"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, November 11, 2018

MATASA A FAGEN SIYASA.....

HADEJIA A YAU!



1. MATASA A FAGEN SIYASA.  
Da farko zamu dubi kalmar matasa ko matashi, me ake nufi da matasa?
Matasa ko matashi wata kalma ce ta Hausa wadda ake kiran wasu mutane da ita, (Mai Tashe) ana nufin wadanda shekarunsu ya fara daga goma sha takwas  18, zuwa shekara Arba’in 40. Domin ko a musulunci matasa su aka fi bukatar su bada gudunmawarsu don ci gaban al’umma, sannan matasa sune suke shirya duk wani tsari mai inganci na zaman rayuwa wadda idan sun gyaru hakika al’umma ta gyaru.

Matasa a fagen siyasa suna da muhimmiyar gudunmawa da zasu taka domin dorewar Demokradiyya, duk wata gwamnati  bata zama ingancacciyar gwamnati saida matasa. tarihin siyasar duniya  ya nuna matasa sune kan gaba wajen juya akalar rayuwar al’umma, domin sune masu zabe kuma daga cikinsu ake zaba. Babu wata siyasa da zata ci gaba ba tare da matasa ba, kuma matasa zasu iya tsare mutuncinsu a siyasa ba tare da anyi amfani dasu an gurbata siyasa ba. Tun lokacin NPC ta Sardauna da NEPU ta Aminu Kano aka baiwa matasa dama wajen tsayawa takara a kujeru daban daban don inganta rayuwar Al’umma, misali duk dan takarar da ya tsaya takara a lokacin Npc da Nepu babu wadda shekarunsa suka wuce 40, duk daga 35 ne zuwa 37. Haka akayi har zuwa zamanin NPN da PRP Idan ka debe shekarun Shehu Shagari daga lokacin da yayi mulki zuwa yau zaka gane lalle yayi Shugabancin Nigeria ne yana Matashi, Haka Gwamnonin zamaninsa irin su Rimi da sauransu har zuwa Senatoci da ‘yan majalissun Tarayya da na jihohi. Tun daga wancan lokacin zuwa yau matasa ne suke jan akalar Siyasar Nigeria, dukda cewa ana samun tsarmi da yawa da mutanen da muke kira Dattijai. Idan muka dubi lokacin Gwamnatin Saminu zamu ga yayi gwamna ne shekarun sa basu kai Arba’in ba, haka Mataimakin sa Barrister Ibrahim Hadejia ya zama Deputy Governor yana da Shekara 37 zuwa 38. Wannan yana nuna mana cewa Matasa sune dai a fagen Siyasar Nigeria, amma yanzu abin haka yake kuwa? Wadannan mutane da na saka hoton su wato Mustapha Sule Lamido, Ahmed Bello, Hussaini Rally, Barr. Mallam Abubakar Jallo, sune suka fanshi Matasa a fagen Siyasar wannan lokaci, kuma sune zasu zama fitila ga sauran matasan mu zuwa nan gaba, domin sun kasance sun karfafawa matasa Gwuiwa wajen damawa dasu a fagen Siyasa.

MECECE SIYASA?
Ma’anar siyasa itace tsara rayuwa ko samar da shugabanci da duk abinda yake ta’allake dashi, kamar tsarin zabubbuka, yin doka, umarni da hani. Tsarin horo ga wanda ya karya doka, kira ga hukuma da tayi ko ta bar wani abu.

Haka kuma kalmar siyasa kalma ce ta larabci aka arota zuwa harshen Hausa, ita kalmar siyasa ta samo asali ne daga ‘SASA’ ko ‘SULASI’. Kaga kenan wannan kalma ta “SIYASA” tana nufin Jagoranci, hikima, kiwo, horarwa da gudanarwa. Haka kuma ana amfani da siyasa yayinda wani abu na son zuciya ya shiga, amma wannan ba shine ainihin  kalmar ba. Ilmi yana da matsayi mai girma a tsarin siyasar kowace Al’umma. Daga kaarshe ina Addu’ar samun Nasara ga Matasa da suka tsaya Takara a kujeru daban daban, Allah ya tabbatar mana da Alkairi a Nigeria baki daya.

Matsayin Ilmi a siyasar Turai... masu ilmin falsafar Turai sunyi  ijma’i  game da muhimmancin Ilmi a siyasa. Plato yana ganin masu ilmi ne kadai suka cancanci su shugabanci jama’a, yayinda shi kuma  Aristotle yace A’a idan ana son siyasa ta inganta sai a baiwa jama’a  Ilmi. Shi kuma Spinoza cewa yayi amfanin siyasa shine ‘yanta Dan-adam da samar masa da Adalci, wannan kuwa bazai samu ba sai an bashi Ilmi. Shi kuwa Emanuel kant yana ganin rayuwa ce gaba daya sai da ilmi, yadda zaka kare lafiyarka, yadda zaka nemi Aure ka rikeshi, yanda zaka zabi shugaba.

Wasu mutanen su dauki ma’anar siyasa kamar wata kasuwa ce ta baje hajoji, inma a samu riba ko a samu faduwa. Irin masu wannan tunanin ne ake kira ‘yan siyasa marasa akida, domin su babu ruwansu da abinda ya dace illa abinda Aljihunsu ya dace dashi. Wasu kuma sun danganta siyasa kamar  dabi’a ce ta halittu masu rai aga uwa tana gaba ‘ya’yanta suna biye da ita, wato mai hankali shike shiga gaba domin na baya yayi koyi dashi.

Ismaila A Sabo
Ismailasabo@gmail.com

Sunday, July 29, 2018

TARIHIN SARKIN ZAZZAU JAFARU......

