayi bayanin Hadejiya a matsayin masarauta ta mulkin jihadi da kuma fito da tsarin zaman jama'arta da tattalin arzikinta kafin mulkin mallaka na turawan ingilashi a kan daular Usmaniyya ta Sakkwato.
An kuma nuna cewa a fanning Siya sa, Hadejiya gari ne na 'yan Boko da 'yan siya sa masu yawan gaske kuma Hadejiya garine na kasuwanci wadda hakan ya sa mutane suna zuwa siyan kayayyaki daga gurare daban-daban, sannan masarautace mai karfi a tsakanin masarautun da suke gabacin kasar Hausa, musamman yadda take tsoma baki a harkokin cikin gida na makwabtan ta.
Haka kuma nayi wai-waye ta fuskar tsaro ya bayyana cewa Hadejiya kasace jaruma kuma karshen karni na sha tara (K19) sai ta zama kasa mai kyakkawar huldar dangantaka da zama na lumana da abokan taka da sauran masarautu. (Sulaiman Ginsau)
Muhadu a kashi na biyu 2
Friday, August 12, 2016
SARKIN HAƊEJIA ABUBAKAR MAJE HARUNA (1984-2002).
Saturday, July 30, 2016
HADEJIA TOWN WALL AND GATES...
HADEJIA TOWN WALLS AND GATES
"Hadejia was a large town with 5 town gates and excellent walls about 30ft (9. 14m) high, and 30ft(9. 14m) thick " ... (Captain Philips 1909) Hadejia Town walls had a long history dating back to the pre-jihad period. The walls were built to provide security to the people, and to serve as fortification against external invasion. Though mostly in ruins now, with a great proportion having completely disappeared, the walls were
intact up to the time of the colonial invasion in 1906.The construction of the walls was done by direct labour using local building materials. Over the years, the walls have been taken subjected to
several phases of development.
were made extremely strong, thus making it very difficult for an enemy force to break into the town through them. The gates were manned by
gate-keepers or porters (sarakunan kofa)
appointed by the Emir. These keepers used to close the gates everyday from dusk to dawn, thus controlling the movement of people in and out of the town during these periods. Visitors or
strangers were not allowed in unless with the express permission of the Emir. It was reported that one Emir ordered the gates to be left open permanently, confident that no enemy force would dare attack the town.
The first town wall in Hadejia was believed to have been built during the pre-jihad period. Though the exact date of its construction cannot be determined due to lack of proper records, its
perimeter is marked by certain well-known local pits: Mai kilabo in the west, Atafi in the south, and Dallah in the East.
with its perimeter approximately put at 2 miles 170 yards. It had 5 gates. The present wall, which was the third, was also built during Sambo's reign. It was built at a time when Hadejia was at
the centre of a bitter rivalry between Sokoto caliphate and Borno Empire. As such it was much stronger and wider than the previous walls. An extension to this wall was later made on the
Eastern side during the reign of Sarki Haruna (1865 -1885), encompassing a large space to harbor fugitives from surrounding villages in times of war. The Habe settlement of Fantai, which hitherto was outside the wall, also became sheltered in the new extension. This brought the wall to its present size of 4 miles 135 yards, with 5 gates, namely:
Kofar Gabas (also known as Kofar Gwani), Kofar Arewa, KofarYamma
Kofar Kyalesu (also Known as Kofar Kogi), Kofar Mandara (also known as Kofar Talata). Apart from the Kofar Mandara gate, which was destroyed by the British in their attempt to gain
over the years, the latest being in1985 which saw the total re-construction of Kofar Arewa and Kofar Yamma. The Hadejia town gates now stand as
historical monuments rather than as security outposts.
BY: SULEIMAN GINSAU
Friday, July 29, 2016
A SHORT HISTORY OF GARUN-GABAS.. (BIRAM)

Reference--- Assessment reports by K. L. Hall, Assistant District officer Hadejia District Kano Province.14th/July/1915.
Friday, July 15, 2016
SIR AHMADU BELLO'S CHRISTMAS MESSEGE IN 1959...

