"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, April 6, 2012

TARIHIN SHEIKH JA'AFAR MAHMOOD ADAM

*Tarihin Sheikh Jafar Mahmud
Adam***
An haifi marigayi Sheikh
Ja'afar Mahmoud Adam a
garin Daura, a shekara ta 1962
(ko da yake wani lokacin
yakan ce 1964).
Marigayi Sheikh Ja'afar ya fara
karatunsa na allo a gidansu, a
wurin mijin yayarsa, Malam
Haruna, wanda kuma dan
uwansu ne na jini. Daga nan
kuma sai aka mayar da shi
wajen wani Malam Umaru a
wani gari wai shi Koza,
kimanin kilomita 9 a arewa da
Daura, wanda shi ma akwai
dangantaka ta jini a tsakanin
su, wanda kuma shi ne
musabbabin zuwansa Kano.
Bayan sun zo Kano ne tare da
wannan malami nasa, a
shekara ta 1971 (ko 1972), sai
suka zauna a makarantar
Malam Abdullahi, wanda
asalinsa mutumin jamhuriyar
Nijar ne, amma yake zaune a
unguwar Fagge a Kano. Tun
kafin zuwansu Kano, tuni
marigayi Sheikh Ja'afar ya riga
ya fara haddar Alkur'ani mai
girma, wanda ya kammala a
shekara ta 1978.
Bayan da Malam ya kammala
haddar Alkur'ani mai girma,
kasancewarsa mai sha'awar
ilimi, sai ya shiga makarantu
biyu a lokaci daya a shekara
ta 1980. Ya shiga makarantar
koyon Larabci ta mutanen
kasar Misra a cibiyar yada
al'adun kasar Misra, (Egyptian
Cultural Centre), sannan
kuma ya shiga makarantar
manya da ba su yi boko ba ta
Masallaci Adult Evening
Classes, tunda a lokacin
shekarunsa sun wuce shekaru
na primary, amma duk da
haka a wannan lokaci shi ne
mafi kankanta a ajinsu. Haka
ya rika yin wannan karatu
guda biyu: Waccan
makarantar ya je ta da
daddare bayan sallar isha'i,
waccan kuma ta koyo harshen
larabcin da yamma. Ya
kammala wadannan
makarantu a shekara ta 1983.
Wannan kuma shi ya ba shi
damar shiga makarantar
GATC Gwale a shekara ta
1984, kuma ya kammala a
shekara ta 1988. A shekara ta
1989, malam ya sami gurbin
karatu a jami'ar musulunci ta
Madinah, a inda ya karanta
ilimin tafsiri da Ulumul Kur'an,
wanda kuma ya kammala a
shekara ta 1993. Sannan kuma
Sheikh Ja’afar ya sami damar
kammala karatunsa na digiri
na biyu (Masters) a Jami’ar
Musulunci, A Oundurman Sudan.
Sannan kuma, kafin
rasuwarsa, ya riga ya yi nisa
wajen karatunsa na digiri na
uku, wato digiri da digirgir
(PhD), a Jami’ar Usman Dan
Fodiyo da take Sokoto.
Daga cikin malamansa na
ilimi, akwai malaminsa na
farko, mutumin kasar Masar,
Sheikh Abdul-Aziz Ali al-
Mustafa, da kuma Malam
Nuhu a unguwar Dandago,
wanda malam ya karanci ilimi
fikihun malikiyya da wadansu
littattafai na hadisi a gurinsa,
da kuma Malam Muhammad
Shehu, mutumin Lokoja,
wanda Malam ya karanci
nahawu da sarfu da balaga da
adab a wajensa. Akwai kuma
Sheikh Abubakar Jibrin
limamin masallacin Juma'a na
BUK, akwai kuma Dr. Ahmad
Muhammad Ibrahim shi ma na
jami'ar Bayero ta Kano. Daga
cikin malamansa na jami'a
kuma, akwai Sheikh
Abdurrafi'u da Dr. Khalid
Assabt.
Daga cikin karatuttukan da
malam ya karantar da su, sun
hada da tafsirin Alkur'ani mai
girma, Kitabuttauhiid,
Umdatul Ahkaam, Arba'una
Hadiith, Kashfusshubuhaat,
Bulugul Maraam,
Riyaadussalihiin, Siiratun
Nabawiy, Ahkaamul Janaa'iz,
Siffatus Salaatun Nabiiy.
Wasu daga cikin daliban
malam sun hada da Malam
Rabi'u Umar R/Lemo da
Malam Sani Abdullahi
Alhamidi Dorayi da Malam
Abdullah Usman G/Kaya da
Malam Usman Sani Haruna da
Malam Ibrahim Abdullahi Sani
da Malam Ali Yunus
Muhammad da Dr. Salisu
Shehu da Malam Shehu
Hamisu Kura da Malam Anas
Muhammad Madabo.
Kafin rasuwarsa, malam ya
fara gagarumin aikin rubuce
tafsirinsa a harshen Hausa a
karkashin wannan cibiya
(Sheikh Ja'afar Islamic
Documentation Centre).
Marigayi Sheikh Ja'afar
Mahmoud Adam ya rasu ranar
juma'a 26/Rabii'u Awwal/1428
(13/04/2007) sakamakon harin
da wadansu 'yan ta'adda suka
kai masa, a daidai lokacin da
yake jagorantar sallar asuba a
masallacin Juma'a na Dorayi.
Ya rasu ya bar mata biyu, da
'yaya shida, yayin da aka haifa
masa ta bakwai kwanaki 58
daidai bayan aiwatar da
wannan kisan gilla a kansa.
Dubun-dubatar mutane ne
daga ko'ina cikin kasar nan
suka halarci jana'izarsa, kuma
an binne shi ne a makabartar
Dorayi. Allah ya ji kan sa ya
gafarta masa, ya saka masa
da gidan aljanna. Amin

