"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, October 8, 2016

GALADIMAN HADEJIA USMAN.....Daga Suleiman Ginsau.




NAZARI AKAN TARIHI DA RAYUWAR GALADIMAN HADEJIA ALH. USMAN ABDUL'AZIZ. (USMAN II)

(TARE DA SULEIMAN GINSAU)

"SALSALAR HAIHUWA DA KARATUN GALADIMA"

Kamar yadda yake a bayyane an haifi Mai Girma Galadiman Hadejia Alh. Usman Abdul'aziz a cikin garin Hadejia da ke Jihar Jigawa a ranar 23 ga watan Oktoba a shekara ta 1959, wadda yayi dai-dai da 20 ga watan Rabi'ul Sani na shakarar ta 1379. Idan muka dubi rayuwar Galadima a bangaran karatunsa ya halarci Makarantar Hudu Islamiyya dake garin Hadejia a shekarar 1963, ya halarci Makarantar Firamare ta Hadejia Central a cikin shekarar 1965-1971, inda daga nan kuma ya wuce zuwa Kwalejin Geamnati dake Kano wadda a yanzu ta koma Rumfa Kwalej a shekarun 1972-1976, a matakin sakandare daga nan kuma ya wuce Makarantar koyan sana'a dake Kaduna (Kaduna Polytechnic) anan ne ya yi karatunsa na Karamar Diploma ckin shekarun 1976-1979. Yayi Babbar Diploma akan kasuwanci a (Kaduna Polytechnic) cikin shekarun 1979-1981. Yaci gaba da karatunsa a Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa Bauchi a Shekarun 1997-1998 ya sami shaidar Babbar Diploma ta gaba da Digiri a kan kasuwanci, daga nan ya wuce kasar waje domin karo Ilmi inda ya shiga Jami'ar St. Clements da ke kasar Australia a shekarun 1998-1999 a inda ya samu shaidar Digiri na biyu a bangaren Kasuwanci, daga nan ya sake komawa Jami'ar Tafawa Balewa dake Bauchi domin cigaba da karatunsa a inda ya sake samun shaidar wani Digirinsa na biyu a kan kasuwanci na komai da ruwanka wato ( General) a shekara ta 2000-2001. Mai Girma Galadima Usman Abdul'aziz ya yiwa kasa hidima a Jihar Binuwai. daga shekara ta 1981zuwa1982 (Taskar Suleiman Ginsau)



"RAYUWARSA TA AIKI"

Bangaran Rayuwarsa ta aiki kuwa abin abin sha'awa da ban mamaki Mai Girma Galadiman Hadejia Alh. Usman Abdu'aziz ya fara aiki ne a ma'aikatar Ciniki da masana'antu ta tsohuwar Jihar Kano a shekara ta 1982, a matsayin jami'i mai kula da bangaren ciniki.

"AIKIN GALADIMA A KAMFANIN TOTAL"

Daga nan ya kama aiki da Kamfanin Mai na Total a matsayin wakili mai kula da harkokin kasuwanci a watan Augusta na shekarar 1983, bayan samun horo da yayi a Hedikwatar Kamfanin da ke birnin Lagos, daga nan an yi masa canjin aiki zuwa Jihar Kano a matsayin jami'i mai kula da harkokin kasuwanci.

Bayan dawowarsa Kano ansake yi masa canjin aiki zuwa Jihar Barno a shekarata 1988 a matsayin wakilin harkokin kasuwanci mai kula da shiyyar Arewa maso Gabas na Kamfanin Mai na Total. Kasancewarsa a wannan shiyya ya bada gagarumar gudunmawa wajen cigaban wannan Kamfani, hakan ne ya sanya aka sake yi masa canjin aiki zuwa sabon ofishin da aka bude na Kamfanin a Jos, hedkwatar Jihar Filato a matsayin Manaja mai kula sha'anin kasuwanci, zamansa a Jos ya gudanar da ayyukan da suka kai Kamfanin ga samun nasara, a inda aka daga darajarsa a wannan shiyya, hakan ta sa aka kara ciyad dashi gaba aka bashi Manajan kula da kasuwanci a shiyyar Arewa maso Gabas, a shekara ta 1996. A lokacin da yake gudanar da ayyukansa a wannan shiyya a Jos bayan ci gaban da na bayyana mai dorewa ya samar ta fuskar habaka kasuwancin Kamfanin. Lallai Galadima ya tabbatar wa Duniya cewa shi tsayayye ne wanda yasan harkokin kasuwanci bisa gaskiya da rikon amana.

Har ila yau kwarewarsa ce ta sa aka sake karama masa mukami zuwa Manajan yanki wanda ya kunshi Jahohi kamar su:-
1. Bauchi
2. Gombe
3. Barno
4. Yobe
5. Adamawa
6. Taraba
7. Filato
8. Nasarawa
9. Binuwai
10. Kogi
shedikwatar tana nan a matsayinta a Jos. 



A shekara ta 2001 lokacin da Kamfanin Mai na Total da na ELF suka hade an sami canje-canje inda aka kirkiro sabon Ofis mai kula da Arewa mai nisa dake da shedikwata a Kano, tare da nada Galadima a matsayin Manajan shiyya mai kula da Jihohin da suka yi iyaka da kasashen Republic of Benin, Niger, Chad da Cameroon kamar haka:-
1. Kebbi
2. Sakkwato
3. Zamfara
4. Katsina
5. Kano
6. Jigawa
7. Yobe
8. Barno
9. Adamawa
A shekarar 2006 an kuma yi masa canjin aiki zuwa birnin Benin a matsayin Manaja mai kula da shiyyar yamma ta tsskiya. Kamfanin Total ya kirkiro Ofishin kasuwancin Najeriya a Abuja wanda aka bawa Galadima Manajan wannan Ofis mai kula da shi a shekara ta 2008. (Taskar Suleiman Ginsau)

"AIKIN GALADIMA A KAMFANIN MAI NA NNPC"

Dangane da irin gagarumar gudun mawa da jajircewar sane tasa, daga bisani aka yi masa canjin aiki zuwa Kamfanin NNPC a shekara ta 2012 lokacin da Kamfanin na NNPC ya nemi Kamfanin Total da ya basu shi don ya taimaka wajen canja akalar tafiyadda kamfanin NNPC Retail yadda zai yi daidai da sauran manyan kamfanonin mai na kasuwanci irin su TOTAL.

A yayin zamansa a Kamfanin NNPC na kasa ya samar da ci gaba ta fuskar samar da kudaden shiga masu tarin yawa, ya samu nasarar bude kananan gidajen Mai shiryawa tare tabbatar da tsaftace kasafin kudaden Kamfanin, Galadima ya samar da ci gaban Kamfanin NNPC Retail tare da inganta harkokin kasuwanci a matsayin Janar Manaja mai kula da saye da kasuwanci a karkashin NNPC Retail Ltd, a Abuja cikin watan Maris na 2012.

Haka kuma Kamfanin NNPC ya sake ba shi mukami Janar Manaja mai kula da tsare-tsare da dabarun aiki cikin watan Maris na 2013 a dai karkashin NNPC Retail Ltd.

"A JIYE AIKIN GALADIMA"

Alhamdulillah mai Girma Galadima ya yi aikinsa cikin koshin lafiya tare rikon amana da gaskiya wanda hakan ya bashi damar ajiye aikinsa cikin walwala da jindadin, Galadima ya ajiye aiki don kashin kansa a shekara ta 2014, inda ya kafa Kamfaninsa mai suna ENCEE BUSINESS SERVICES, wanda yake gudanar da shawarwari da horo kan yadda za'a bunkasa harkokin kasuwanci Mai da Iskar Gas...

Galadima yana da matan Aure guda biyu da 'ya'ya Goma... Ina mai addu'a agareshi Allah ya tayashi riko, Allah ya daukaka wannan Masarauta ta Hadejia.

Tsarawa
ISMAILA A SABO


Mai Nazari
SULEIMAN GINSAU
Association Of Nigerian Authors (ANA)

Monday, October 3, 2016

TSARIN ZAMAN JAMA'A DA TATTALIN ARZIKI A KASAR HADEJIYA KAFIN ZUWAN TURAWAN MULKIN MALLAKA. (Kashi na 1). Daga Suleiman Ginsau...









Kasar Hadejiya tana da kabilu daban daban, amma duk da haka wannan masarauta a cure take a waje daya. Addinin Musulunci shi ne ya dada hada su da kuma harshen Hausa wadda suke magana da shi a matsayin harshen kasa. Babu wata tababa cewa Addinin Musulunci shine Addinin da mafi yawan jama'a suke bi a wannan masarautar ta Hadejiya. Ka'idoji da dokoki da hukunce-hukuncen Musulunci su ne suke tafiyar da rayuwa da ayyukan mutanen wannan kasa. Addinin Musulunci ya hada kan jama'a kuma ya samar da hanya madaidaiciya ta zaman al-umma. Ta hakane Musulmi masu rinjaye da wadanda ba Musulmi ba marasa rinjaye mazauna kasar Hadejiya kafin mulkin mallaka suna ganin sarkin Hadejiya nada mutukar kima kuma shugaba ne babba duk da yake suna da hakimai da dagatai wadda suke jagorancinsu, Mutanen Hadejiya sukan hadu a kowace shekara su gudanar da bukukuwan Sallah karama da Sallah babba a Hadejiya.

Ta haka al'ummar Hadejiya take cudanya da juna cikin walwala, farin cikin, nishadi, jindadi da annashuwa da sakin fuska. Kuma bisa dukkan alamu, kabilun da suke zaune a Hadejiya sun shiga juna, za'a taras bisa asali, Bahaushe, Bababbare ne, ko Bamange, ko babade, ko kuma bafulatani. Haka dai kabilun kasar Hadejiya suka sarki juna.

Jama'ar da ba Musulmi ba suna karkashin kariya ta wannan masarauta, amma su kuma suna bayar da jizya. Al'adun Hausawa/Fulani Hadejiya suna da babban tasiri na mutanen Gabas wato al'adun Barebari. Akwai misali da yawa da za a iya bayarwa a kan haka, kauki misalin sunayen wasu mukaman sarautu kamar Zangoma da Bulama da Kacallah da Maina (dan Sarki) duka daga wajen Barebari a ka samo su.

Hatta ma bikin Sallar maulidi ana gudanar da shi ne dai-dai yadda Barebari suke yi. Ashe ke nan al'adun Barebari sun yi tasiri. (Sulaiman Ginsau )
Kari a kan wadanan kyawawan huldodi na mutanen Hadejiya a tsakanin junansu, tsarin da masarautar ta bi wajen tafiyar da al'amuranta na mulki ya dada kara wannan dankon zuminci. Tun daga farkon kafuwar daular, Sarkin Hadejiya Malam Sambo ya dora kowace kabila daga cikin kabilun kasar a kan wani mukami na sarauta. Wannan tsari da aka ci gaba da aiwatar da shi, ya sanya jama'ar kasar sun zauna a dunkule tamkar tsintsiya domin kowace kabila ta san tana da wakilci a majalissar wannan masarauta.