“We are people of many different races, tribes and religions, who are knit together by common history, common interests and common ideals. Our diversity may be great but the things that unite us are stronger than the things that divide us. On an occasion like this, I always remind people about our firmly rooted policy on religious tolerance. Families of all creeds and colour can rely on these assurances. We have no intention of favouring one religion at the expense of another. Subject to overriding need to preserve law and order, it is our determination that everyone should have absolute liberty to practise his beliefs.
It is befitting on this momentous day, on behalf of my ministers and myself, to send a special word of gratitude to all Christian missions. Let me conclude this with a personal message. I extend my greetings to all our people who are christians on this great feast day. Let us forget the difference in our religion and remember the common brotherhood before God, by dedicating ourselves afresh to the great tasks which lie before us.”
Monday, July 4, 2016
AL'ADUN KASAR HADEJIA... Kashi na Daya (1)
WASU DAGA CIKIN AL’ADUNMU KYAWAWA…
Kasar Hadejia mutanen cikinta suna da Al’adunsu kyawawa wadda suka dace da koyarwar Addinin musulunci, wadannan Al’adu saboda kyawunsu yasa mun taso a cikin kyakkyawan tsari da taimakon Junanmu. Shekaru da dama da suka gabata zakaga mutumin Hadejia bubba da yaro yana da Tarbiyyar idan yaga bubban mutum ya gaidashi, kokuma idan yaganshi da kaya a hannu yaje ya karveshi, wannan Al’ada tana da kyau kuma tayi daidai da tsarin Addinin musulunci. Sannan a shekarun baya duk Unguwar da kaje zakaga tsarin zamantakewarsu akwai ban sha’awa, domin wurin zaman manya daban na yara daban sannan idan zaka wuce Bubban mutum yana zaune zaka cire Takalmi sai ka wuce sannan ka saka. Wani abin ban sha’awa shine Lokacin cin Abinci babu yadda zakaga mutum yaci abinci shi kadai ai haduwa ake mutum huxu ko biyar ake ci tare domin neman Albarka. Wannan ya nuna akwai son juna a tsakaninmu, domin wadda Allah bai bashi ikon yin abinci a gidansa ba to bazai wuni da yunwa ba domin idan yazo Dandali zaici tare da ‘yan-uwansa. Haka yara matasa suma kowa yakan dauko abinci daga gidansu a fito a hadu a ci, wannan muke kira da suna Ciyayya.
ZAMANTAKEWA…
Zamantakewa wata kalma ce da take nuni ga yanayin yadda mutum yake rayuwarsa tare da Abokan zamansa wadda Allah ya hadasu, walau a zaman Makwaftaka ko sana’a da sauransu.
TSARIN SHUGABANCHI…
Shugabanci yana nufin rikon on ragamar Al’umma da basu Umarni da kuma yi musu Jagoranci bisa tafarkin da suka aminta dashi, sannan da tsara musu Dokoki da sasanta tsakaninsu. A Kasar Hadejia tsarin shugabanci ya faro ne tun daga cikin gida inda mutum a gidansa shine shugaba mai shirya komai da kuma bada Doka da Oda, sannan sai shugabancin Unguwa wadda ya kasance kowace Unguwa tana da nata shugaban mai sawa da hanawa da bada umarni shine muke kiransa da suna Mai-unguwa. Duk wani umarni yana fitowa ne daga bakin Mai-unguwa kamar hani da kuma sawa. Shi wannan Mai-unguwa duk abinda ya shafi Unguwarsa shine keda iko akai, kamar Umarni, hani, sasanto tsakanin mutane. Kuma duk Bakon da yazo wannan Unguwa akan kaishi gidan Mai-unguwa ne domin shike da Alhakin yaji abinda ke tafe dashi idan mazauni ne shine da hakkin bashi masauki ta haka ake tsaftace Nagari da Mugu a cikin Unguwa. Baya da Mai-unguwa a gari akwai Malami wadda idan wani Bakon malami yazo wurin Wannan malamin za’a kaishi shi zai bashi masauki sannan yaji Dalilin abinda ke tafe dashi. Haka kuma Idan Bakon dan kasuwa ne akan kaishi Gidan Zangoma wadda shine da hakkin saukar Baki musammam masu saye da sayarwa, shi zangoma shine zai tambayeshi irin Hajojin da yake sayarwa kokuma yake saye domin ya sadashi da masu ciniki. Kaga duk wannan yana nuna muna da kyakkyawan tsari na zamantakewa wadda duk mutumin da ya shigo kasar Hadejia ansan Dalilin zuwansa da kuma abinda yazo yi. A duk lokacin da aka samu hakan shi Mai-unguwa shike da Alhakin sanarwa Bulama sannan Bulama ya sanarda Hakiminsa, shi kuma Hakimi zai sanarda Majalissar Sarki.