HADEJIA A YAU!




TARIHIN SARKIN ZAZZAU JA'AFARU....1936-1959.
Na rubuta wannan labari nawa don in bayyana godiya ta ga Ubangiji, kuma mutane kuga tsaunukan da na taka har na kawo ga wannan matsayi.

A cikin shekarar 1911, watau ina da shekara Ashirin da hudu (24) da haihuwa kenan, aka aika dani makarantar Dan-Hausa dake Kano. Na shekara guda acan na dawo gida. rannan ina zaune sai ga Shehu Baloha masinjan Joji, yace wai Joji yana kira na a Bariki. bayan naje sai naga Razdan ya dauki lambar Masinja ya lika mini a riga ta, yace "Yau ka zama Masinja" sai na durkusa nayi godiya. aka yanka mini albashin sule Talatin (30).

 Bayan nayi shekara uku ina wannan aikin sai rannan na roki Razdan ya maida ni makarantar Turawa ta Zariya, in rika koyawa 'yan makaranta Larabci.
Razdan yace "A'a wannan aiki bazai yi maka ba" saboda haka ya kai Magatakardar sa M. Kwasau can, Malami guda kuma Malam Umaru ya maida shi aikin Shanu, nikuwa aka game mini aikin su duka nake karbar Sule saba'in (70).

Ina cikin wannan aiki a cikin shekarar 1918 sai wani Hakimi na Zangon Katab ya taba kudin Jangali, aka fishe shi, ashe Allah ya nufa Sarautar a kaina zata fada, aka nada ni Hakimcin Zangon Kataf na koma can.

Sa'ad da nake Hakimi a wannan Kasa, naga abubuwan Tashin hankali guda biyu. wata shekara ina karbar Haraji sai Arnan Unguwar Gayya suka yi mini Tawaye. ina zuwa kauyen sai naji sun dauki kuwwa, nan da nan baka suka taru makil, kowa daga kwari sai baka a hannun sa, sai kayi tsammani wani abu ne yasa wannan bore. Dalili kuwa wai sun gaji da biyan Haraji ne kawai! Abu kamar wasa sai wani Arne wai shi Gankwan ya dana kibiya, yako duban ya sako mini ita. Sai ya kuskure mini ya samu Sarkin fada na a kafada. Yara na daga ganin haka sai suka yi kazam akan Arna! da Arnan nan suka ga bamu da Alamar tsoro sai suka bada baya, suka shige Kurmi gidan Tsafi.

Muka shiga garin muka tarar ba kowa, duk sun gudu mazan su da matan su. Na kira Sarakunan su da basu cikin tawayen, na gaya musu su lallashi mutanen su su dawo, babu komai. Washegari ni kuwa na yi zuwa Mabushi. A can na samu labari sun dawo sai shi Gankwan da ya harbi Sarkin fada na shine ba'a gani ba. Na aika ga Sarkin Zazzau Dalhatu da abinda ya faru duka, yace in kara matsawa kan neman Gankwan. Amma Ina? Ai har yau ba'a same shi ba, kamar an biya bashi dashi. Sarkin fada na kwanan sa wajen Arba'in a Mabushi yana jinyar daffin kibiyar nan.

Kai Arnan Zangon Katab a lokacin suna da wuyar sha'ani wajen al'amarin Haraji! Dubi wata shekara kuma da ni da wani Joji muna kama Awakin wadanda basu biya Haraji ba a Zankuwa, ba sai muka kama na wani wadda ya biya ba? sai gashi faram faram da matar sa suka zo suka durkusa suka ce mana "Wadannan Awaki namu ne, mu kuwa mun biya Haraji" Joji yace "To mu dai mun kama Awaki. Watau Makwafcin ka ya biya kenan, in ya samu kudi sai ya biya ka."
Da suka koma gida sai matar sa ta shiga zuga mijin ta na cewa "Allah wadan ka! Ashe dai kai ba Namiji bane? yaya don tsoron Sarauta zamu yarda a kwace mana Awaki? Ina ruwan mu da Makwafcin mu da zamu biya masa Haraji? Kai in baka dauki Kwari da baka ka tarad da Baturen nan ba, ina sa Wuta in kone su in kuma rabu da kai." Daga nan sai maigida ya dauki Kwari da baka ya tanka, 'ya'yan sa kuwa kowa ya dauko tasa, suka nufo wajen mu zasu tada Jihadi. Da na hango shi sai na daka masa tsawa sai ya yada Baka sai yazo ya fadi gabanmu yana haki. Na lallashe shi, na bashi magana sa'an nan ya koma. Ka ji tashin hankali da na hadu dasu lokacin ina Hakimcin Zangon Katab.

Na samu wannan Sarauta zamanin Sarkin Zazzau Aliyu ne, bayan shi aka nada Dalhatu. Daga nan sai Sarkin Zazzau Ibrahim ya kama Sarauta, shi kuma ranar 31/1/1937 ya rasu. Allah yaji kan su Amin. Bayan rasuwar Sarkin Zazzau Ibrahim, ina Hakimci a Zangon Katab sai ga waya ana nema na a Zariya, don Gwamna da manyan mashawartan Zazzau sun yarda in zama Sarki a shekarar 1936.

Madogara... Gaskiya Ta fi Kwabo ta 17. 1939.

 Daga nan sai na koma Zazzau da zama, muna rokon Allah da ya taimake mu rikawa Amin.

Sarkin Zazzau Ja'afaru shine dan M. Isyaku Sarkin Zazzau, dan Sarkin Zazzau Abdu dan Hammada. Allah ya masa rahma.