Ta fuskar tattalin arzikin kasa kuwa, Hadejiya tana da yalwataccen arziki tare da sana'o'i da masana'antu iri-iri, duk da yake harkokin noma sunfi daukar kaso mai yawa. Magidanci shi ne tushen arziki a tsarin zaman jama'a tare da iyalansa a matysayin masu taimakawa. Talakawa sun tsayu sosai wajen yin noma na lokacin damina da noman fadamu a lokacin rani, sannan kuma kamun kifi da kiwo sun zama ruwan dare a tsakanin mazauna kasar Hadejiya. Amfanin gonar da aka fi nomawa sun hada da:-
1. Gero
2. Dawa
3. Shinkafa
4. Wake
5. Masara
6. Gyada
7. Auduga
8. Alkama
9. Ridi da Kankana
10. Rake da sauran kayan lambu kamarsu Timatir da Tatttasai da Taruhu da Rake da sauran kayan lanbu ana noma su ne ta hanyar noman fadama a lokacin rani. Kasar Hadejiya, kamar sauran kasashen wannan nahiya, tana da kyakkyawar kasar noma Gero da Kiwon Dabbobi. Har wa yau kuma wannan yanayin wuri ne mai albarka ya ba da damar aiwatar da wasu sana'o'I kamar su Rini da Saka da Kira da Ginin Tukwane da Jima da Dukanci da Gini da sauransu.


A bangaren saka kuwa kauyen Bangelu wanda yake tsakanin Auyo da Hadejiya ya shahara sosai wajen saka da dinka Rigar Bullamai tare da sauran Rigunan Saki Fari masu inganci. Haka kuma kauyen Hadejia ya yayi suna a sana'ar Rini. Mutanen Hadejiya da suke zaune a daura da kogin Hadejiya sunyi fice a sana'ar Su ta kamun kifi. Haka kuma dajin Hadejiya cike yake da kudan zuma inda ake samun zuma mai tarin yawa. Diban zuma ya zama wata sana'a mai riba ga jama'ar kasar Hadejiya musamman yadda take tallafawa wajen warware matsalolin rayuwar yau da kullum.

Bugu da kari mutanen Hadejiya kamar sauran wurare, sukan sayar da amfanin gona wanda ya yi rara, ta haka suka shiga hada-hadar kasuwancin amfanin gona daga cikin hanyoyin da suka kara habaka Tattalin Arzikin Kasar Hadejiya kafin zuwan turawan mulkin mallaka. Ta wannan hanya masarautar Hadejiya ta zama wata cibiya kuma muhimmiyar mahada ta cinikin kayan amfanin yau da kullum a gabacin kasar Hausa a karni na sha tara (K19). Masarautar ta yi fice wajen fitar da kayayyakin abinci kamar Alkama da Kifi zuwa Kano da wasu wurare, ita kuma sai ta sayo Goro da makamancin abubuwan da masarautar take da bukata. Kamar yadda aka fada a baya, mutanen Hadejiya na kasuwancin Rigunan Saki ko Rigunan Fari da Zuma da Kiraga wato (Fatu) da Shanu, su kuma su sayo Gishiri da Dawakai da Kanwa. Ana kuma jin cewa Hadejiya ta zama wata hanya ta fatauci na fataken da suke ratso Sahara zuwa Kano ta yamma da kuma Barebari da Larabawan Fezzan da Azbinawa da Buzaye daga gabas da kuma yamma. Wadannan fataken sukan hadu a kasuwar Hadejiya su gudanar da harkokin cinikayyarsu na kayayyaki kamar Rigunan kano da kanwa da Shanu da Bayi da kayan Yaji (Sulaiman Ginsau).

A wannan lokacin da ake Magana, a Hadejiya akwai manyan kasuwanni guda biyu (2) daya kasuwar an yi ta a wajen ganuwa, an kakkafa rumfunan da kuma masaukai na baki wadanda aka yi don samar da wuraran zama da jin dadin fatake da sauran yan kasuwa. A cikin ganuwa ta birnin Hadejiya akwai wata kasuwa wadda take kula da bukatun mazauna birnin Hadejiya da makwabtanta. Wannan ya nuna cewa bayan kasancewar Hadejiya cibiyar mulkin da ayyukan jin dadi jama'a, haka kuma tana matsayin ingantacciyar cibiya ta kasuwanci. Wannan kasuwa tana karkashin kulawar Zangoma wato Sarkin kasuwa. Zangoma shi ne yake karbar dukkan haraji na wannan kasuwa tare da masu taimka masa.
A dunkule, wannan yayi bayanin Hadejiya a matsayin masarauta ta mulkin jihadi da kuma fito da tsarin zaman jama'arta da tattalin arzikinta kafin mulkin mallaka na turawan ingilashi a kan daular Usmaniyya ta Sakkwato.

An kuma nuna cewa a fanning Siya sa, Hadejiya gari ne na 'yan Boko da 'yan siya sa masu yawan gaske kuma Hadejiya garine na kasuwanci wadda hakan ya sa mutane suna zuwa siyan kayayyaki daga gurare daban-daban, sannan masarautace mai karfi a tsakanin masarautun da suke gabacin kasar Hausa, musamman yadda take tsoma baki a harkokin cikin gida na makwabtan ta.

Haka kuma nayi wai-waye ta fuskar tsaro ya bayyana cewa Hadejiya kasace jaruma kuma karshen karni na sha tara (K19) sai ta zama kasa mai kyakkawar huldar dangantaka da zama na lumana da abokan taka da sauran masarautu. (Sulaiman Ginsau)

Muhadu a kashi na biyu 2

Friday, August 12, 2016

SARKIN HAƊEJIA ABUBAKAR MAJE HARUNA (1984-2002).



Bayan rasuwar Sarkin Haɗejiya Alhaji Haruna sai aka naɗa Ɗansa Alhaji Abubakar Maje Haruna a matsayin Sarkin Haɗejiya na goma sha biyar (15), A jerin sarakunan Fulani, an naɗashi ranar Juma'a 31st/august/1984. Sai akayi Sarki mai farin jini da hakuri da son mutane, a wajen kyauta kuwa ya kasance mai Alheri tun yana ƙaraminsa. Sarkin Haɗejiya Abubakar kafin zamansa sarki yayi Ayyuka da dama, sannan ya kasance Ɗan kasuwa.

A zamaninsa an samu sauye sauye da dama a ƙasar Haɗejiya, musamman Ɓangaren Ilmin Addini dana zamani Kasuwanci da siyasa. Sarkin Haɗejiya Abubakar Maje ya halarci makarantu da dama inda ya fara halartar makarantar Elementary dake Unguwar Dallah a shekarar 1945, sannan ya tafi makarantar Middle School dake Unguwar fantai a shekarar 1949 zuwa 1952. Haɗejia A yau.

Sarkin Haɗejiya Abubakar ya tafi makarantar T.T.C. Maru dake a Lardin Sokoto a wancan lokacin, ya fara a cikin shekarar 1953 zuwa 1956. Sarkin Haɗejia Abubakar ya koma makarantar horar da ma’aikata dake Potiskum ta jihar Borno, wadda yanzu take a jihar Yobe. Kuma ya fara aikin gwamnati a matsayin Malamin Hakimi a Gundumar Bulangu, sannan ya riƙe muƙamin Magatakarda a majalissar Sarki. Saboda iya mu’amala da son jama’a sai yazama duk inda ka ganshi bazaka ganshi shi kaɗai ba sai da jama’a, hakan ya bashi nasarar gogewa wajen tafiyar da shugabancin jama’a. Haɗejia A yau.

A zamaninsa an samu ci gaba da yawa a ƙasar Haɗejia ta kowane fanni na rayuwa, musamman zaman lafiya da Kwanciyar hankali, sannan an samu bunƙasar garin Haɗejia wajen gine ginen zamani da gina sabin Unguwanni. A zamaninsa aka rushe ƙofar Garin Yamma da ta Arewa aka Gina sabi domin dacewa da zamani sannan aka sake gina Sabi guda uku, an gina ɗaya a Kusa da Kadime ɗaya kuma an ginata a hanyar Gumel da kuma hanyar Nguru. A zamaninsa an gina sha tale-tale (Round about) guda biyu ɗaya a yamma da kofar garin yamma, ɗaya kuma a Titin Tashar mota tsohuwa, sannan anyi sababbin hanyoyin mota a ciki da wajen Haɗejia. A zamaninsa....... Hadejia A yau! A duba littafin Fulani da mulkinsu na Ismaila A Sabo.
posted from Bloggeroid

Saturday, July 30, 2016

HADEJIA TOWN WALL AND GATES...

HADEJIA A YAU!BY: SULEIMAN GINSAU


HADEJIA TOWN WALLS AND GATES
"Hadejia was a large town with 5 town gates and excellent walls about 30ft (9. 14m) high, and 30ft(9. 14m) thick " ... (Captain Philips 1909) Hadejia Town walls had a long history dating back to the pre-jihad period. The walls were built to provide security to the people, and to serve as fortification against external invasion. Though mostly in ruins now, with a great proportion having completely disappeared, the walls were
intact up to the time of the colonial invasion in 1906.The construction of the walls was done by direct labour using local building materials. Over the years, the walls have been taken subjected to
several phases of development. 

Expansions and reinforcements were made to accommodate a growing population or to enhance security against attack by powerful enemies. The walls were invariably complimented by gates whose history could be linked to that of the walls. The gates provided the only entry points into the town. They
were made extremely strong, thus making it very difficult for an enemy force to break into the town through them. The gates were manned by
gate-keepers or porters (sarakunan kofa)
appointed by the Emir. These keepers used to close the gates everyday from dusk to dawn, thus controlling the movement of people in and out of the town during these periods. Visitors or
strangers were not allowed in unless with the express permission of the Emir. It was reported that one Emir ordered the gates to be left open permanently, confident that no enemy force would dare attack the town.

The first town wall in Hadejia was believed to have been built during the pre-jihad period. Though the exact date of its construction cannot be determined due to lack of proper records, its
perimeter is marked by certain well-known local pits: Mai kilabo in the west, Atafi in the south, and Dallah in the East.

 It was said to be one mile in circumference, and had four gates. The second wall was built by Sarki Sambo in the early years of the Jihad. It was wider than the previous wall,
with its perimeter approximately put at 2 miles 170 yards. It had 5 gates. The present wall, which was the third, was also built during Sambo's reign. It was built at a time when Hadejia was at
the centre of a bitter rivalry between Sokoto caliphate and Borno Empire. As such it was much stronger and wider than the previous walls. An extension to this wall was later made on the
Eastern side during the reign of Sarki Haruna (1865 -1885), encompassing a large space to harbor fugitives from surrounding villages in times of war. The Habe settlement of Fantai, which hitherto was outside the wall, also became sheltered in the new extension. This brought the wall to its present size of 4 miles 135 yards, with 5 gates, namely:
Kofar Gabas (also known as Kofar Gwani),  Kofar Arewa, KofarYamma
Kofar Kyalesu (also Known as Kofar Kogi), Kofar Mandara (also known as Kofar Talata). Apart from the Kofar Mandara gate, which was destroyed by the British in their attempt to gain
entry into Hadejia town in 1906, the other gates are still standing in their original positions. They have, however, undergone several modifications
over the years, the latest being in1985 which saw the total re-construction of Kofar Arewa and Kofar Yamma. The Hadejia town gates now stand as
historical monuments rather than as security outposts.
BY: SULEIMAN GINSAU

Friday, July 29, 2016

A SHORT HISTORY OF GARUN-GABAS.. (BIRAM)


Garun-gabas generally recognised as the ancient Biram, i believe and Bagdaza to be Baghdad. The legend in another form is connected with that of the Origin of the Hausa Bakwai. Mukhtar or Bayajidda was compelled to flee Bornu with his wife, on his Journey west he left her on the road and she gave birth to Biram who founded Garun-gabas. Bayajidda continued his journey to Daura where the well known encounter with the Snake took place and Bayajidda's marriage with the Queen Daurama.

