"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, February 2, 2020

TARIHIN GARIN GUMEL (TUMBI)... Kashi na daya.

HADEJIA A YAU!

         TARIHIN GARIN GUMEL

.
Asalin mutanen Gumel Barebari ne kuma sun fito daga garin Ngazargamu, Muhammadu shine ya fito da ‘ya’yan sa guda biyu, Danjuma da Adamu Karo. Dalilin fitar sa shi Dan uwan Shehu ne, to shehu yana da wani Doki wadda yake so kwarai har yasa aka ware shi daga cikin Dawakai aka masa gida daban. Shi kuma Muhammadu yana da  Godiya sai ya tsanantawa mai kiwonsa yayi mata baye, ana nan sai  godiya ta haihu ta haifi Dan Doki har ya girma ya fara hamimiya sannan sai Shehu yaji hamimiyar dan Dokin wannan , sai shehu yace “Duk inda Dokin nan ya fito dan Doki na ne” sai yayi kiran mai kiwon sa yace masa “In baka fada min wadda yayi baye da doki na b azan halaka ka” sai yace masa “Muhammadu ne ya tsananta min”,  sai Shehu yace to shikenan.

 To da Muhammadu yaji wannan zance sai ya tsorata ya gudu shi da ‘ya’yan sa biyu yazo wani gari da ake kira Nagalu kasar Shadiko, yanzu tana cikin Jamhuriyar Nijer. Yana nan sai Shehu ya aika masa cewa ya koma gida ba komai, sai Muhammadu yace “NA ATIMA DIGAIYE” Wai Anan na fita. To saboda waccan kalma da ya fada shine har yanzu ake kiransa da Diga Diga kakan Mangawa. To daga Nagalu da Shehu ya aiko ya koma har yau sai ya bar nan ya tashi ya koma Babaye don yayi Noma, daga nan sai suka taru suka yi shawara a Dogoma ya kamata ayi Shugaba, sai Muhammadu yace a yiwa Adamu Karo bubban dan sa, shine ya fara sarauta a Dagoma suka zauna gari ya zama nasu suka shekara uku, daga nan Adamu Karo ya tashi zuwa yaki kasar Kano sai Fulani suka harbe shi da kibiya a wani gari da ake kira Kanebu sai ya rasu.
Sai aka dawo gida aka nada kaninsa Danjuma yayi shekara goma sha bakwai yana sarauta sai ya rasu, sai aka nada dan Adamu Karo Muhammadu Mai Kota, sai suka tafi wajen Shehun Barno don ya basu Tuta, sun karbi Tuta a hijira ta 1781. 

Shi Muhammadu Mai Kota shine ya fara karbar Tuta, dalilin da yasa ake ce masa Mai Kota shine bayan ya karbi Tuta a Barno sai ya koma Sokoto wajen Sarkin Musulmi don ya bashi Tuta, to Sarkin Musulmi yasan akwai Tutar Shehun Barno a hannun sa sai yace dashi;- “Sai ka koma wadda aka min izni in bayar ta kare” Sai yayi Addu’ah a jikin Kota ta Noma ya bashi yace kaje da wannan ba kai ba duk Sarkin da za’ayi in Damina tayi ya karta wannan Kota ko da sau biyu ne, in da duk Duniya za’a yi yunwa to kasar sa baza su yi ba. To saboda wannan Kotar sai ake kiransa Muhammadu na Kota, kuma wannan Kotar tana nan har yanzu a gidan Sarautar Gumel.

Muhammadu na Kota ya shekara Ashirin da bakwai (27) yana Sarauta ya rasu, sai aka nada Dan sa Muhammadu Kalgo yayi shekara Hudu (4) yana sarauta sai wani Barawo da ake kira  Barjo ya biyo dare ya kashe shi. Sai aka tafi Barno aka nadaMuhammadu Dan Auwa, ya shekara Goma sha bakwai yana Sarauta kuma Jarimi ne domin ya shahara wajen yaki. Ya sha kaiwa hari kasar kano yana cinye musu kauyuka, har ma mai wakar Bagauda yana cewa “Da Tumbi da Washa sun ga banza sun hada kai suna dibar kanawa, sannan sun tashi daga Dagoma sun dawo Tumbi”  A lokacin mulkin sa kasar Kano suka yi ta kawo chaffa wajen sa, tun daga Dutse Gadawur suke kaiwa haraji har Tumbi.

Lokacin da Shehu Laminu ya samu labarin cewa Muhammadu Dan Auwa yayi karfi duk sararin nan babu kamar sa, ko shi zuwa gaba zai fi karfin sa. Sai Shehu Laminu ya aiko Dan Auwa yaje yana neman sa, sai Dan Auwa yaki zuwa har saida Shehu Laminu yah au da kansa yazo wani gari da ake kira BARMARI, kasar Yalawa tsakanin su da Tumbi bai fi Mil Bakwai ba (7) inda Dan Auwa yake. Da Shehu yazo wannan gari sai ya aika Dan Auwa yazo, duk da haka sai yaki zuwa yace a fadawa Shehu yazo nan Tumbi ya same shi domin in yazo nan babu yadda zai yi dashi, amma in shine yaje to Uban dakin sa ne sai yadda Shehu yayi dashi. 