Wannan tsarin shugabanci shi ake amfani dashi a kasar Hadejia har lokacin zuwan Turawan Mulkin Mallaka. Koda yake Turawa ma da sukazo sai suka lura cewa muna da kyakkyawan tsari na shugabanci, dan haka sai suka nemi Hadin kan Sarakunanmu ya zamanto zasu bada Umarni ne ga Sarakuna sannan Sarakuna su bada Umarni ga Talakawansu. Turawa sunzo sun samemu da Al’adunmu kyawawa sannan muna da tsari na shugabanci kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada mana, wannan dalili yasa Turawa suka samu damar Mulkarmu ba tare da sunsha wahala ba.
Sunday, February 21, 2016
MARIGAYI ALHAJI ADAMU KWANO HADEJIA.....

Daga Mallam Muhammad Rabakaya...
Da fatan zamuyi koyi da irinsu a duk bangarorin rayuwa.
Friday, February 19, 2016
TARIHIN HADEJIA.

Takaitaccen Tarihin masarautar Hadejia.
posted from Bloggeroid
Tuesday, October 6, 2015
KO KUN SAN?........
A shekarar 1971 anyi wata gagarumar yunwa da fari wanda aka sawa suna KWAKWUDUBA, a wannan lokacin hatta fadamu da koguna duk sun kafe babu ruwa, kuma abinci yayi karanci ga mutane. Hakan tasa mutanenmu musamman wadanda garuruwansu yake kusa da Kogi (Masunta) sukayi Kaura daga garuruwansu suka nufi Gabas. Wasu sun wuce har Chadi wasu kuma suka shiga har Kamaru, yayinda wasunsu suka tsaya a garin Baga.
Koda yake a lokacin wannsn garin da ake Kira Doran Baga mutanenmu ne suka je suka kafa Daba a kusa da gabar Kogi. Anan ne sukaci gaba da zamansu suna Kamun Kifi da sauran Albarkatun ruwa sannan su sarrafa su kawo Maiduguri da wasu sassa na jihar Yobe su sayar. Haka gari yaci gaba da girma sakamakon zuwan mutane Masunta domin su samu abinda zasuci da Iyalensu. Sakamakon gari ya zama gari har sai ake kiran Dabar tasu DORON BAGA.
Akasarin mutanen da suka tafi daga kasar Hadejia mutanen Kafinhausa ne da kuma yankunan Kirikasamma da Guri, idan ka lissafa wancan lokacin zuwa yau zai baka shekara 44. Wadannan mutanen wasunsu sun bar garuruwansu ba tare da suna dawowa suna gaida Iyayensu ba, wasunsu kuma har iyayen nasu suka bar Duniya basuzo sun gansu ba,wasu a cikinsu sun manta yanda yanayin garinsu ma yake saboda sun samu Duniya acan. Da yake ba duk aka taru aka zama daya ba wasu sukan zo su gaida 'yan-uwansu da abokan Arziki sannan su koma tunda Allah yayi zamansu acan.
RIKICIN BOKO HARAM....
A cikin Shekarar 2008/2009 Rikicin Boko Haram ya faru a Gabashin Nigeria, musamman yankunan Jihar Borno da Yobe da wasu sassa na Adamawa da Bauchi da Gombe, wanban rikici yayi Asarar Rayuka da Dukiyoyi masu dinbin yawa, inda akayi ta kone Gidaje da Kasuwanni da wuraren Sana'a. Wannan ne yasa wadancan mutane da na Ambata a sama wadanda Kwakuduba tasa suka bar garuruwansu sai suka fara tunanin su dawo gida, sakamakon fadin Hausawa " Giji Lahira ce" anan ne fa suka fara dawowa ba tare da abinda suka tara a can ba, wasu sun dawo gida sun tarar duk wadanda suka sani sun mutu wasu kuma tsufa ya kama su.