The Town was founded by Arabs from Baghdad, one Mukhtar and his younger brother Biram migrated West and came to Birnin Bornu (Kukawa). The Shehu of Kukawa gave Mukhtar his daughter in marriage and the town of Kulunfardu where he lived until his death. Biram and his younger brother then migrated further West and founded Garun-gabas.

The following is a list of Chiefs of Garun-gabas.
1. BIRAM

2.BOMI... One of the Biram's follower who came with him from Kulunfardu but no relation.

3. TUNKU... Also one of the Biram's followers. The length of time for which these three held the Sarauta unknown.

4. ABDULLAHI. Called Ajab... He ruled for three days and then miraculously disappeared.

5. ASAWA... Thirty years the grandfather of the present Sarkin Gabas, he was deposed by Sambo Diginsa the first Fulani Emir of Hadejia, on account of his son was murdered.

6. MUSA... Nephew of Asawa Eleven years, appointed by Sambo.

7. GAUYAMA... Not of the ruling family fourty years, half way through his reign he became blind.

8. BARWAI... Younger brother of Sambo, Nine years.

9. USMAN... Son of Barwai, Six years he then Emigrated to Shira.

10. GABDO... One year and Emigrated to Katagum. Hadejia A yau.

11. BURMI... A fulani, one year fled to Katagum in terror of Buhari.

12. SARKIYO... One of the Buhari's "Hakimi" Ten years, Buhari then died and was succeeded by Umaru who remove Sarkiyo to Hadejia and made him Barwa.

13. MUHAMMAD BAKO... Son of Asawa and thus descendent to the Original Arab founders, Appointed by Haru Bubba. He held the Sarauta for Two years and then went to Mecca.

14.MUHAMMAD DARINGI... A fulani, seven month deposed by the Emir. By Ismaila A Sabo.

15. TUKUR... Son of Gauyama, after five years of his rule Muhammad Bako returned from Mecca, but leave as a private individual. Muhammad Tukur ruled for another five years and was then deposed by Haru for shaving his wife's head.

16. KANKARAU... A fulani appointed by Haru, but deposed after seven month. Muhammad Tukur Was then reinstalled and rule for seven years when he became blind and was deposed. KANKARAU reinstated but after seven years was again deposed by the Emir Muhammadu for having married seven wives.

The Emir then called in all the man of Garun-gabas to choose their own Chief. They unanimously choose Abubakar son of Muhammad Bako a direct descendant of the original Arab founders. Abubakar at first however persistently refused to accept the honour and on being pressed for a reason, told the Emir that as an Arab who had been to Mecca he could not countenance the perversion of the prophet's laws which was rife in Hadejia. The Emir is then stated to have admitted the Truth of this and on condition that he would take the Sarauta to have promised that he should administer according to the true Law at any rate in Garun-gabas.

Abubakar then became Chief and has been Sarkin Gabas for twenty three years to the present day. The famine in common with other Hadejia District, the famine last year was the cause of considerable mortality chiefly among the children. Hadejia A yau.

Reference--- Assessment reports by K. L. Hall, Assistant District officer Hadejia District Kano Province.14th/July/1915.

Friday, July 15, 2016

SIR AHMADU BELLO'S CHRISTMAS MESSEGE IN 1959...


“We are people of many different races, tribes and religions, who are knit together by common history, common interests and common ideals. Our diversity may be great but the things that unite us are stronger than the things that divide us. On an occasion like this, I always remind people about our firmly rooted policy on religious tolerance. Families of all creeds and colour can rely on these assurances. We have no intention of favouring one religion at the expense of another. Subject to overriding need to preserve law and order, it is our determination that everyone should have absolute liberty to practise his beliefs.

It is befitting on this momentous day, on behalf of my ministers and myself, to send a special word of gratitude to all Christian missions. Let me conclude this with a personal message. I extend my greetings to all our people who are christians on this great feast day. Let us forget the difference in our religion and remember the common brotherhood before God, by dedicating ourselves afresh to the great tasks which lie before us.”

Monday, July 4, 2016

AL'ADUN KASAR HADEJIA... Kashi na Daya (1)



WASU DAGA CIKIN AL’ADUNMU KYAWAWA…
Kasar Hadejia mutanen cikinta suna da Al’adunsu kyawawa wadda suka dace da koyarwar Addinin musulunci, wadannan Al’adu saboda kyawunsu yasa mun taso a cikin kyakkyawan tsari da taimakon Junanmu. Shekaru da dama da suka gabata zakaga mutumin Hadejia bubba da yaro yana da Tarbiyyar idan yaga bubban mutum ya gaidashi, kokuma idan yaganshi da kaya a hannu yaje ya karveshi, wannan Al’ada tana da kyau kuma tayi daidai da tsarin Addinin musulunci. Sannan a shekarun baya duk Unguwar da kaje zakaga tsarin zamantakewarsu akwai ban sha’awa, domin wurin zaman manya daban na yara daban sannan idan zaka wuce Bubban mutum yana zaune zaka cire Takalmi sai ka wuce sannan ka saka. Wani abin ban sha’awa shine Lokacin cin Abinci babu yadda zakaga mutum yaci abinci shi kadai ai haduwa ake mutum huxu ko biyar ake ci tare domin neman Albarka. Wannan ya nuna akwai son juna a tsakaninmu, domin wadda Allah bai bashi ikon yin abinci a gidansa ba to bazai wuni da yunwa ba domin idan yazo Dandali zaici tare da ‘yan-uwansa. Haka yara matasa suma kowa yakan dauko abinci daga gidansu a fito a hadu a ci, wannan muke kira da suna Ciyayya.

ZAMANTAKEWA…
Zamantakewa wata kalma ce da take nuni ga yanayin yadda mutum yake rayuwarsa tare da Abokan zamansa wadda Allah ya hadasu, walau a zaman Makwaftaka ko sana’a da sauransu.

TSARIN SHUGABANCHI…
Shugabanci yana nufin rikon on ragamar Al’umma da basu Umarni da kuma yi musu Jagoranci bisa tafarkin da suka aminta dashi, sannan da tsara musu Dokoki da sasanta tsakaninsu. A Kasar Hadejia tsarin shugabanci ya faro ne tun daga cikin gida inda mutum a gidansa shine shugaba mai shirya komai da kuma bada Doka da Oda, sannan sai shugabancin Unguwa wadda ya kasance kowace Unguwa tana da nata shugaban mai sawa da hanawa da bada umarni shine muke kiransa da suna Mai-unguwa. Duk wani umarni yana fitowa ne daga bakin Mai-unguwa kamar hani da kuma sawa. Shi wannan Mai-unguwa duk abinda ya shafi Unguwarsa shine keda iko akai, kamar Umarni, hani, sasanto tsakanin mutane. Kuma duk Bakon da yazo wannan Unguwa akan kaishi gidan Mai-unguwa ne domin shike da Alhakin yaji abinda ke tafe dashi idan mazauni ne shine da hakkin bashi masauki ta haka ake tsaftace Nagari da Mugu a cikin Unguwa. Baya da Mai-unguwa a gari akwai Malami wadda idan wani Bakon malami yazo wurin Wannan malamin za’a kaishi shi zai bashi masauki sannan yaji Dalilin abinda ke tafe dashi. Haka kuma Idan Bakon dan kasuwa ne akan kaishi Gidan Zangoma wadda shine da hakkin saukar Baki musammam masu saye da sayarwa, shi zangoma shine zai tambayeshi irin Hajojin da yake sayarwa kokuma yake saye domin ya sadashi da masu ciniki. Kaga duk wannan yana nuna muna da kyakkyawan tsari na zamantakewa wadda duk mutumin da ya shigo kasar Hadejia ansan Dalilin zuwansa da kuma abinda yazo yi. A duk lokacin da aka samu hakan shi Mai-unguwa shike da Alhakin sanarwa Bulama sannan Bulama ya sanarda Hakiminsa, shi kuma Hakimi zai sanarda Majalissar Sarki.

Wannan tsarin shugabanci shi ake amfani dashi a kasar Hadejia har lokacin zuwan Turawan Mulkin Mallaka. Koda yake Turawa ma da sukazo sai suka lura cewa muna da kyakkyawan tsari na shugabanci, dan haka sai suka nemi Hadin kan Sarakunanmu ya zamanto zasu bada Umarni ne ga Sarakuna sannan Sarakuna su bada Umarni ga Talakawansu. Turawa sunzo sun samemu da Al’adunmu kyawawa sannan muna da tsari na shugabanci kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada mana, wannan dalili yasa Turawa suka samu damar Mulkarmu ba tare da sunsha wahala ba.

Sunday, February 21, 2016

MARIGAYI ALHAJI ADAMU KWANO HADEJIA.....


Daga Mallam Muhammad Rabakaya...

A madadin al'ummar Hadejia da gaba dayan masarautar Hadejia muna addu'a da alhinin Marigayi Alhaji Adamu Kwano (kwano baka karaya) Allah ka gafartawa wannan bawa naka, ka yafe masa kura kurensa da iyayenmu Allah ta'ala kasa aljannah madaukakiya ce makomarsu. Alhaji Adamu Kwano miliyoyin mutane sunyi tarayya da 'ya'yansa wajen gadon dukiyar da Allah ya mallaka masa Allah ka hada mu a Aljannah. zaka\ki so ka\kiji dalili -biyoni..................

Duk wadda ya baka Ilmi ko yayi ma hanyar samun Ilmi ya gama maka alfarma kuma kaci gado daga cikin gadonsa tare da 'ya'yansa. Marigayi Alhaji Adamu Kwano Hadejia Tun kafin a haifeni wannan bawan Allah yana da gida babba mai kallon gidanmu (Gida na a yanzu) Rahama chemist a yanzu ya gina yayi fasalin ajujuwa na Kasa da rufin kwano ya maidashi makarantar  Islamiyya (islamiyyar farko a garin Hadejia), ya tafi kano ya samo Marigayi Malam Aminu Yusuf da Malam Alhaji da Malam Sabo na Madabo da Malam Nasiru Ahli da Malam Rufa'i Kafin Hausa  kuma a matsayin Headmaster da malamai, kuma yabasu mahalli a wancan lokacin mun samu tabbaci daga matar daya daga cikinsu cewa daga gidansa ake dauko musu abinci. Aka saka yara maza da mata aka fara koyarda su darussan addini a tsarin zamani (formal education) mai Allo da Alli.