Sai Shehu ya hada Dabara da Malamai na cikin garin Tumbi yace “Ku sani zan je Tumbi amma duk abinda ya faru ku sani yaki tsakanin Musulmi da Musulmi babu kyau, ku fadawa Dan Auwa gaskiya yazo” sai wani Malami daga cikin Malaman Tumbi yaje gaban Dan Auwa ya rantse da Alqur’ani cewa  in ya kais hi gaban Shehu zai tashe shi ya dawo gida, sai Dan Auwa ya yarda suka tafi gaban Shehu Laminu. Da suka je gaban Shehu sai Malamin ya tashi Dan Auwa a tsaye yace masa “ Kamar yadda na maka rantsuwa zan tashe ka to na cika Alkawari, sai Malami ya tafi ya bar Dan Auwa da Shehu Laminu. Bayan sun kama Dan Auwa sun rasa yadda zasu yi su kashe shi, sai Dan Auwa da kan say ace a samo mazagin wando a shake shi dashi. Haka kuwa aka yi suka samo mazagi suka shake shi ya mutu, sai kuma Shehu yasa aka yanka Sa aka fede shi aka dauki fatar aka saka gawar Dan Auwa a ciki aka nade aka jefa a Kogi, tun daga wannan lokacin kogin ya daina kawowa Ruwa.

Dalilin tsagen fuskar Gumelawa kuwa Muhammadu Dan Auwa ne ya Auri wata ‘yar Sarkin Washa da ta haihu sai ‘Yanuwan matar suka ce sai ayiwa yaron tsage irin nasu, to wannan tsagen an same shi ne daga Washa. Bayan Shehu Laminu ya kama Dan Auwa ya kashe shi sai ya nada kanin sa  Muhammadu Dan Tanoma a sarautar Tumbi.

Bayan Muhammadu Dan Ta Noma ya shekara Tara (9) yana sarautar Tumbi sai yaso yayi gidan gona, sai ya fadawa Malaminsa sai Malamin yayi rubutu yace a baiwa Godiya tasha duk inda tayi fitsari to anan za’ayi. To anan Gumel kusa da fada Duhuwa ce da wata Saniya ta gawurta ta zama kamar Bauna take tsare mutane, ana kiran Saniyar da suna Gumale. Sai Dan Tanoma yasa aka je aka kashe Saniyar sannan aka tafi da wannan Godiyar, da tazo kusa da wurin wani zuwo sai tayi fitsari. Sai mutanen da suke biye da ita suka ce “LAU TAYI” ma’ana sunan Godiyar Lau, wannan shine dalilin da ake cewa Gumel Lautai. Da aka zo aka fadawa Sarki sai ya tambaya a ina da inda aka kashe Gumale tayi? Sai suka ce masa a gabas da wurin ne kadan, wannan shine dalilin da yasa ake kiran garin da suna Gumel. Zamu kawo muku kashi na biyu.

Madogara...  
Assessment report on Gumel Emirate 1916.
Eap.bl.uk/Archive-file EAP087-3-24.
Gado da Masun Gumel. 


Tuesday, September 17, 2019

DAMA CE KAWAI.... Dr. Nuruddeen Muhammad

HADEJIA A YAU!

Labarin Rayuwata

Dama ce kawai...! Dr. Nuruddeen Muhammad. 

Ma'anar Dama itace "wani lokaci ko wasu jerin al’amura da kan yi dalilin faruwar wani abu."

Rayuwata gaba d'ayanta labari ne na damarmaki wanda ke sanya fata da karfafa zuciya. Wadannan damarmaki sun kasance da iznin Allah mad'aukaki tamkar wata fitila ce da ta haskaka mini tafarkin rayuwa na zama duk abunda na zama.

Dacewa da samun wad'annan damarmaki, da kuma amfani da su a lokutan da su ka bijiro, shine dalili da kuma matakin dagowata daga tsukun yankin mahaifata a Hadeja, Jihar Jigawa, arewa maso yammacin Najeriya, inda ya kaini zuwa madaukakan wurare kamar ofisoshi da d'akunan taron Majalisar ‘Dinkin Duniya da ke birnin New York na k'asar Amurka da kuma dukkan nahiyoyin da ke fadin wannan duniya.

Babbar dama ta farko a gareni ita ce ta samun mahaifi irin wanda Allah ya azurta ni da shi (Mallam Muhammad Adamu UNIK), jajirtaccen malamin makaranta kuma Hedimasta da ya shahara kan gaskiya da rikon amana da kuma aiki tukuru. Malam ne ya fara cusa min ak'idar sanin darajar ilmi da maida hankali a kan aiki, tare da nusar da ni kyawawan dabi’u na rayuwa irin su: gaskiya da rik'on amana, hak'uri da juriya, karfin hali, sanin darajar d'an adam, fin k'arfin zuciya, tausayi, da kuma uwa uba, ya dasa min ginshik'in tsoron Allah a zuciyata. 