TAKAITACCEN TARIHIN RAYUWAR CHIROMAN HADEJIA. ALH. AMINU HARUNA
Daga Muhammad Yawale....
.
text-align: center;">An haifi Alh Muhammadu Aminu Haruna a garin Guri a shekara ta 1943, A lokacin mahaifinsa Alhaji Haruna Abdulkadir yana Chiroman Hadejia Hakimin Gundumar Guri. Ya halarci makarantar kur'ani wato allo a garin Guri makarantar sule Gangaran a 1952-1956, ya halarci makarantar Elementary primary Dallah a cikin garin Hadejia a 1953-1956, ya halarci makarantar middle school ta fantai hadejia a 1957-1960, sannan ya halarci makarantar horarda malamai ta Bichi a shekara ta 1960-1962.
Marigayi ciroman Hadejia yayi karatu a potiskum (s.t.c sage 1) a 1970 yayi karatu a kaduna polytechnic (stage2-3) a 1971-1974 yayi karatun higher diploma a zaria Insitute of Administration (A.B.U) a 1979-1980. Ya halarci tarurruka na karawa juna sani a wurare daban daban na kasarnan.
AYYUKAN DA YAYI:
Yayi malamin makaranta a lokacin (N.A) ta Hadejia na tsawon shekaru 2, a karkashin tsohon Head master marigayi Alh Abdu maigari Tafidan Hadejia, yayi malamin makaranta a primary ta dubantu a 1965, yayi sakataren karamin minista na MADAKIN Hadejia Muhammadu Gauyama, a ma'aikatar tsaro ta kasa a lagos bangaren jiragen sama (Air-force) a shekarar 1965-1966,
Yayi malami a kotun babban alkali lokacin alkali Dahiru. A shekarar 1966-1968, yayi malamin Turakin Hadejia lokacin Turaki Adamu, yayi Akawu a ma'aikatar mulki ta (N.A), yayi sakataren karamar hukuma a wadannan wurare Bichi, ringim, gumel, wudil, babura, gezawa, kafin hausa, dawakin tofa yayi sakatare na musamman a karamar hukumar birni da kewaye (kano municipal council).
Ya rike mukamin DPM a kananan hukumomin garki, malam madori, Taura a inda yayi ritaya. Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya nadashi Tafidan Hadejia Dan majalisar sarki a shekara ta 1994, cikin yardar Allah kuma Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar ya nadashi Chiroman hadejia a ranar asabar 13 ga watam march 2004 a inda ya gaji yayansa chiroman Hadejia Alh. muhammad Abbas.
Marigayi chiroman Hadejia mutum ne mai jajircewa kan gaskiya da rikon amana akan harkar da aka dorashi kuma ya nemawa mutane da dama aiki a lokacin gwamnati kuma duk abinda ya gani ba daidai ba baya yin shiru sai yayi magana hakazalika bai yarda kayimasa zancen waniba. Marigayi chiroman Hadejia ya rasu ranar juma'a da daddare 03/10/2015 bayan ya sha fama da jinya muna rokon Allah ya jikansa ya kuma kyautata bayansa.
Thursday, May 14, 2015
YAN GUDUN HIJIRA...

YAN GUDUN HIJIRA!
Tun a lokacin da rikicin Boko Haram ya Addabi jihohin Borno da Yobe aka samu watsuwar 'yan gudun hijira a wasu sassa na Nigeria, ciki harda jihar Jigawa, kuma akasarin wadannan 'yan gudun hijira zakaga Mata ne da kankanan yara wadanda mafiya yawa suna a kasar Hadejia da kasar Gumel. A lokacin da suka fara zuwa wadannan yankuna saboda basu da abinda zasuyi dole wasu daga cikinsu suke bin masallatai da majlissai domin neman abinda zasuci abinci da yaransu. Abin tausayi zakaga yara da basu fi shekara 7 zuwa 10 ba suna bi kantuna da wurin zaman jama'a suna neman taimako, a kwanakin baya basuyi yawan da ya wuce kaga biyu ko uku ba a kullum amma yanzu abin sai karuwa yake wanda a kalla sai kaga goma zuwa sama a rana daya da mata da kananan yara abin tausayi. zaka gansu a kofar masallatai da kasuwa har da Bankuna wurin layin Atm. Dole mumini mai Imani ya tausayawa rayuwar wadannan bayin Allah domin ba a son ransu suka bar gidajensu da 'yan uwansu suka zo suke yin Bara ba! Saboda yawan kwararowarsu yasa jama'a sun fara kosawa ganin abin ya zama ba na kare ba, yanzu kullum a baka gansu a gidanka ba kaga biyar ko shida.