Daga nan abu ya kara fadada, yasa kudinsa ya cike wani rami mai tarihi wato RAMIN MALAM HUDU inda ya gina ajujuwa na siminti akan ramin da staffroom islamiyya ta koma can ya kara malamai, lokacin duk babu islamiyya sai ita Hudu islamiyya prim. sch. mai tsohon tarihi daga nan gwabnati ta shigo ta taimaka masa da karin Malamai da tsare tsare, Amma gini da gudanarwa nasane.
Bai tsaya nan ba tashinsa zuwa Asibiti inda yake aiki, ya sayi fili anan farin gida ta yanzu ya kara Gina wasu ajujuwan islamiyya ya bude makarantar Islamiyya Garko, duk a lokacin babu Islamiyya sai dai makarantun mu na zaure da na allo, daga nan ya kara fadada niyyarsa da burinsa na habaka ilmin addini a Hadejia ya raba Islamiyya Garko ya Kirkiri Karamar sakandare Islamiyya yasa mata sunan Headmaster na makarantarsa ta farko wato Malam Aminu Yusuf. Ya sake samo wani mutumin Sudan Sheik Ali Fu'ad a matsayin principal inda ya dauka mata malamai itace Aminu Yusuf Junior Islamiyya sec. sch. Hadejia. Wadda daga baya gwabnati ta bashi wani bangare a cikin Buhari primary school Hadejia ta tashi daga Garko ta koma can inda takoma hannun gwamnati kachokam bayan Allah ya masa rasuwa, wannan makaranta yanzu itace babbar sakandaren Islamiyya ta jeka ka dawo ta mata da maza a garin Hadejia.

Daga wancan lokacin zuwa yanzu mutum nawa aka raya? mutum nawa su kuma nawa suka raya da Ilmi? Kuma Bayansa tayi kyau, yana da 'ya'ya da jikoki da sukayi karatun Addini da Boko a fannoni da dama, da wadda yayi digirin farko tun 1977 har zuwa yau agida da kasar waje, sannan kafin yabar aiki yana daya daga cikin wadanda Gen. Olusegun Obasanjo ya baiwa lambar yabo yana shugaban Kasa a shekarar 1977.

Da fatan zamuyi koyi da irinsu a duk bangarorin rayuwa.
posted from Bloggeroid

Friday, February 19, 2016

TARIHIN HADEJIA.



Takaitaccen Tarihin masarautar Hadejia.


Masarautar Hadejia dadaddiyar Masarauta ce wadda ta kafu shekaru aru aru da suka gabata, daga lokacin kafuwarta kawo yanzu masarautar tayi fice da yin suna bisa ga muhimman tarihi da take dashi. Masarautar Hadejia tana daga cikin masarautu da sarakunan HABE suka mulka kafin Jihadin Shehu Usmanu Danfodiyo, kuma tana daga cikin masarautun da ake kira Hausa Bakwai. Masarautar tana daga cikin Masarautu da suke karkashin Daular Usmaniyya, daga Gabas tayi iyaka da Tsohuwar Daular Borno daga yamma tayi iyaka da Masarautar Kano, daga Kudu kuma tayi iyaka da Masarautar Katagum sannan daga Arewa tayi iyaka da Masarautar Gumel. Birnin masarautar yana cikin garin Hadejia dake Arewa maso gabashin Jigawa a Arewacin Nigeria, sunan garin ya samo asali ne daga wani Maharbi wadda shine ya kafa garin wato HADE, da kuma Matarsa JIA. Sunayen wadannan mutane shi aka hada ya zama HADEJIA, domin a lokacin mutanen wasu garuruwa in zasu zo sukan ce mun tafi garin Haden jiya, wato ana masa Lakabi da sunan Matarsa. Saboda takaita kalma ta Hausawa shine yasa aka hade sunan ya zama Hadejia. 

Masarautar Hadejia tana da fadin kasa wadda ta kai Murabba’in kilo mita dubu shida da dari tara da sittin da uku(6963), wannan yanki yana da shimfidaddiyar kasa mai kyau wadda ake kwatanta yanayinta da na kasar Chadi, kuma tana da Jigayi masu tarin yashi da kuma kwari mai tabo da laka amma bada da tsaunuka ko Duwatsu. Kasar Hadejia tana da Kogi wadda ya kasance akwai ruwa kowane lokaci, sannan tana da fadamu masu yawa wadanda suke kafewa lokaci zuwa lokaci.

Kogin kasar Hadejia ya taso ne daga Kudancin Katsina ta Arewa da Zaria sannan ya nufi Arewa maso gabas ya shigo ta Kasar Kano ya ratsa kasar Hadejia, sannan ya nufi Tafkin Chadi. Wannan Kogi ya ratsa ne ta Kudancin Hadejia da Gabashinta, wannan bangare ne da yake samarda ruwan sha da kamun kifi da kuma aiwatar da Noman rani. A lokacin damina kogin yakan cika inda yake samarda kananan fadamu a sassa daban daban wadda ake amfani dasu a wajen noman lambu. A bangaren Noma Masarautar Hadejia tana gabatarda noma a lokuta biyu wato Rani da Damina, inda masana yanayin kasa suka tabbatar cewa duk abinda aka shuka a wannan kasar zai fito yayi kyau saboda yanayin kyawun kasar. 

A bangaren kasuwanci kasar Hadejia ta shahara wajen saye da sayarwa tun kafin Jihadi, domin ta zama wata mahadar kasuwanci ce tsakanin Daular sokoto da Daular Borno. Mutanen Masarautar suna da sana’oinsu da dama kama daga sana’ar hannu zuwa Fatauchi da sauransu. Kasar Hadejia tana da kasuwanni da yawa wadanda suke ci a dukkanin sati sannan da masu ci a kowacce rana.

Masarautar Hadejia tana da Kabilu da yawa wadanda suke yarensu da Al’adunsu sun banbanta kuma suna zaune a yankuna daban daban na kasar, Kabilun kuwa sun kunshi Hausawa, Fulani, mangawa, Ngizmawa, koyamawa, Baddawa, da sauransu. Wadannan Kabilu kowanne da irin yarensa da kuma Al’adarsa da irin tsarin zamantakewarsu, sai dai duka suna bin Tafarkin Addinin Musulunci ne tun bayan Jihadin Shehu Usman Danfodiyo.

posted from Bloggeroid

Tuesday, October 6, 2015

KO KUN SAN?........

KO KUN SAN?.....
A shekarar 1971 anyi wata gagarumar yunwa da fari wanda aka sawa suna KWAKWUDUBA, a wannan lokacin hatta fadamu da koguna duk sun kafe babu ruwa, kuma abinci yayi karanci ga mutane. Hakan tasa mutanenmu musamman wadanda garuruwansu yake kusa da Kogi (Masunta) sukayi Kaura daga garuruwansu suka nufi Gabas. Wasu sun wuce har Chadi wasu kuma suka shiga har Kamaru, yayinda wasunsu suka tsaya a garin Baga.

Koda yake a lokacin wannsn garin da ake Kira Doran Baga mutanenmu ne suka je suka kafa Daba a kusa da gabar Kogi. Anan ne sukaci gaba da zamansu suna Kamun Kifi da sauran Albarkatun ruwa sannan su sarrafa su kawo Maiduguri da wasu sassa na jihar Yobe su sayar. Haka gari yaci gaba da girma sakamakon zuwan mutane Masunta domin su samu abinda zasuci da Iyalensu. Sakamakon gari ya zama gari har sai ake kiran Dabar tasu DORON BAGA.

Akasarin mutanen da suka tafi daga kasar Hadejia mutanen Kafinhausa ne da kuma yankunan Kirikasamma da Guri, idan ka lissafa wancan lokacin zuwa yau zai baka shekara 44. Wadannan mutanen wasunsu sun bar garuruwansu ba tare da suna dawowa suna gaida Iyayensu ba, wasunsu kuma har iyayen nasu suka bar Duniya basuzo sun gansu ba,wasu a cikinsu sun manta yanda yanayin garinsu ma yake saboda sun samu Duniya acan. Da yake ba duk aka taru aka zama daya ba wasu sukan zo su gaida 'yan-uwansu da abokan Arziki sannan su koma tunda Allah yayi zamansu acan.

RIKICIN BOKO HARAM....
A cikin Shekarar 2008/2009 Rikicin Boko Haram ya faru a Gabashin Nigeria, musamman yankunan Jihar Borno da Yobe da wasu sassa na Adamawa da Bauchi da Gombe, wanban rikici yayi Asarar Rayuka da Dukiyoyi masu dinbin yawa, inda akayi ta kone Gidaje da Kasuwanni da wuraren Sana'a. Wannan ne yasa wadancan mutane da na Ambata a sama wadanda Kwakuduba tasa suka bar garuruwansu sai suka fara tunanin su dawo gida, sakamakon fadin Hausawa " Giji Lahira ce" anan ne fa suka fara dawowa ba tare da abinda suka tara a can ba, wasu sun dawo gida sun tarar duk wadanda suka sani sun mutu wasu kuma tsufa ya kama su.

TAKAITACCEN TARIHIN RAYUWAR CHIROMAN HADEJIA. ALH. AMINU HARUNA

Daga Muhammad Yawale....
.

text-align: center;">

Bismillahirrahmanir-rahim.
An haifi Alh Muhammadu Aminu Haruna a garin Guri a shekara ta 1943, A lokacin mahaifinsa Alhaji Haruna Abdulkadir yana Chiroman Hadejia Hakimin Gundumar Guri. Ya halarci makarantar kur'ani wato allo a garin Guri makarantar sule Gangaran a 1952-1956, ya halarci makarantar Elementary primary Dallah a cikin garin Hadejia a 1953-1956, ya halarci makarantar middle school ta fantai hadejia a 1957-1960, sannan ya halarci makarantar horarda malamai ta Bichi a shekara ta 1960-1962.
Marigayi ciroman Hadejia yayi karatu a potiskum (s.t.c sage 1) a 1970 yayi karatu a kaduna polytechnic (stage2-3) a 1971-1974 yayi karatun higher diploma a zaria Insitute of Administration (A.B.U) a 1979-1980. Ya halarci tarurruka na karawa juna sani a wurare daban daban na kasarnan.

AYYUKAN DA YAYI:
Yayi malamin makaranta a lokacin (N.A) ta Hadejia na tsawon shekaru 2, a karkashin tsohon Head master marigayi Alh Abdu maigari Tafidan Hadejia, yayi malamin makaranta a primary ta dubantu a 1965, yayi sakataren karamin minista na MADAKIN Hadejia Muhammadu Gauyama, a ma'aikatar tsaro ta kasa a lagos bangaren jiragen sama (Air-force) a shekarar 1965-1966,
Yayi malami a kotun babban alkali lokacin alkali Dahiru. A shekarar 1966-1968, yayi malamin Turakin Hadejia lokacin Turaki Adamu, yayi Akawu a ma'aikatar mulki ta (N.A), yayi sakataren karamar hukuma a wadannan wurare Bichi, ringim, gumel, wudil, babura, gezawa, kafin hausa, dawakin tofa yayi sakatare na musamman a karamar hukumar birni da kewaye (kano municipal council).

Ya rike mukamin DPM a kananan hukumomin garki, malam madori, Taura a inda yayi ritaya. Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya nadashi Tafidan Hadejia Dan majalisar sarki a shekara ta 1994, cikin yardar Allah kuma Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar ya nadashi Chiroman hadejia a ranar asabar 13 ga watam march 2004 a inda ya gaji yayansa chiroman Hadejia Alh. muhammad Abbas.