Wannan Damar dai ita ce ta ingantaccen ilimin da na samu  k'yauta a makarantun gwamnati (tun daga makarantar firamare ta unguwa zuwa sakandaren yanki, jami'a da kuma k'ololuwar mataki na karatun aikin likita. Karatu, tarbiyya da kuma jajircewa su ne dai ta hanyar da Ubangiji ya d'aukaka Nura ya koma Dakta Nura a yau.

Dama ce bud'e ido da na yi da wuri akan harkokin siyasa na gane yadda ake gudanar da ita, a inda na fahimci tasiri ko k'arfi na tarayyar jama'a a karkashin wata manufa guda idan aka yi amfani da shi wajen yad'a ak'idar da za ta amafanar da daukacin al'umma, musamman bangaren talakawa.

Babbar Dama ita ce da Allah (SWT) ya had'ani da Dr Sule Lamido, wanda ya gano wad'ancan halaye nawa, da tarbiyya, da karatu, da kuma bibiyar siyasa, ya gamsu da su, sannan kuma ya ci alwashin sarrafa su. Shine dai sanadiyyar da ta kai ni can k'ololuwar  gwamnati ina matashi d'an shekara 34 kacal, inda a gefe daya na san maza kuma maza su ka san ni, amma kuma a wani gefen na gane cewa duniyar nan fa ba komai ba ce face wani yanayi na k'ank'anin lokaci.

Ba komai ba ne face Dama ta jawo min yabo da girmamawa daga shugabannin k'asashe, manyan jami'an difilomasiyya da siyasa, fitattun shugabannin al'umma,  hamshak'an ‘yan kasuwa da kuma y'an uwana likitocin da na samu dacewar yin gogayya da su, kuma Allah ya ba ni damar nuna musu kokari da jajircewata ta ganin na kai gaci a duk wani al’amari da na sa a gaba ko kuma duk wani aiki da aka sanya ni.

Babbar tambaya a nan ita ce, ta ya ya wani matashi marar gata a sama, wanda ya fito daga arewacin Nijeriya, yankin da miliyoyin ‘ya’yan talakawa irinsa su ke rasa makomar rayuwa tun suna ‘yan kasa da shekaru 10, ya zama Ministan Najeriya ma fi k'arancin shekaru tun bayan dawowar mulkin damokirad'iyya a kasar a 1999, k'wararre a aikin likitanci, gogagge a harkar diflomasiyya, kuma har ya taka rawa a harkokin siyasar al'ummarsa, a k'asar da samun irin wannan tagomashi sai ‘yan tsiraru, masu uwa a gindin murhu??!
..... Amsar dai mai SAUK'I ce!!...

Alhamdulillah... DAMA CE KAWAI!!!

Sanin da na yi cewa, ba dan wad'annan damarmaki da na samu a rayuwata ba, da kuwa ni ma zan iya shiga kowane irin hali, shine babban k'aimin da ya sanya na yi tunanin kafa wannan Gidauniya ta Unik Impact (www.unikimpact.foundation). Ita dai wannan Gidauniya tamkar wani dandamali ne na yi wa al'umma, musamman 'yan uwa matasa, kokarin samun dama a rayuwa ta hanyar bayar da tallafi ga harkokin ilminsu, tattalin arziki da kiwon lafiya, har ma da inganta muhallinsu. Sannan da yi musu jagoranci bisa sanin muhimmancin ilimi da kuma rungumar dabi’un kirki irin su: jajircewa a kan aiki, gaskiya da rik'on amana, fin k'arfin zuciya da kuma nuna tausayi ta hanyar yi wa al’umma hidima da taimakon na kasa.

Babban burin wanna Gidauniya shine tarairayar zukatan matasanmu da d'ora su a kan tafarkin samun d'aukaka da cin nasara a rayuwarsu. Idan har ni zan sami irin wannan d'aukaka, to a cikin ikon Allah kowa ma zai iya samun irin ta, ko sama da hakan  ma idan ya sami dama.

Hakika tarbiyya ce, da kuma karatun da duniya ta koya min, su ka ganar da ni cewa, d'aya daga cikin hanyoyin da mutum zai nuna godiya a bisa ni'imomin da Allah ya yi ma sa, shine, shi ma ya yi sanadiyyar samun dama ga wasu. Ta haka ne kawai zamu yi tunanin gyara al'ummar nan; ko da kuwa a sannu sannu ne.

Wani k'wararre da na yi aiki tare da shi, ya ta6a yi min tambaya cewa ya ya na ke hangen wannan Gidauniya ta Unik Impact a cikin zuciyata?... sai na amsa masa da cewa:

"Kamar gungu ne na wasu mutane da  Allah ya bai wa Dama a rayuwa  inda su ma su ke k'ok'arin ganin wasu da yawa sun sami irin wannan damar."

Hausawa dai su kan ce: ‘Yi wa wani, yi wa kai....’