MASU HANNU DA SHUNI....
Hakika Masu hali sai sunyi amfani da damar da Allah ya basu wajen taimakon wadannnan bayin Allah da muhalli da Sutura da Abinci, da kuma kula da rayuwarsu musamman kananan yaran. yana da kyau masu hali su ware wani abu daga cikin Dukiyarsu don taimakon wadannan bayin Allah a matsayin Sadakatul-jariya.
GWAMNATI MAI JIRAN GADO...
Koda yake bani da masaniya game da yunkurin da Gwamnatin Jigawa tayi game da wadannan bayin Allah, kuma ban taba ganin wani wuri da aka ware don 'yan gudun hijira ba zanso in bada shawara ga Gwamnati mai jiran Gado, A karkashin mulkin ko jagorancin Jam'iyyar Apc, dasu fara duba wannan Matsalar ta 'yan Gudun Hijira kafin su fara Aiwatar da kowane Aiki domin ceto rayuwar wadannan Mata da kananan yara daga yin Bara, wanda hakan ya fara jefa wasu daga cikinsu zuwa ga halaka. An fara samun rade radin wadannan mata 'yan gudun hijira sun fara yin Arangama da wasu gurbatattun mutane suna yin lalata dasu suna basu kudi, har ma ance wasu da yawa sunyi cikin shege Allah ya kiyaye! Abin takaici sai kaga idan 'yan Hisbah suka kama mace tana lalata in suka bincika sai kaga 'yar gudun hijira ce. Kasan Dalilin da yasata cikin wannan hali?
SHAWARA GA GWAMNATI....
Ina bada shawara ga Gwamnati mai jiran gado da suyi la'akari da wannan matsalar domin su san ta yadda zasu bullowa wannan Al'amari, ya kamata Gwamnati ta samar musu mahalli na wucin gadi sannan ta sanya yaransu a Makaranta don ceto rayuwarsu. kuma Ina baiwa Gwamnati Shawara da ta sama musu sana'oi domin su dogara da kansu. misali Gwamnati zata iya amfani da makarantar koyon sana'a don koyawa Matan yanda ake yin SABULU, SAKA, DINKI,Da sauransu. Daga karshe ina Rokon Allah da kar ya nuna mana makamanciyar wannan Bala'i da zai sa mutum ya bar gidansa da iyalinsa ya tafi wani wuri yana yin abinda ko a Addini yana daga cikin Abu mai Kaskanci. Allah ka zaunar da kasarmu da Jiharmu lafiya.
Ismaila A Sabo Hadejia.
13/may/2015.
posted from Bloggeroid
Thursday, March 26, 2015
TAKOKO GARIN SARKI BUHARI...

Garin Takoko yana daya daga cikin garuruwan Tarihi a Masarautar Hadejia, kuma yana Arewa da garin Mairakumi wanda take karkashin karamar hukumar Mallammadori, Takoko tana karkashin Mulkin Hakimin Garungabas. A lokacin da aka cire Sarkin Hadejia Buhari daga Sarauta ya koma garin Takoko da zama shi da Mutanensa inda kuma anan ne ya zauna tsawon lokaci yana kai hare hare ga kasar Gumel, Damagaram da wasu sassa na yankin Gorgaram (Bade). A zamansa na wannan gari ya samu goyon baya daga Daular Shehun Borno da kuma Machina, sakamakon karesu da yayi daga hare hare daga Mayakan Damagaram.
Bayan cireshi daga mulki da akayi ya koma Takoko Sarkin Hadejia Buhari ya zama Barazana ga Sarakunan Daular Usmaniyya, domin suna tunanin idan aka barshi a wannan gari to Daular Borno zatayi Amfani da karfin mayakansa ta rusa Daular Usmaniyya. Dan haka sai sukayi shawarar suje su yakeshi su kama shi kokuma su kashe shi, sai aka hada mayaka daga kano, katagum, Bauchi, Zamfara da sauransu.