Marigayi chiroman Hadejia mutum ne mai jajircewa kan gaskiya da rikon amana akan harkar da aka dorashi kuma ya nemawa mutane da dama aiki a lokacin gwamnati kuma duk abinda ya gani ba daidai ba baya yin shiru sai yayi magana hakazalika bai yarda kayimasa zancen waniba. Marigayi chiroman Hadejia ya rasu ranar juma'a da daddare 03/10/2015 bayan ya sha fama da jinya muna rokon Allah ya jikansa ya kuma kyautata bayansa.

Thursday, May 14, 2015

YAN GUDUN HIJIRA...



YAN GUDUN HIJIRA!
Tun a lokacin da rikicin Boko Haram ya Addabi jihohin Borno da Yobe aka samu watsuwar 'yan gudun hijira a wasu sassa na Nigeria, ciki harda jihar Jigawa, kuma akasarin wadannan 'yan gudun hijira zakaga Mata ne da kankanan yara wadanda mafiya yawa suna a kasar Hadejia da kasar Gumel. A lokacin da suka fara zuwa wadannan yankuna saboda basu da abinda zasuyi dole wasu daga cikinsu suke bin masallatai da majlissai domin neman abinda zasuci abinci da yaransu. Abin tausayi zakaga yara da basu fi shekara 7 zuwa 10 ba suna bi kantuna da wurin zaman jama'a suna neman taimako, a kwanakin baya basuyi yawan da ya wuce kaga biyu ko uku ba a kullum amma yanzu abin sai karuwa yake wanda a kalla sai kaga goma zuwa sama a rana daya da mata da kananan yara abin tausayi. zaka gansu a kofar masallatai da kasuwa har da Bankuna wurin layin Atm. Dole mumini mai Imani ya tausayawa rayuwar wadannan bayin Allah domin ba a son ransu suka bar gidajensu da 'yan uwansu suka zo suke yin Bara ba! Saboda yawan kwararowarsu yasa jama'a sun fara kosawa ganin abin ya zama ba na kare ba, yanzu kullum a baka gansu a gidanka ba kaga biyar ko shida.

MASU HANNU DA SHUNI....

Hakika Masu hali sai sunyi amfani da damar da Allah ya basu wajen taimakon wadannnan bayin Allah da muhalli da Sutura da Abinci, da kuma kula da rayuwarsu musamman kananan yaran. yana da kyau masu hali su ware wani abu daga cikin Dukiyarsu don taimakon wadannan bayin Allah a matsayin Sadakatul-jariya.

GWAMNATI MAI JIRAN GADO...

Koda yake bani da masaniya game da yunkurin da Gwamnatin Jigawa tayi game da wadannan bayin Allah, kuma ban taba ganin wani wuri da aka ware don 'yan gudun hijira ba zanso in bada shawara ga Gwamnati mai jiran Gado, A karkashin mulkin ko jagorancin Jam'iyyar Apc, dasu fara duba wannan Matsalar ta 'yan Gudun Hijira kafin su fara Aiwatar da kowane Aiki domin ceto rayuwar wadannan Mata da kananan yara daga yin Bara, wanda hakan ya fara jefa wasu daga cikinsu zuwa ga halaka. An fara samun rade radin wadannan mata 'yan gudun hijira sun fara yin Arangama da wasu gurbatattun mutane suna yin lalata dasu suna basu kudi, har ma ance wasu da yawa sunyi cikin shege Allah ya kiyaye! Abin takaici sai kaga idan 'yan Hisbah suka kama mace tana lalata in suka bincika sai kaga 'yar gudun hijira ce. Kasan Dalilin da yasata cikin wannan hali?

SHAWARA GA GWAMNATI....

Ina bada shawara ga Gwamnati mai jiran gado da suyi la'akari da wannan matsalar domin su san ta yadda zasu bullowa wannan Al'amari, ya kamata Gwamnati ta samar musu mahalli na wucin gadi sannan ta sanya yaransu a Makaranta don ceto rayuwarsu. kuma Ina baiwa Gwamnati Shawara da ta sama musu sana'oi domin su dogara da kansu. misali Gwamnati zata iya amfani da makarantar koyon sana'a don koyawa Matan yanda ake yin SABULU, SAKA, DINKI,Da sauransu. Daga karshe ina Rokon Allah da kar ya nuna mana makamanciyar wannan Bala'i da zai sa mutum ya bar gidansa da iyalinsa ya tafi wani wuri yana yin abinda ko a Addini yana daga cikin Abu mai Kaskanci. Allah ka zaunar da kasarmu da Jiharmu lafiya.

Ismaila A Sabo Hadejia.
13/may/2015.

posted from Bloggeroid

Thursday, March 26, 2015

TAKOKO GARIN SARKI BUHARI...

TAKOKO GARIN SARKI BUHARI...



Garin Takoko yana daya daga cikin garuruwan Tarihi a Masarautar Hadejia, kuma yana Arewa da garin Mairakumi wanda take karkashin karamar hukumar Mallammadori, Takoko tana karkashin Mulkin Hakimin Garungabas. A lokacin da aka cire Sarkin Hadejia Buhari daga Sarauta ya koma garin Takoko da zama shi da Mutanensa inda kuma anan ne ya zauna tsawon lokaci yana kai hare hare ga kasar Gumel, Damagaram da wasu sassa na yankin Gorgaram (Bade). A zamansa na wannan gari ya samu goyon baya daga Daular Shehun Borno da kuma Machina, sakamakon karesu da yayi daga hare hare daga Mayakan Damagaram.

Bayan cireshi daga mulki da akayi ya koma Takoko Sarkin Hadejia Buhari ya zama Barazana ga Sarakunan Daular Usmaniyya, domin suna tunanin idan aka barshi a wannan gari to Daular Borno zatayi Amfani da karfin mayakansa ta rusa Daular Usmaniyya. Dan haka sai sukayi shawarar suje su yakeshi su kama shi kokuma su kashe shi, sai aka hada mayaka daga kano, katagum, Bauchi, Zamfara da sauransu.

YAKIN TAKOKO:-
Bayan an nada Ahmadu a matsayin Sarkin Hadejia, sauran Magoya bayan shi Buhari sai suma suka bar Hadejia suka koma Takoko inda Buhari yake suka zauna tare. Sarkin Hadejia Buhari anan ya zauna tsakanin Takoko da Shafowa a Arewacin Hadejia da mutanensa kuma yake tafiyar da wannan yankin. Kuma iyakar Hadejia ce da Damagaram da Machina ta Arewa maso Gabas wato yankin Niger da kuma Borno. Kuma Buhari ya bada Gudun mawa sosai a wannan Yankin wajen karesu daga barazanar mayaka, kuma a wannan zama da yayi a Takoko Buhari ya samu kyakkyawar dangantaka da Sarkin Machina da kuma Shehun Borno Umar wanda ya mulki Borno a wannan shekara (1835-1880) wannan dangantaka ta karawa Sarki Buhari kwarewa a yake yake.

(Bishiyar da Sarki Buhari yake hutawa, tana nan a gabas da garin Takoko).


A shekarar 1851, Sarkin Musulmi Alu Bubba yayi shirin ya dauki matakin Karshe akan Buhari, saboda yana tunanin Shehun Borno zai iya amfani da Buhari ya rusa Daular Sokoto saboda ya zame musu Barazana a Arewa Maso Gabas.
A wannan lokacin kuma Dan Galadiman Sokoto ya hada Mayaka daga Hadejia,Kano,Katagum,Misau da Jama'are zuwa Takoko.

A wannan lokacin kuma Buhari da mutanensa sun fita kudu da garin shafowa a lokacin Sarkin Machina ya kawowa Buhari ziyara a garin Takoko shida Jarumansa.
A lokacinda Dan galadiman sokoto suka fito don su yaki Buhari sai ya zabi Sarkin Jama'are Samboli ya jagoranci Mayakan, saboda shi ya fisu sanin Yankin.

A ranar da zasu yaki Buhari kuma a ranar Buhari ya shirya mamaye Garuruwan da suke kudu da Hadejia, sai aka hadu a Garin Shafowa. Yayin da aka hadu aka gwabza fada Buhari yaci Galaba a kansu duk suka gudu, Sarkin Hadejia Ahmadu yayi kokarin ya Gudu Kasar Kano amma sai Barde Risku ya bishi ya Kashe shi.

Bayan Yakin Takoko yazo karshe kuma an kashe Sarkin Hadejia Ahmadu Amma ba'a son ran Buhari ba kuma aka masa Sallah aka kaishi Hadejia aka binne shi, sannan sai Buhari ya koma Hadejia yaci gaba da Mulki. Sakamakon wannan yakin, dangantaka ta sake baci tsakanin Hadejia da Sokoto, kuma Sarkin Musulmi yaki yarda da ya nada Buhari Sarkin Hadejia. Sai ya nada Tukur Na yayari, kanin Sarki Ahmadu kuma yace ya zauna a Mashama a Kasar Katagum a Matsayin sarkin Hadejia ya Gaji dan'uwansa Ahmadu. Amma Tukur bai yarda ya zama Sarkin Hadejia ba saboda yana tsoron Buhari, sai yaga bazai iya yin haka ba. Kuma saboda Gudun kar Buhari ya kasheshi sai Tukur ya Gudu daga Mashema yayi kaura zuwa Kano Lokacin Sarkin Kano Usman Na1(1846-1855) Sai aka Turashi ya Mulki Yayari a Kasar Birnin Kudu. (Yayarin Tukur) Tukur ya zauna acan Har zuwa lokacinda ya Mutu 1909. Buhari kuma yaci gaba da mulkin Hadejia yana kai hare hare a matsayin Jihadi Har saida yakai Gabasawa,Sankara,Ringim da Kuka kwance A Arewa maso yamma. A Kudu saida ya mamaye Kununu,Takalafiya, Kafin baka, Doma, Ruba, Itas da Kwanda. A Gabas kuwa saida ya Mamaye Babuwari, Kazura, Dawah, Gatare da Margadu. Saida Sarki Buhari ya fadada kasar Hadejia tafi Ko ina fadin Kasa a karni na19.

Saturday, January 31, 2015

HISTORY OF BARIKIN HADEJIA...

HADEJIA A YAU!
BY: S. Ginsau...




Bariki is a Hausa corruption of the English work barrack, The Bariki in Hadejia town is an old Government Reserved Area (G.R.A.) which contains some important colonial structures. It is located in the eastern part of Hadejia town, at the outskirts of the town, about 2km from the Emir's palace. Bariki was built in 1905 mainly to serve as a new base for the British: specifically,as the barracks of the "B" and "C" Company of the imperial army - the Royal West African Frontier Force (RWAFF) - which later invaded and occupied Hadejia in 1906. After the establishment of colonial rule, bariki became the permanent

residence of the divisional officer (D.O) in charge of the Northern Division, His office was also established there. Other British colonial officers such as the divisional medical officer and the works engineer had their residence and offices located there.