Thursday, April 5, 2012

HADEJIA RULER'S (3)

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU

DAGA ISMAILA A SABO!



9. Haru bin Sambo, 1865-1885
With the successful removal of Umaru from power, Haru (Bubba) assumed the emirship of Hadejia.


Haru reigned for 20 years, during which he introduced many far reaching changes in the emirate. He enlarged the wall of Hadejia town to its present size.


He pursued a policy of Islamization of the emirate by opening schools and inviting the Ulama (Islamic Scholars) from other emirates. He was even said to have been in the habit of intercepting many scholars on their way to the holy land and persuading them to settle in Hadejia, in a bid to spread Islamic education.


He was also credited with the re-construction of a much bigger Friday mosque in Hadejia town. In the socio-economic sphere, Emir Haru pursued a policy which attracted foreign traders into Hadejia markets.


He did that by levying lower import duties on certain imports. He waged jihad wars against non¬Muslims areas of Kare-Kare and Bade country, leading to the conquest and subsequent incorporation of the border town of Adiani to Hadejia emirate. Also, it was during Haru's reign that the incessant conflicts between Hadejia and Gumel came to an end with a full blown war at the battle of Zaburam in 1872, in which Sarkin Gumel Jatau was killed.

This success brought to an end the hitherto frequent Hadejia-Gumel wars. Haru died in 1885.

10. Muhammadu bin Haru, 1885-1906 Haru was succeeded by his eldest son Muhammadu, who previously held the titles of Chiroma and Sarkin Marma. Muhammadu, popularly known as Maishahada was an Islamic scholar and a warrior-king who spent most part of his reign fighting wars and battles. His militaristic policies were likened to that of Emir Buhari.

He organized and personally led many battles, including six battles fought in Kare-Kare and Badde country; intervened in the Kano and Katagum civil wars; forcefully seized two neighboring districts of Kano Emirate,
namely Miga and Kwanda, and held them till
the British conquest of Hadejia, when they were returned to Kano.

Finally, he confronted the British forces militarily in the defense of his Emirate. He was killed in the ensuing battle with the British in 1906.

8. Umaru bin Buhari, 1863-1865 With the death of Buhari at the battle field, his son Umaru became the seventh Fulani ruler of Hadejia at the tender age of 18. He assumed the emirship with the active support of Sarkin Arewa Tatagana and Sarkin Yakin Hadejia Jaji, the two most powerful and trusted slave officials of Buhari. The Caliph in Sokoto approved his appointment in a desperate move to get Hadejia back to the Caliphate fold. Umaru reigned for two years only. But those were eventful years indeed. Haru, his uncle, had his eye on the throne, and was secretly plotting against Emir Umaru. Tatagana and Jiji, Umaru's most loyal and powerful supporters, were first eliminated as part of the grand plot to get Umaru deposed. Subsequently, when Umaru went out on one of his usual pleasure rides to the Hadejia river side; he was deserted by a conspiratorial entourage and refused entry back into Hadejia town. Umaru made good his escape to Kano emirate; he took refuge in chamo, Kano Emirate, where he lived for the rest of his life, and died in 1920.