YAKIN TAKOKO:-
Bayan an nada Ahmadu a matsayin Sarkin Hadejia, sauran Magoya bayan shi Buhari sai suma suka bar Hadejia suka koma Takoko inda Buhari yake suka zauna tare. Sarkin Hadejia Buhari anan ya zauna tsakanin Takoko da Shafowa a Arewacin Hadejia da mutanensa kuma yake tafiyar da wannan yankin. Kuma iyakar Hadejia ce da Damagaram da Machina ta Arewa maso Gabas wato yankin Niger da kuma Borno. Kuma Buhari ya bada Gudun mawa sosai a wannan Yankin wajen karesu daga barazanar mayaka, kuma a wannan zama da yayi a Takoko Buhari ya samu kyakkyawar dangantaka da Sarkin Machina da kuma Shehun Borno Umar wanda ya mulki Borno a wannan shekara (1835-1880) wannan dangantaka ta karawa Sarki Buhari kwarewa a yake yake.
(Bishiyar da Sarki Buhari yake hutawa, tana nan a gabas da garin Takoko).

A shekarar 1851, Sarkin Musulmi Alu Bubba yayi shirin ya dauki matakin Karshe akan Buhari, saboda yana tunanin Shehun Borno zai iya amfani da Buhari ya rusa Daular Sokoto saboda ya zame musu Barazana a Arewa Maso Gabas.
A wannan lokacin kuma Dan Galadiman Sokoto ya hada Mayaka daga Hadejia,Kano,Katagum,Misau da Jama'are zuwa Takoko.
A wannan lokacin kuma Buhari da mutanensa sun fita kudu da garin shafowa a lokacin Sarkin Machina ya kawowa Buhari ziyara a garin Takoko shida Jarumansa.
A lokacinda Dan galadiman sokoto suka fito don su yaki Buhari sai ya zabi Sarkin Jama'are Samboli ya jagoranci Mayakan, saboda shi ya fisu sanin Yankin.
A ranar da zasu yaki Buhari kuma a ranar Buhari ya shirya mamaye Garuruwan da suke kudu da Hadejia, sai aka hadu a Garin Shafowa. Yayin da aka hadu aka gwabza fada Buhari yaci Galaba a kansu duk suka gudu, Sarkin Hadejia Ahmadu yayi kokarin ya Gudu Kasar Kano amma sai Barde Risku ya bishi ya Kashe shi.
Bayan Yakin Takoko yazo karshe kuma an kashe Sarkin Hadejia Ahmadu Amma ba'a son ran Buhari ba kuma aka masa Sallah aka kaishi Hadejia aka binne shi, sannan sai Buhari ya koma Hadejia yaci gaba da Mulki. Sakamakon wannan yakin, dangantaka ta sake baci tsakanin Hadejia da Sokoto, kuma Sarkin Musulmi yaki yarda da ya nada Buhari Sarkin Hadejia. Sai ya nada Tukur Na yayari, kanin Sarki Ahmadu kuma yace ya zauna a Mashama a Kasar Katagum a Matsayin sarkin Hadejia ya Gaji dan'uwansa Ahmadu. Amma Tukur bai yarda ya zama Sarkin Hadejia ba saboda yana tsoron Buhari, sai yaga bazai iya yin haka ba. Kuma saboda Gudun kar Buhari ya kasheshi sai Tukur ya Gudu daga Mashema yayi kaura zuwa Kano Lokacin Sarkin Kano Usman Na1(1846-1855) Sai aka Turashi ya Mulki Yayari a Kasar Birnin Kudu. (Yayarin Tukur) Tukur ya zauna acan Har zuwa lokacinda ya Mutu 1909. Buhari kuma yaci gaba da mulkin Hadejia yana kai hare hare a matsayin Jihadi Har saida yakai Gabasawa,Sankara,Ringim da Kuka kwance A Arewa maso yamma. A Kudu saida ya mamaye Kununu,Takalafiya, Kafin baka, Doma, Ruba, Itas da Kwanda. A Gabas kuwa saida ya Mamaye Babuwari, Kazura, Dawah, Gatare da Margadu. Saida Sarki Buhari ya fadada kasar Hadejia tafi Ko ina fadin Kasa a karni na19.