The colonial structures at bariki-were initially built with mud blocks, However, after the consolidation
of colonial rule, the mud-buildings were replaced with that of burnt bricks which were manufactured at filin birki, also in Hadejia town, in the early 1930s. After independence in 1960, bariki continued to serve as the residence and office of the (D.O) and other senior government officials. The D.O.'s office also became the first Hadejia Local Government Secretariat, after the 1970 local government reforms.

The colonial structures at bariki-were initially built with mud blocks. However after the consolidation of colonial rule, the mud-buildings were replaced with that of burnt bricks which were manufactured at filin birki, also in Hadejia town, in the early 1930s. After independence in 1960, bariki continued to serve as the residence and office of the (D.O) and other senior government officials. The D.O.'s office also became the first Hadejia Local Government Secretariat, after the 1970 local government reforms. HADEJIA A YAU!

Monday, January 26, 2015

TARIHIN KAFUWAR GARIN MAIRAKUMI.







Hadejia A yau!
posted from Bloggeroid

Saturday, January 10, 2015

TARIHIN RAYUWAR ALH. SHU'AIBU HARUNA.


ALHAJI SHU'AIBU HARUNA HADEJIA.
An haifi Alh. Shu'aibu Haruna a cikin garin Hadejia a shekara ta 1-february 1954, yayi makarantar firamare a Matsaro firamare a shekarar1961-1967, yayi makarantar sakandire ta KEDC dake Kano a shekara ta 1969-1974, sannan yayi N. C. E a ATC/ABU Zaria yayi (Degree) a ABU Zaria a inda ya karanci B. ed a Social Studies a shekara ta 1980-1982, Sannan yayiwa kasa shidima wato (NYSC) a Kwara State a shekarar 1979-1980.

Daganan yayi aikin koyarwa a Auyakayi Auyo LGA, a shekara ta 1974-1975, daganan ya koma Bichi Kano State inda yayi aikin koyarwa a shekara ta 1979-1980, Sannan ya rike mukamin (Principal) a Garo dake Kabo LGA a Kano State, a shekara ta 1982-1986, Alh. Shu'aibu Haruna ya sake rike mukamin (Principal) bayan ya koma Kiru LGA Kano State da aikin koyarwa, a cikin shekarar 1986-1991, Sannan yasake rike matsayin (Principal) a Danbatta LGA Kano State a shekara ta 1991-1992, Sannan ya sake rike da matsayin (Principal) a Kaugama LGA Jigawa State, a shekara ta 1992.

Bayan Alh. Shu'aibu Haruna Hadejia ya gama aikin koyarwarsa lafiya cikin nasara da fatan alkairi da abokan aikinsa suka masa, ya rike matsayin (Director General Ministry of Land & Regional Planing Jigawa State) a shekara ta 1992-1993. Sannan ya sake rike matsayin (Dirctor General Budget & Planing Jigawa State) 1993-1994. 

Alh Shu'aibu Haruna Hadejia, ya rike matsayin (Coucilor Hadejia LG Works & Housing) a shekara ta 1994-1996, Sannan ya Zama  (Member Constitutional Amendement) 1999.
Sannan (Chairman Hadejia World Bank Project) sannan (Asst. Sec. Movement for the creation of Hadejia State). Alh. Shu'aibu Haruna gogegge ne a fagen siyasa ya fara harkar siyasa a 1979. NEPU, PRP, NPN, NCPN, NDP, PDP, ANPP, Yanzu kuma yana APC, Kuma (National Delegate) har zuwa yanzu. ganin irin wannan godewa tasa da hakuri irin nasa yasa mutanen Hadejia
suka Tsayar da shi dan Takarar (National House of Assembly) a 2003, NDP. Mai wakiltar Hadejia Auyo da K/Hausa. Alh. Shu'aibu Haruna babban dan kasuwa ne kuma manomi ne, shine mutum na farko da ya fara kawowa kasar Hadejia cigaban da babu wanda ya kawo kasar Hadejia wato Kamfanin Leda mai suna(NAKOWA PLASTIC
LTD) wanda ya samar aiki ga matasan kasar Hadejia, sanadiyyar daukansu aiki da yayi a Kamfaninsa, wanda yanzu sama da mutum 250 suna aiki a karkashin sa, sannan ya
kawo babban cigaba a Harkokin samar da Wayoyin Hannu wato (Handset).Yana da shagunan da ake siyar da wayoyin hannu da dama a cikin garin Hadejiya, wanda mutane sama da 150, suna aiki a shagonan sa. Sannan (Chairman Nakowa Plastics Ltd) & (Pressident Jigawa Chamber of Commerce Mine & Agriculture.

Alh. Shu'aibu Haruna Hadejiya mutum ne mai hakuri da juriya da sanin yakamata. Mutanan Kasar Hadejiya suna maka fatan alkairi Allah ya daukaka rayuwarka Allah ya taimaki zuri'arka baki dayansu. Allah sauran mutanan kasar Hadejia zasuyi koyi da irin halinka. Allah yasake buda maka kasake kawomana wani cigaban kasar Hadejia wanda mutane zasuna karuwa da ita. Amin.

HADEJIA A YAU!

Saturday, December 20, 2014

ZIYARA DA AMFANINTA.

a.

r">
Ziyara wani Nau'i ne na zumunci wanda mutane suke aiwatar da ita domin sada zumunci ga 'yan'uwa da abokan Arziki. zumunci wata irin halayya ce ta kwarai wacce ke sadar da dangantaka ta nasaba tsakanin ’yan'uwa ko bare. Zumunci ne ke kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali da fahimtar juna tsakanin al’umma.

Ta hanyoyin da mutum zai bi ya inganta zumunci shine, kaiwa ziyara ga 'yan'uwansa kamar kaka, uba kokuma kanin mahaifi ko kanin mahaifiya da sauransu. Ta haka ne mutum zai gane irin yadda Alaqarsa take da 'yan uwansa na nesa ko na kusa. Haka kuma kowa yana da iya kimar zumuncin da zai gudanar a tsakaninsa da wani. Kamar yadda Hausawa suka ce zumunta a kafa take, to wannan gaskiya ne,domin
kuwa daya daga cikin manyan ginshikan zumunta shi ne ziyartar juna. Idan ka kula da zumunci shike sa mutum ya niki gari zuwa gidan abokinka ko wani dan'uwanka, ko bare musamman domin ganin yadda yake. Wannan ziyara kawai, ita ke haddasa kauna da mutunci mai dorewa a tsakanin al’umma.

A shekarun baya kamar shekara kamar goma zuwa sama,saboda muhimmancin ranar Juma'a,iyaye sukan je da 'ya'yansu gidajen 'yan'uwansu da Abokan Arziki domin gaisawa wanda hakan yana nuna ana nusar da yara ne da kaiwa ziyara ga 'yan uwansu. Harma yara suke kiran wannan ziyara da yawon Juma'a. Amma saboda shagaltar da zuciya irin ta shaidan tasa wannan kyakkyawan Aiki na ziyara ya fara ja baya ga yara harma da manyan a wannan zamani,domin shi bubba yana tunanin ai in yaje zai bada kudi, sannan yaro yana tunanin kar yaje ba'a bashi kudi ba.

Wednesday, December 3, 2014

TAKAITACCEN TARIHIN HASHIM UBALE YUSUF..

Hadejia A yau!

An haifi Hashim Ubale Yusufu a Garun Gabas da ke cikin yankin Karamar Hukumar Mallam Madori ta yanzu, A ranar 21 ga Satumba na shekarar 1956. Ya fara karatunsa a makarantar firamare a nan Garun Gabas inda ya fita da kyakkyawan sakamako a matsayin dalibi mafi kwazo da hazaka Daga nan ya wuce zuwa Sakandaren gwamnati dake Birnin Kudu inda ya yi karatu daga 1969 zuwa 1973, lokacin da ya rubuta jarrawar makarantun sakandare ta Afirka ta Yamma wato WASC.

Ya halarci Makarantar Koyon ilimi mai zurfi ta Kano, wato College of Advanced Studies daga 1973 zuwa 1975, inda ya fita da babbar takardar shaida, wato Higher School Certificate. Daga nan kuma ya sami shiga jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria inda ya yi karatun digiri a fannin ilimin harhada magunguna (wato pharmacy) wanda ya gama a shekarar 1981.Bayan ya kammala karatun jami-a, sai sai ya tafi aikin bautar kasa a jihar Imo inda aka tura shi Federal Polytechnic da ke garin Afikpo -Okposi inda ya yi aiki a matsayin mai bayar da magani na wannan makarantar da kuma koyar da darasin chemistry daga 1982 zuwa 1983.Hashim ya fara aiki tun daga matakin karamin ma'aikaci inda a tsawon shekaru ya taka matakai daban daban har zuwa matsayin darakta a hukumar kula da tsaftar abinci da magunguna a Nigeria, da kuma bubban sakatare wato permanent secretary.

Ya fara aiki a shekarar 1974 a matsayinsa na Mataimakin Jami'in gandun daji a karkashin sashen kula da gandun daji na tsohuwar Jihar Kano, sannan daga bisani ya canja aiki zuwa bubban Asibiti na Kano (wanda aka fi sani da asibitin Murtala a yanzu) inda yayi aiki amatsayin jami'i mai bada magani na wucin-gadi a cikin shekarar 1981 da 1982, inda kuma a shekarar 1983 aka daukeshi aiki a karkashin Sashen Kula da ayyukan lafiya kuma aka tura shi Asibitin Murtala da ke Kano a matsayin Jami'in bayar da magani mai daraja ta daya. Daga 1985 zuwa 1987, ya yi aiki a cibiyar sayar da magani ta Lafiya Pharmacy dake garin Hadejia, wadda ta kasance daya daga cikin cibiyoyin sayar da magani da aka bude a wancan lokacin. Bayan daukar lokaci yana aiki karkashin gwamnati,sai ya tsallaka zuwa ma'aikatu masu zaman kansu inda ya yi aiki a kamfanonin sayar da magunguna na NAMCO da kuma ANHEL das u ke cikin binin Kano daga 1987 zuwa 1989. Haka nan ya yi aiki a da hukumar bada tallafin cigaba ta kasar Amurka wato USAID a matsayin jami’in gudanar da ayyuka na kasa karkashin shirin Inganta Lafiyar Iyali (wato Family Health Services).

A shekarar 1989, ya rike mukamin Mai bada shawara a gandun daji na tsohuwar Jihar Kano, sannan daga bisani ya canja aiki zuwa Babban Asibiti na Kano (wanda aka fi sani da asibitin Murtala a yanzu) inda ya yi aiki a matsayin jami'i mai bada magani na wucin-gadi tsakanin 1981 da 1982, inda kuma a shekarar 1983 aka dauke shi aiki karkashin Sashen Kula da ayyukan lafiya kuma aka tura shi Asibitin Murtala da ke Kano a matsayin Jami'in bayar da magani mai daraja ta daya.

Wednesday, October 29, 2014

HADEJIA TOWN WALLS AND GATES.

BY: SULEIMAN GINSAU HADEJIA A YAU! HADEJIA TOWN WALLS AND GATES "Hadejia was a large town with 5 town gates and excellent walls about 30ft (9.14m) high, and 30ft (9.14m) thick " (Captain Philips 1909)

Hadejia Town walls had a long history dating back to the pre-jihad period. The walls were built to provide security to the people, and to serve as fortification against external invasion. Though mostly in ruins now, with a great proportion having completely disappeared, the walls were intact up to the time of the colonial invasion in 1906. Hadejia A yau!

The construction of the walls was done by direct labour using local building materials. Over the years, the walls have been taken subjected to several phases of development. Expansions and reinforcements were made to accommodate a growing population or to enhance security against attack by powerful enemies. The walls were invariably complimented by gates whose history could be linked to that of the walls. The gates provided the only entry points into the town. They were made extremely strong, thus making it very difficult for an enemy force to break into the town through them. Hadejia A yau.

The gates were manned by gate-keepers or porters (sarakunan kofa) appointed by the Emir. These keepers used to close the gates everyday from dusk to dawn, thus controlling the movement of people in and out of the town during these periods. Visitors or strangers were not allowed in unless with the express permission of the Emir. It was reported that one Emir ordered the gates to be left open permanently, confident that no enemy force would dare attack the town.

The first town wall in Hadejia was believed to have been built during the pre-jihad period. Though the exact date of its construction cannot be determined due to lack of proper records, its perimeter is marked by certain well-known local pits: Mai kilabo in the west, Atafi in the south, and Dallah in the East. It was said to be one mile in circumference, and had four gates. The second wall was built by Sarki Sambo in the early years of the Jihad. It was wider than the previous wall, with its perimeter approximately put at 2 miles 170 yards. It had 5 gates. The present wall, which was the third, was also built during Sambo's reign. It was built at a time when Hadejia was at the centre of a bitter rivalry between Sokoto caliphate and Borno Empire. As such it was much stronger and wider than the previous walls. An extension to this wall was later made on the Eastern side during the reign of Sarki Haruna (1865 -1885) encompassing a large space to harbor fugitives from surrounding villages in times of war.


The Habe settlement of Fantai, which hitherto was outside the wall, also became sheltered in the new extension. This brought the wall to its present size of 4miles 135yards, with 5 gates, namely: 

Kofar Gabas (also known as Kofar Gwani) Kofar Arewa KofarYamma Kofar Kyalesu (also Known as Kofar Kogi) Kofar Mandara (also known as Kofar Talata) Apart from the Kofar Mandara gate, which was destroyed by the British in their attempt to gain entry into Hadejia town in 1906, the other gates are still standing in their original positions.


They have, however, undergone several modifications over the years, the latest being in1985 which saw the total re-construction of Kofar Arewa and Kofar Yamma. The Hadejia town gates now stand as historical monuments rather than as security outposts. HADEJIA A YAU BY: SULEIMAN GINSAU -- Sent from A. Sabo note fad. HADEJIA A YAU!

Monday, September 29, 2014

TARIHIN RAYUWAR GALADIMAN KANO A TAKAICE! Alhaji Tijjani Hashim.

Hadejia A yau!< p> An haifi Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim a cikin garin Kano, a shekarar 1932. Mahaifinsa shine Turakin kano Hashim dan sarkin kano Abbas jikan sarkin Kano Ibrahim Dabo. Ya fara karatun Elementary  a garin Bebeji a cikin shekarar 1944. sannan ya shiga makarantar Middile ta Kano inda ya kammala a  shekarar 1951.

A shekarar 1952 Galadiman kano ya fara aiki a  hukumar N. A. (Native Authority) ta Kano a matsayin Malamin Dabbobi, mai kula da tsafta da lafiyar dabbobi. A 1956 aka zabe shi  a matsayin dan majalissa mai wakiltar Sumaila a majalisar dokoki ta Arewa dake kaduna.

A zaman sa a wannan majalisa ne ya rike mukamai da dama ciki har da shugaban hukumar bada kwangila ta Kaduna sannan ya rike shugaban kwamitin tabbatar da jamiyyar NPC ta lashe zabe a lardin Sardauna. Sannan ya rike mukamin Ministan Ayyukan cikin gida na Jihar Arewa. Yayi Kwamishinan lardi mai kula Lardin Kabba wandda yana kan wannan mukamin ne sojoji suka yi juyin mulki.

Bayan ya dawo gida sai  Sarkin Kano Ado Bayero ya nada shi sarautar Dan-isan Kano kuma kansila mai kula da ayyukan gayya da taimakon kai da kai.

A cikin shekarar 1976 ne ya samu karin girma zuwa sarautar Turakin Kano da bashi kulawa da gundumar Kumbotso. sannan A 1980, ya sami canji zuwa kansila marar ofis saboda yawan  harkokinsa na kasuwanci. A shekarar 1989, ya samu karin girma zuwa sarautar Dan-iyan Kano, kuma ya ci gaba rike mukamin kansila marar ofis.

A shekarar 1992, ya samu karin girma a sarauta inda aka nadashi Galadiman Kano kuma shugaban kwamitin kudi na majalisar Sarki. A shekarar 2012 Sarki ya kara masa aikin hakimcin birnin Kano. Wannan aiki ya ke rike dashi har Allah ya masa rasuwa.

Galadiman Kano Tijjani mutum ne mai hakuri da juriya da Alkairi. Kuma yana da daraja a Idanun mtane sakamakon amfani da yayi da damarsa ya kafa mutane a Gwamnati. kuma babu inda zai nemi Alfarma a gwamnati bai samu ba, wannan tasa ake masa Laqabi da GAJERE WAN GWAMNATI.

A ranar28/september/2014, Allah ya yiwa Galadiman kano rasuwa ya rasu ya bar 'ya'ya da Matan Aure da 'yan-uwa da dama. Muna Addu'a Allah ya gafarta masa.

Friday, August 15, 2014

TARIHIN DAN-AMAR DIN HADEJIA M. USMAN GINSAU.

MARIGAYI DAN AMAR ( ALH. MALAM GINSAU) 1917 -1997……………………………..
Marigayi Dan Amar din Hadejia Alhaji Malam Usman Ginsau dan Chiroman Hadejia Ali, dan Sarkin Hadejia Haruna Maikaramba dan Sarki Muhammadu Maishahada ne. Yayi karatun makaranta a garin Hadejia.Yana daga cikin yan makaranta na farko da suko ka bude Clerical College da ke Congo a garin Zaria, kafin ta rikide ta koma ABU Zaria.

Malam ya koma England (UK) domin karin karatu a harkar Community Development. Marigayi Dan Amar ya zama Community Dev. Secretatry na Hadejia N.A. Bayan wannan aiki Marigayi ya kama aikin Gona gadan gadan har zuwa1980.

Ya zama Representative Na Hadejia NA a Old Kano State wanda ya bashi damar shiga Co -operative Society na Nigeria shi da Sarkin Ringim Alh. Sayayadi Mahmudu.Marigayi ya zama 2nd Vice President na Co-operative Society of Nigeria. Yayi Ritaya daga wannan aiki a 1980.

Daga nan Marigayi ya kafa Makarantar Islamiyya da ta Karatun Alkura’ani a Gidansa, shi da kansa yake karantar da mutane, wato manya da yara. Malam yayi ta yin wannan aiki har zuwa 1983 a lokacin da aka nada shi Dan Amar din Hadejia, Hakimin Kafin Hausa.Malam yana daya daga cikin dattijan da suka tsaya wa Kasar Hadejia da addu’a da kuma bada gudummawa wajen duk wani aiki na dattako a Kasar Hadejia. Malam ya rasu ya bar ‘ya ‘ya ashirin da shida.. Daga cikinsu Akwai Dan-Amar din Hadejia na yanzu Alh. Aliyu Usman Ginsau, Hakimin Kafin-hausa, da Baraden Hadejia, Alh. Haruna Usman Ginsau.

Allah ya jikansa ya gafarta masa, ya kara sa albarka a zuriyar da ya bari. Ameen.Posted from WordPress for Android via Hadejia A yau.

Monday, March 17, 2014

TARIHIN JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO (DAGA NA GABA PART FIVE 5)

TAKAITACCE TARIHIN MAIGIRMA JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO!!
Daga Muhammad Yawale.




An haifi Alh. Abba sambo a shekara ta 1943 a cikin garin hadejia, ya fara karatun allo a matakin karatunsa na farko sannan lokacin ya isa shiga makarantar boko. Ya fara da hadejia junior elementary school dake dalla wanda a yanzu ake kira Abdulkadir primary school a shekarar 1953-1957 a garin hadejia. Bayan ya kammala wannan makarantane ya samu shiga middle school a cikin shekarar 1957-1959, daga nan bayan kammala middle school ya koma makarantar horan malamai ta wudil/bichi teachers collage a shekarar 1960-1965.


Bayan kammala wannan karatune ya samu zama headmaster a garin gabas primary school a shekara ta 1966-1971, ya koma karin karatu a advance teachers collage zaria a cikin shekara ta 1971-1974 wanda ya samu certificate in education (NCE). Bayan kamamala (NCE) bai tsaya ba domin samun degree na farko a fannin physical Health Education (PHE) wanda ya kammala a 1975-1978 ABU Zaria. Yayi hidimar kasa (NYSC) a federal advance teachers collage dutsinma katsina state daga 1978-1979.

Wasu ayyuka da yayi:
(1) mataimakin shugaban wasannin motsa jiki gwamnatin tarayya (NSSF) 1985-1989
(2) wakili a hukumar ilimi mai zurfi ta jami'ar Ahmadu
bello dake zaria 1988-1991 
(3) wakilin tantance jarabawar dalibai na kasashen africa 1995. 

(4) shugaban wasannin motsa jiki na makarantun jihar jigawa.


Mukaman da ya rike: (1) shugaban makarantar primary ta garun gabas.(2) jami'i mai kula da shiyar kudu maso yamma wadda take birnin kudu a jihar kano (3) mataimakin shugaban kwalejin makarantar horarda malamai dake garin hadejia (4) mataimakin jami'in ilimi na shiyoyin kananan hukumomin gezawa, da minjibir a jihar kano (5) shugaban makarantar sakandiren jeka ka dawo dake kazaure (6) shugaban kwalejin horar da malamai ta garki. Da sauransu.

Jarman hadejia ya bar aiki ranar 30th ga watan oktoba, 2001 a matakin aiki na 16/17. Bayan rasuwar marigayi jarman Hadejia Alh. Usman sambo na (2) a ranar Asabat 4 ga watan december 2010, maimartaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar maje Con, ya nada ALH. ABBA SAMBO a matsayin JARMAN HADEJIA na (3) a gidan Tafarki Guruza, Jarman Hadejia na biyar (5) a jerin Sarautar Jarma a kasar Hadejia kuma Dan majalisar maimartaba sarki.
HADEJIA A YAU....

Thursday, March 6, 2014

TAURARINMU HADEJIAWA (Part four 4)

DAGA MUHAMMAD IDRIS



Hadejia A yau! 

FARFESA HARUNA WAKILI...............Farfesa Wakili haifaffen kofar fadar Hadejia ne, kuma kamar yadda sunansa ya nuna mahaifinsa shi ne Wakilin kudun Hadejia [Dandalma] wato mai kula da yankin kudancin garin Hadejia.

Farfesa Wakili shi ne Farfesa na biyu a masarautar Hadejia kuma yana daya daga cikin `yan majalissar dattijai na Jami`ar Bayero ta kano kuma babban Alaramma a tsangayar tarihi ta makarantar, harwayau shi ne Mufti akan harkar tarihi a Arewacin kasar nan dominkafafen watsa labarai da dama na ciki da wajen Nijeriya suna dogara da fatawowinsa wajen warware matsalolin tarihi da suka bujuro musu.Baya da harkokinsa na cikin Jami`a Farfesa Haruna Wakili ya rike Daraktan Cibiyar Nazarin Harkokin Siyasa na Jami`ar wato MUMBAIYA dake Gidan Malam Aminu Kano a Unguwar Gwammajar kano.

" Na zaune bai ga gari ba", wanda bai sanJami`a ba, ba zai san gudunmawar Wakiliba domin a shekaru ashirin da biyar da suka gabata duk dan masarautar Hadejia da ya je Bayero ofishin Wakili ne zangonsa, shi kansa ba zai iya kididdige daliban da ya yi wa hanyar karatu a jami`a ba.

"Mai kamar zuwa kan aika" Yana cikin wannan gwagwarmaya Allah [swt] ya yi masa kwamishinan Ilmi na Jihar Jigawa. wannan mukami nasa duk Bahadeje mai hankali ba zai taba mantawa da shi ba domin baya da ci gaba a gyaran makarantu da samar da aiyuka da matasa da ya yi to kuma a lokacinsa babbar bukatarmu da muka dade muna nema ta neman babbar makaranta ta kai ga biya wato muka samu Jami`ar Kafin Hausa kuma aka gina babbar makarantaraiyukan gona ta Hadejia ta bar lungu ta dawo kan hanya.

Farfesa Haruna Wakili cikakken Bahadeje ne ba ya son raini amma yana da kishin al`ummarsa yana son ci gabansu kuma saboda daga darajar wannan masarauta shi rubutunsa ma na digirinsa na biyu akan wannan Masarauta ya yi.a takaice dai rayuwarsa akan bautawa Ilmi take.Hadejawa suna addu`a Allah Ya ba gwanin yafe gwado.



FARFESA HARUNA BIRNIWA............kamar yadda sunansa ya nuna Farfesa Haruna Birniwa haifaffen garin Birniwa ne kuma yana cikin haular masu mulkin garin.Birniwa shi ne farfesa na farko a cikin wannan masarauta kuma farfesa nabiyu a fadin Jihar Jigawa.


Gaba daya rayuwar Birniwa a kan bautawa Ilmi take domin ya kasance daya daga cikin dattawan malamai a Jami`ar Danfodiyo dake Sokoto na shekaru masu yawa kuma ya rike 'provost' a kwalejin Ilmi dake Gumel sannan ya rike kwamishinan Ilmi a wannan Jiha.

Farfesa Birniwa ya bayarda gudunmawa a fagen bayarda ilmi a Jihar nan matuka domin daruruwan mutane sun ci moriyarzamansa a sokoto domin shi 'admission' a wurinsa kamar mutum ya mari budurwa ne don haka za a ya ce wa shi ne ya budewa Hadejawa kofa a sokoto kuma bai bar sokoto ba sai da ya yi dashe.
Lokacin yana 'provost' ma masu rabo sun samu aiki a wurin.Birniwa ba harkar ilmin zamani kadai ya tsaya ba domin fakihi ne a fannin addini kuma fahintarsa da addini ta kara sa kyawawan halayensa sun kara kyautata domin mutum ne mai hakuri da gaskiya da rikon amana da saukin kai.wani abun sha`awa ga halayensa mai unguwarsa a Hadejia ya ce in dai yana gari duk yadda za a je neman ci gaba da shi ake yi. munaaddu`a Allah ya albarkaci bayansa.

Saturday, March 1, 2014

DAGA NA GABA! HADEJIAWA (PART TWO 2)





DAGA HASHIM AMAR...
MUHAMMAD (ABBAS SECRETARY)- Tsohon Sakataren kananan hukumomin Hadejia, Malam Maduri, SuleTankarkar da Guri; tsohon jami'in kula dajin dadin jama'a, a halin yanzu Akawun Majalisar dokoki ta Karamar Hukumar Guri(Clerk).

Wannan bawan Allah ya taka rawar gani wurin samar wa matasa da dama aikin yia lokacin da yake mukamin Sakatare musamman a Hadejia da Guri. Na san mutane da dama da wannan mutum ya samawa aikin yi, cikin su kuwa har da ni kaina.

HAJIYA SABUWA SHEHU- Shohuwar jami'ar ilmi, tsohuwar shugabar makarantar firamare, tsohuwar Sakatariyar ilmi ta Karamar Hukumar Hadejia; daya daga cikin mata 'yan boko na farko a Kasar Hadejia. Wannan baiwarAllah ta taimaka matuka wurin ci gaban ilmin mata a wannan yanki, ita ce ta dauki mafi yawanmata Malaman Makaranta a Hadejia.

Ta wani bangaren 'yar kasuwa ce da ta samar da aikin yi ga matasa ta wannan bangaren, ita ta kafa shagon gudanar da harkokin sarrafa na'ura mai kwakwalwa (Bussiness Centre)na farko a Hadejia. A yanzu haka 'yar kwamitin kwararru ce masu kula da aiyukan Bankin Duniya a Hadejia. Kuma ta na cikin kwamitin kula da Makarantun Firamare da Bankin duniya suka gina a Hadejia.

Wani abin sha'awa ita ta samar da filin ginin daya Makarantar (Shagari Community), ta nemi filin a hannun Karamar Hukumar Hadejia a  madadin LEA, filin yana hannun ta fiye da shekaru goma. Hajiya Sabuwa ta bayar da tsohongidan ta kyauta ga hukumar ilmi (LEA Hadejia) don gina Makaranta, gidan na unguwar Chadi. Allah Ya saka mata da alkhairi, ya yawaita mana irin ta.

Wednesday, February 19, 2014

DAGA NA GABA! HADEJIAWA...(part one 1)


;
*****Ciroman Hadejia Sambo da ne ga Sarkin Hadejia Abdulkadir.Yana daga cikin 'yan boko na farko a Arewa kuma mutum na farko da ya fara zuwa England a Masarautar Hadejia.Ya rike mukamin Dan Majalissar tarayya a zamaninsa kuma shi ne Babban Dan Majalissar Sarki (senior councillor) a wannan masarauta.Idan aka yi Tarihin ci gaban kasar Hadejia ba a sanya Ciroma Sambo ba tamkar an yi tuya ba a sa albasa ba ne.


Ciroma Sambo dan ajinsu Sardauna ne Sir Ahmadu Bello kuma amininsa ne don haka Sardauna ya yi masa tayin mukamin minista amma ya ki saboda ya ce "idan na bar Hadejia to ba za ta ci gaba ba"A takaice dai ciroman Sambo shi ne kashin bayan ci gaban Hadejia, a zamaninsa ne aka yi gagarumin fashin layi wanda ya zama sanadin titunan da muke gani a cikin gari a yau kuma zamaninsa ne aka fara ginin rumfunan kasuwa na bulo.



Zamaninsa aka fara gina asibiti aka ofisosin gudanarwa da muke da su,a dai lokacin aka kawo wayar tangaraho a Hadejia da Malam Madori kuma Saboda hangen nesa da sanin muhinancin ilmi ciroma ya tursasawa jama'a su sa 'ya'yansu makaranta wanda wannan ce ta sa wannan gari ya yi fice a fagen ilmi har a yau.Wato ba za mu iya kididdigewa aiyukan marigayi ciroma sambo ba saboda aiyukansa ya hade masarautar baki daya.



Ciroma sambo shi ne ya koyawa Sarkin Kano Sunusi Turanci saboda zamani. Allah ya albarkanci bayansa domin har yau Hadejia tana cin gajiyar 'ya'yansa da jikokinsa.Marigayi ciroma sambo masanin ilmin addini ne da na zamani, rumfa sha shirgi,mai hannun kyauta,mai dimancaccen tunani, mai kishin Hadejia na farko.An haifi marigayi a 1909 Ya rasu a 1958 wato yana da shekaru arba'in da tara a duniya kenan. Allah ya sa jannatil firdausi ce makomarsa. Amin.

FARFESA MUHAMMAD IBRAHIM YAKASAI 
*************** Farfesa Muhammad Ibrahim Yakasai haifaffan kasar Garin Gabas ne ta karamar Hukumar Malam Madorin Hadejia.Ya samu lakabin Yakasai saboda ya yi karatunsa a gaban yayarsa da ke aure a 
unguwar Yakasai ta kano. Muhammad Ibrahim yana daya daga cikin manyan 'yan boko na wannan Masarauta kuma shi ne Bafulatani na farko da ya samu darajar farfesa a wannan masarauta.Yakasai ya fara malamin makaranta a sakandiren wunti da ke Hadejia na gajeren lokaci sannan ya samu koyarwa a Jami'ar Bayero da ke kano.



Allah ya yi masa nasibi a harkar karatu domin ya kammala karatuttukansa a cikin lokaci takaitacce. Yakasai yana cikin malamai dake taimakawa 'yan wannan masarauta da ma jihar jigawa baki daya wajen samun shiga jami'a.Baya da daukansu kuma yakan dauki al'alar taimakawa wajen warware matsalar da duk wani dalibi ya shiga cikin jami'a.

Yakasai mutum ne mai fara'a,mai saukin kai,mai sanin yakamata,Karatunsa bai sa ya dauki duniya da zafi ba.Muna masa addu'ar zama vice chancellor nan gaba. Hadejia A yau...

Wednesday, February 5, 2014

EMIRE OF HADEJIA ALH.HARUNA ABDULKADIR.

Emir of HADEJIA Alh. Haruna Abdulkadir ruled from 1950, before he was appointed as Chiroma as Distric head of Guri at the age of 12 in 1921, he experienced a poor health for some years, during which the emirate council ischaired by successive Galadimas, the decendent of Jaji on his behalf who takes charge on the administration of HADEJIA town, just like Sarkin Arewa is district head of Birniwa and Sarkin Dawaki administers kirikasamma district.

But while previously, during colonial period, the Tafida administered Kafin Hausa as district head, until more recently when it was given to Chiroma, a son to the Emir. Fallowing Chiroma’s appointment as a chairman of the Kano state local government service commission he was unfortunately obliged to reside at Kano city, leaving Kafin Hausa to be administered by his deputy while he retain the title.

The old emirate council from 1971 – 1975meet more frequently under the chairmanship of the Galadima Yusuf and Adamu, the major responsibilities of that administration rested firmly with Dan’iya,M. abdulkadir Maidugu, himself a grandson a grand of the Emir Abdulkadir and formally Sarkin Auyo and district head of Auyo, he represented HADEJIA inthe Federal House of Assembly. In his return after the abolition of a civilian rule, he was appointed Senior Executive Councillor of the Emirate council in charge of finance, the native administration,works, rural water supplyand community development.

TheTafida alh. Abdulkadir Maigari, another grandson of the emir Abdulkadir was appointed a councillor in charge of Agric and Natural resourses.The Danburan muhammadu Hurdi……………….

.(Culled from “Local Government at Hadejiia 1977” By M. G. Smith)
By Ma'aji I Abubakar.